الشمس

تفسير سورة الشمس

الترجمة الهوساوية

هَوُسَ

الترجمة الهوساوية

ترجمة معاني القرآن الكريم للغة الهوسا ترجمها أبو بكر محمود جومي، نشرها مجمع الملك فهد لطباعة المصحف الشريف بالمدينة المنورة، عام الطبعة 1434. ملاحظة: ترجمات بعض الآيات (مشار إليها) تم تصويبها بمعرفة مركز رواد الترجمة، مع إتاحة الاطلاع على الترجمة الأصلية

﴿بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ وَالشَّمْسِ وَضُحَاهَا﴾

Ina rantsuwa da rãnã da hantsinta.

﴿وَالْقَمَرِ إِذَا تَلَاهَا﴾

Kuma da wata idan ya bi ta.

﴿وَالنَّهَارِ إِذَا جَلَّاهَا﴾

Da yini a lõkacin da ya bayyana ta.

﴿وَاللَّيْلِ إِذَا يَغْشَاهَا﴾

Da dare a lõkacin da ya ke rufe ta.

﴿وَالسَّمَاءِ وَمَا بَنَاهَا﴾

Da sama da abin da ya gina ta.

﴿وَالْأَرْضِ وَمَا طَحَاهَا﴾

Da ƙasã da abin da ya shimfiɗa ta.

﴿وَنَفْسٍ وَمَا سَوَّاهَا﴾

Da rai da abin da ya daidaita shi.

﴿فَأَلْهَمَهَا فُجُورَهَا وَتَقْوَاهَا﴾

Sa'an nan ya yi masa Ilhamar fãjircinsa da shiryuwarsa.

﴿قَدْ أَفْلَحَ مَنْ زَكَّاهَا﴾

Lalle ne wanda ya tsarkake* shi (rai) ya sãmi babban rabo.

﴿وَقَدْ خَابَ مَنْ دَسَّاهَا﴾

Kuma lalle ne wanda ya turbuɗe* shi (da laifi) ya tãɓe.

﴿كَذَّبَتْ ثَمُودُ بِطَغْوَاهَا﴾

Samũdãwa sun ƙaryata (Annabinsu), dõmin girman kansu.

﴿إِذِ انْبَعَثَ أَشْقَاهَا﴾

A lõkacin da mafi shaƙãwarsu ya tafi (wurin sõke rãkumar sãlihu).

﴿فَقَالَ لَهُمْ رَسُولُ اللَّهِ نَاقَةَ اللَّهِ وَسُقْيَاهَا﴾

Sai Manzon Allah ya gaya musu cewa: "Ina tsõratar da ku ga rãƙumar Allah da ruwan shanta!"

﴿فَكَذَّبُوهُ فَعَقَرُوهَا فَدَمْدَمَ عَلَيْهِمْ رَبُّهُمْ بِذَنْبِهِمْ فَسَوَّاهَا﴾

Sai suka ƙaryata shi, sa'an nan suka sõke ta. Sabõda haka Ubangijinsu Ya darkãke su, sabõda zunubinsu. Sa'an nan Ya daidaita ta (azãbar ga mai laifi da maras laifi).

﴿وَلَا يَخَافُ عُقْبَاهَا﴾

Kuma bã ya tsõron ãƙibarta (ita halakãwar).

الترجمات والتفاسير لهذه السورة: