الفجر

تفسير سورة الفجر

الترجمة الهوساوية

هَوُسَ

الترجمة الهوساوية

ترجمة معاني القرآن الكريم للغة الهوسا ترجمها أبو بكر محمود جومي، نشرها مجمع الملك فهد لطباعة المصحف الشريف بالمدينة المنورة، عام الطبعة 1434. ملاحظة: ترجمات بعض الآيات (مشار إليها) تم تصويبها بمعرفة مركز رواد الترجمة، مع إتاحة الاطلاع على الترجمة الأصلية

﴿بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ وَالْفَجْرِ﴾

Inã rantsuwa da alfijiri.

﴿وَلَيَالٍ عَشْرٍ﴾

Da darũruwa gõma.

﴿وَالشَّفْعِ وَالْوَتْرِ﴾

Da (adadi na) cikã da (na) mãrã.

﴿وَاللَّيْلِ إِذَا يَسْرِ﴾

Da dare idan yana shũɗewa.

﴿هَلْ فِي ذَٰلِكَ قَسَمٌ لِذِي حِجْرٍ﴾

Ko a cikin waɗannan akwai abin rantsuwa ga mai hankali (da yake kange shi daga zunubi)?

﴿أَلَمْ تَرَ كَيْفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍ﴾

Ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata da Ãdãwa ba?

﴿إِرَمَ ذَاتِ الْعِمَادِ﴾

Iramawa mãsu sakon* ƙĩrar jiki.

﴿الَّتِي لَمْ يُخْلَقْ مِثْلُهَا فِي الْبِلَادِ﴾

Waɗanda ba a halitta kwatankwacinsu ba a cikin garũruwa (na dũniya).

﴿وَثَمُودَ الَّذِينَ جَابُوا الصَّخْرَ بِالْوَادِ﴾

Da samũdãwa waɗanda suka fasa duwãtsu a cikin Wadi* suka yi gidãje)?

﴿وَفِرْعَوْنَ ذِي الْأَوْتَادِ﴾

Da Fir'auna mai turãku.

﴿الَّذِينَ طَغَوْا فِي الْبِلَادِ﴾

Waɗanda suka ƙẽtare iyãkarsu, a cikin garũruwa?

﴿فَأَكْثَرُوا فِيهَا الْفَسَادَ﴾

Sabõda haka, suka yawaita yin ɓarna a cikinsu.

﴿فَصَبَّ عَلَيْهِمْ رَبُّكَ سَوْطَ عَذَابٍ﴾

Sabõda haka Ubangijinka Ya zuba musu bũlãlar azãba.

﴿إِنَّ رَبَّكَ لَبِالْمِرْصَادِ﴾

Lalle ne, Ubangijinka Yana nan a mafaka.

﴿فَأَمَّا الْإِنْسَانُ إِذَا مَا ابْتَلَاهُ رَبُّهُ فَأَكْرَمَهُ وَنَعَّمَهُ فَيَقُولُ رَبِّي أَكْرَمَنِ﴾

To, amma fa mutum idan Ubangijibsa Ya jarraba shi, wãto Yã girmama shi kuma Ya yi masa ni'ima, sai ya ce: "Ubangijina Ya girmama ni."

﴿وَأَمَّا إِذَا مَا ابْتَلَاهُ فَقَدَرَ عَلَيْهِ رِزْقَهُ فَيَقُولُ رَبِّي أَهَانَنِ﴾

Kuma idan Ya jarraba shi, wãto Ya ƙuntata masa abincinsa, sai ya ce: "Ubangijina Ya walãkanta ni."

﴿كَلَّا ۖ بَلْ لَا تُكْرِمُونَ الْيَتِيمَ﴾

A'aha! Bari wannan, ai bã ku girmama marãya!

﴿وَلَا تَحَاضُّونَ عَلَىٰ طَعَامِ الْمِسْكِينِ﴾

Bã ku kwaɗaitã wa jũnanku ga (tattalin) abincin matalauci!

﴿وَتَأْكُلُونَ التُّرَاثَ أَكْلًا لَمًّا﴾

Kuma kuna cin dũkiyar gãdo, ci na tãrãwa.

﴿وَتُحِبُّونَ الْمَالَ حُبًّا جَمًّا﴾

Kuma kuna son dũkiya, so mai yawa.

﴿كَلَّا إِذَا دُكَّتِ الْأَرْضُ دَكًّا دَكًّا﴾

A'aha! Idan aka niƙa ƙasa niƙewa sosai.

﴿وَجَاءَ رَبُّكَ وَالْمَلَكُ صَفًّا صَفًّا﴾

Kuma Ubangijinka Ya zo, alhãli malã'iku na jẽre, sahu- sahu.

﴿وَجِيءَ يَوْمَئِذٍ بِجَهَنَّمَ ۚ يَوْمَئِذٍ يَتَذَكَّرُ الْإِنْسَانُ وَأَنَّىٰ لَهُ الذِّكْرَىٰ﴾

Kuma a ranar nan aka zo da Jahannama. A ranar nan mutum zai yi tunãni. To, inã fa tunãni yake a gare shi!

﴿يَقُولُ يَا لَيْتَنِي قَدَّمْتُ لِحَيَاتِي﴾

Yana dinga cẽwa, "Kaitona, dã na gabatar (da aikin ƙwarai) domin rãyuwata!"

﴿فَيَوْمَئِذٍ لَا يُعَذِّبُ عَذَابَهُ أَحَدٌ﴾

To, a rãnar nan bãbu wani mai yin azãba irin azãbar Allah.

﴿وَلَا يُوثِقُ وَثَاقَهُ أَحَدٌ﴾

Kuma bãbu wani mai ɗauri irin ɗaurinSa.

﴿يَا أَيَّتُهَا النَّفْسُ الْمُطْمَئِنَّةُ﴾

Yã kai rai mai natsuwa!

﴿ارْجِعِي إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةً مَرْضِيَّةً﴾

Ka koma zuwa ga Ubangijinka, alhãli kana mai yarda (da abin da Ya ƙaddara maka a dũniya) abar yardarwa (da sakamakon da zã a ba ka a Lãhira).

﴿فَادْخُلِي فِي عِبَادِي﴾

Sabõbda haka, ka shiga cikin bãyiNa (mãsu bin umurui a dũniya).

﴿وَادْخُلِي جَنَّتِي﴾

Kuma ka shiga AljannaTa (a Lãhira).

الترجمات والتفاسير لهذه السورة: