الإنشقاق

تفسير سورة الإنشقاق

الترجمة الهوساوية

هَوُسَ

الترجمة الهوساوية

ترجمة معاني القرآن الكريم للغة الهوسا ترجمها أبو بكر محمود جومي، نشرها مجمع الملك فهد لطباعة المصحف الشريف بالمدينة المنورة، عام الطبعة 1434. ملاحظة: ترجمات بعض الآيات (مشار إليها) تم تصويبها بمعرفة مركز رواد الترجمة، مع إتاحة الاطلاع على الترجمة الأصلية

﴿بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ إِذَا السَّمَاءُ انْشَقَّتْ﴾

Idan sama ta kẽce,

﴿وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ﴾

Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron,

﴿وَإِذَا الْأَرْضُ مُدَّتْ﴾

Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta,

﴿وَأَلْقَتْ مَا فِيهَا وَتَخَلَّتْ﴾

Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.

﴿وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ﴾

Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren,

﴿يَا أَيُّهَا الْإِنْسَانُ إِنَّكَ كَادِحٌ إِلَىٰ رَبِّكَ كَدْحًا فَمُلَاقِيهِ﴾

Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.

﴿فَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ بِيَمِينِهِ﴾

To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa.

﴿فَسَوْفَ يُحَاسَبُ حِسَابًا يَسِيرًا﴾

To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi.

﴿وَيَنْقَلِبُ إِلَىٰ أَهْلِهِ مَسْرُورًا﴾

Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.

﴿وَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ وَرَاءَ ظَهْرِهِ﴾

Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa.

﴿فَسَوْفَ يَدْعُو ثُبُورًا﴾

To, zã shi dinga kiran halaka!

﴿وَيَصْلَىٰ سَعِيرًا﴾

Kuma ya shiga sa'ĩr.

﴿إِنَّهُ كَانَ فِي أَهْلِهِ مَسْرُورًا﴾

Lale ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha.

﴿إِنَّهُ ظَنَّ أَنْ لَنْ يَحُورَ﴾

Lalle ne yã yi zaton bã zai kõmo ba.

﴿بَلَىٰ إِنَّ رَبَّهُ كَانَ بِهِ بَصِيرًا﴾

Na'am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.

﴿فَلَا أُقْسِمُ بِالشَّفَقِ﴾

To, ba sai Nã rantse da shafaƙi ba.

﴿وَاللَّيْلِ وَمَا وَسَقَ﴾

Da dare, da abin da ya ƙunsa.

﴿وَالْقَمَرِ إِذَا اتَّسَقَ﴾

Da watã idan (haskensa) ya cika.

﴿لَتَرْكَبُنَّ طَبَقًا عَنْ طَبَقٍ﴾

Lalle ne kunã hawan wani hãli daga wani hãli.

﴿فَمَا لَهُمْ لَا يُؤْمِنُونَ﴾

To, mẽ ya sãme su, ba su yin ĩmãni?

﴿وَإِذَا قُرِئَ عَلَيْهِمُ الْقُرْآنُ لَا يَسْجُدُونَ ۩﴾

Kuma idan an karanta Alkur'ãni a kansu, bã su yin tawãli'u?

﴿بَلِ الَّذِينَ كَفَرُوا يُكَذِّبُونَ﴾

Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi.

﴿وَاللَّهُ أَعْلَمُ بِمَا يُوعُونَ﴾

Alhãli Allah Shĩ ne Mafi sani ga abin a suke tãrãwa.

﴿فَبَشِّرْهُمْ بِعَذَابٍ أَلِيمٍ﴾

Saboda haka, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.

﴿إِلَّا الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ لَهُمْ أَجْرٌ غَيْرُ مَمْنُونٍ﴾

Fãce waɗanda suka yi ĩmãni, suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da wani sakamako wanda bã ya yankẽwa.

الترجمات والتفاسير لهذه السورة: