البحث

عبارات مقترحة:

الآخر

(الآخِر) كلمة تدل على الترتيب، وهو اسمٌ من أسماء الله الحسنى،...

القدير

كلمة (القدير) في اللغة صيغة مبالغة من القدرة، أو من التقدير،...

القاهر

كلمة (القاهر) في اللغة اسم فاعل من القهر، ومعناه الإجبار،...

MUSULUNCI : Taqaitaccen Saqo game da Musulunci kamar yadda ya zo cikin Al-qur'ani da Sunnanr Annabi

الهوساوية - هَوُسَ

المؤلف Muhammad Bn Abdullahi Al-Suhaim ، مركز رواد الترجمة
القسم كتب وأبحاث
النوع نصي
اللغة الهوساوية - هَوُسَ
المفردات تعريف الإسلام
Littafi ne mai Muhimmanci wanda ya qunshi bayani game da Musulunci da yake bayanin mafi Muhimmancin Tushensa da koyarwarsa da kyawawunsa wanda aka samo su daga Tushe na Asali shi ne Al-qur'ani Maigirma da Kuma Sunnar Annabi da kuma Saqon da aka turashi zuwa ga baki xayan Baligai na Musulmai da Yarukansu a kowane lokaci da kuma ko ina suke duk da savanin Yanayi da kuma Hali

التفاصيل

MUSULUNCI 1-Musulunci shi Saqon Allah zuwa ga Mutane baki xayan su shi ne Saqon Allah wanzazze 2. Kuma Musulunci ba Addinin wasu kevantattun Mutane ba ne ko jinsi a'a Addinin Allah ne ga Mutane baki xayansu 3-Musulunci shi ne Saqon Allah wanda ya zo don cika Saqonnin Annabawa da Manzanni waxanda suka gabata -Amincin Allah ya tabbata a gare su- zuwa ga Al-ummansu 4. Annabawa Amincin Allah a gare su Addininsu xaya ne kuma Shari'unsu sun sha banban 5,Musulunci yana kira -Kamar yadda kowane Annabi yayi: Nuhu da Ibrahim da Musa da Sulaiman da Daud da Isa -Amincin Allah a gare su- zuwa ga Imani cewa Ubanji kaxai shi ne Allah wanda yayi halitta kuma mai raya wa mai kashewa Mai Mulki Mamallaki, kuma shi wanda yake gudanar da Al-amura, kuma shi ne mai jin Qai mai Tausasasawa 6: Allah Maxaukakin Sarki shi ne wanda yayi halitta kuma shi ne wanda ya cancanci Ibada shi kaxai, kuma ba'a bautawa kowa waninsa tare da shi 7: Allah shi ne Mahalicci ga baki xayan halitta abunda muke iya gani da waxan da bama iya gani, kuma duk wani abu da ba shi ba to shi abun Halitta ne da cikin halittunsa, kuma shi ya halicci Sammai da Qasa cikin kwana Shidda 8-Kuma Allah Maxaukakin Sarki bashi da abikin tarayya a cikin Mulkinsa da halittunsa ko Bayinsa 9. Allah Maxaukakin Sarki bai Haifa ba kuma ba'a haifeshi ba kuma bashi wani kini ko mai kamanceceniya da shi 10. Allah Maxaukakin Sarki baya sauka a cikin wani abu, ko kuma ya saje da jikin wani abu daga cikin halittunsa 11-Allah Maxaukakin Sarki Mai rangwame ne muka mai jin Qai ga bayinsa shi yasa ya aiko Manzanni kuma ya saukar da litattafai 12. Allah shi ne Ubangiji Mai jin qai shi kaxai wanda shi ne zai yi Hisabi ga Halittu a ranar Al-qiyama lokacin da zai tashe su baki xayansu daga Qaburburansu, saboda ya sakawa kowanne Mutum da aikin da yayi na Al-kairi ko sharri, saboda dik wanda yayi aiki nagari kuma yana mai Imani to yana da Ni'ama Matabbaciya, kuma duk wanda ya Kafirta kuma yayi mummunan aiki to yana da Azaba Mai girma a Lahira. 13. Allah Maxaukakin Sarki ya halicci Xan Adam daga turvaya, kuma ya sanya Zurriyarsa tana yaxuwa bayansa, saboda Mutane a Asalisu daidai suke, kuma babu banbanci a tsakanin jinsi da jinsi ko kuma Mutane kan Mutane sai da tsoron Allah. 14. Kuma kowane Yaro ana haifarsa ne akan Fixra 15. kuma babu wani Mutum da aka haifeshi da Savo ko ya gaji savon waninsa 16. Kuma Manufa na halittar Mutane ita ce bautar Allah shi kaxai 17. Musilunci ya Karrama Mutum -Maza da Mata- kuma ya xauke masa baki xayan Haqqoqinsa, kuma ya sanya shi abun tambaya akan baki xayan sauran Zaxuxxukansa, da Ayyukansa da kuma Tasarrufinsa, kuma ya xora masa nauyin kowane irin aiki da zai cutar da kansa ko ga wani akansa 18. kuma ya Sanya Namiji da Mace daidai da daidai wajen xaukar Alhakim aikinsu da kuma sakamako da bada lada 19. Musulunci ya karrama Mace, kuma ya sanya Mata su zamanto abokan tafiyar Maza, kuma ya lazamtawa Mazan ciyar da su idan ya kasance yana da iko, saboda haka ya Wajaba Uba ya ciyar da Xiyarsa, haka Uwa akan Xanta idan ya kasance ya Balaga kuma yana da Iko, haka Mata akan Mijinta 20. kuma Mutuwa ba Karewa bace ta har Abada, a'a ita wata tafiya daga Gidan aiki zuwa gidan Sakamako, kuma Mutuwa yana samun Jiki da Ruhi, Mutuwar Ruhi ita ce rabuwar Ruhi daga jiki, sannan kuma ya dawo zuwa jinkin bayan tashin Al-qiyama, kuma Ruhi baya tafiya zuwa wani jikin bayan Mutuwa, kuma baya sake tsiruwa a wabi jikin daban 21, kuma Musulunci yana kira ne zuwa Imani da jigajigan Imani Manya, kuma shi ne Imani da Allah da Mala'ikunsa da Imani da litattafan Allah Kamar Al-taura da linjila da Zabuea -kafin jirkita su- da kuma Al-qurani, da kuma Imani da bai xayan Annabawa da Manzanni -Amincin Allah a gare su- kuma yayi Imani da cika makin su shi Annabu Muhaddu Manzon Allah cikamakin Annabawa da Manzanni da Kuma Imani da Ranar Lahira kuma ya sani cewa Rayuwar Duniya da ita ce Qarshe da kuma da Halittu sun zama tsantsar Wasa kuma Imani da Hukuncin Allah da Qaddarara 22. kuma Annabwa Ma'asumai ne -Amincin Allah a gare su- cikin abunda suka isar da shi daga Allah, kuma Ma'asumai ne ga barin dukkanin abunda ya sava da Hankali, ko kuma kyawawan halaye su kyamace shi, kuma Annabawa an xira musu isar da Umarnin Allah ga bayinsa, kuma Annabawa basu da wani abu na abunda ya kevanxi Allantaka; aa suma Mutane kamar sauran Mutane Allah yai Musu wahayi da Manzantakarsa 23. Kuma Musulunci yana kira zuwa ga bautar Allah shi kaxai da ginshiqan Ibada Manya, sune Sallah wacce ita ce tsayuwa da Ruku'u da Sujada da anbaton Allah da yabonsa da kuma Addu'a, kuma Mutum yana sallatarta sau biyar a wuni, kuma a cikinta babu banbanci tsakanin Mawadaci da talaka da shugaba da kuma Talaka a sahu qwara xaya a cikin Sallah da kuma Zakka wacce taje wani yanki ne kaxan daga cikin Dukiya -daidai da sharaxai da kuma gwargwado wanda Allah ya qaddara,kuma tana wajaba ne a Dukiyar Mawadata kuma a bada ita ga Talakawa da wasunsu, kuma sau xaya ce a Shekara, da kuma Azumi wanda shi ne kamewa ga barin ci da sha da rana a watan Azumi, kuma yana koyawa Mutum Dauriya da haquri, da kuma Hajji wanda shi ne: Nufar Xakin Allah a Makka Mai Alfarma sau xaya a rayuwa ga Mai Iko wanda zai iya, kuma a cikin wannan Hajjin akwai daidaito ga kowa da kowa wajen fuskanta zuwa ga Mahalicci SWT, kuma Banbance banbance da Nuna wani fifiko duka ya kau a cikin sa. 24. kuma daga cikin mafi girman abunda Ibada ta kevanta da shi a Musulunci cewa yadda ake yinta da lokutanta da sharaxanta Allah SWT ne ya Shar'anta ta su kuma ya isar da ita ga Manzonsa SAW, kuma babu wani Mutum da ya da yayi shigege a cikin su ta hanyar qari ko ragi har zuwa wannan rana, kuma baki xayan Manyan Ibadu baki xayan Annabwa sunyi kira zuwa gare su -Amincin Allah a gare su- 25, Manzon Musulunci shi ne Muhammad Bn Abdullahi daga cikin Zuriyar Annabi Isma'ila Xan Annabi Ibrahim -Amincin Allah a garesu- an haife shi Makka a shekara ta 571 Miladiyya, kuma yai Hijita zuwa madina, kuma baiyi tarayya sa Mutanensa ba a Al-amuran bautar Gunki, sai dai shi ya kasance yana tarayya da su a Ayyukan kirki, kuma ya kasance kan kyawawan Halaye tun kafin a aiko shi, kuma Mutanensa sun kasance suna kiransa Amintacce, kuma Allah ya aiko shi yayin da ya cika Shekara Arba'in kuma Allah ya Qarfafe shi da da Ayoyi (Mu'ajizozi) Masu girma, kuma girmansu shi ne Al-qur'ani Mai girma, kuma shi ne mafi girman Ayoyin Annabawa, kuma shi ne Ayoyin Annabwa har zuwa yau xin nan, kuma yayin da Allah ya cika wannan Addinin, kuma Manzon Allah SAW ya isar da shi matuqar isarwa sai ya yi wafati she, Kuma Manzon Allah karunsa suna Sittin da Uku, kuma aka binne shi a garin Madina SAW Kuma manzon Allah Muhammad SAW shi cika makin Annabawa da Manzanni Allah ya aiko shi da shiriya da Addini na gaskiya don ya futar da Mutane daga duhun Bautar Gumaka da Kafirci da Jahilci zuwa hasken Kaxaita Allah da Imani, da Kuma Allah yai masa shida cewa shi ne ya aiko shi yana mai kira zuwa gare shi da umarninsa 26. Kuma Shari'ar Musulunci wacce Manzon Allah Muhammad SAW ya zo da ita ita ce cika makin Saqonnin Allah da kuma shari'ar Ubangiji; kuma ita ce Shari'ar cikawa, kuma a cikinta akwai gyaruwar Addinin Mutane da Duniyarsu, kuma tana tsarewa a mataki na farko ga Addinin Mutane da Jininsu da Dukiyarsu da Hankulansu da Zuriyarsu, kuma ta shafe kowa ce Shari'a da ta gabace ta na daga Shari'u, kamar yadda ta soke vangaren wasun da suka gabaceta. 27. Kuma Alla SWT baya karvar wani Addini in ba Musulunci ba wanda shi ne wanda Annabi Muhammad SAW ya zo da shi, kuma duk wanda ya riqi wanin Musulunci Addini to ba za'a larva ba 28. Al-qu'ani maigirma shi ne littafin da Allah yai wahayinsa ga Manzo Muhammad SAW kuma shi ne zancen Ubangijin Talikaia aikowa Manzon Allah SAW kuma shi ne zancen Ubangijin Talikai wanda Allah ya qure Mutum da Al-jann kan su zo da kwatankwacin sa, ko Sura kwatankawcinsa, kuma har yau qurewa bata qare ba, Kuma Al-qurani yana bada Amsar Muhimmai masu yawa da Muliyoyin Mutane suka gaza, Kuma Al-qurani Maigirma abun kiyayewa ne har zuwa yau xin nan da yaren larabci da ya sauka da shi, kuma ba'a rage ko harafi xaya ba, kuma yana nan a buge ana yaxa shi, Kuma littafi ne Maigirma Mai gajiyarwa wanda ya dace da a Karanta shi ko a karanta Fassararsa, Kamar yadda Sunnar manzon Allah SAW da koyarwarsa da Tarihinsa ababan kiyayewa ne kuma ababan rawaito ne daidai da tsanin jerin Masu riwaya da aka yarda da su, kuma an buga ta da Larabci wanda Manzon Allah SAW yayi magana da shi kuma an fassara ta a Yaruka da yawa, kuma Al-qur'ani da Sunnar Manzon Allah su ne Tushen qwara xaya na Hukunce hukuncen Musulunci da Shari'unsa, saboda Musulunci, saboda ba'a xaukar Musulunci daga aiyukan xaixaikun Mutane da suke danganta kansu da Musulunci; kawai ana xauka ne daga Wahayin Allah a Al-qur'ani Maigirma da Sunnar Annabi 29. Kuma Musulunci yana Umarni da kyautatawa Iyaye, koda kuwa sun kasance ba Musulmai ba ne, kuma ya na wasiyya da 'Ya'ya. 30-. Musulunci yana Umarni da Adalci a cikin Magana da kuma Aiki koda kuwa tare da Abokan gaba ne 31, Kuma Musulunci yana Umarnini da a kyautatawa halitta baki xaya, kuma yana kira zuwa kyawawan Halaye, da kuma kyawawan Ayyuka 32. Kuma Musulunci yana Umarni da kyawawan Halaye Kamar Gaskiya da sauke Amana da kuma kamewa da Kunya da Gwarzanta da Karamci da taimakawa Mabuqaci da kai gudun mawa ga wanda yake cikin wani hali, da ciyar da Mai jin yinwa, da kyautata Makwabtaka, da Sadar da Zumunci, da tausasawa Dabbobi 33. Musulunci ya Halatta abubuwa masu daxi na abun ci da sha, kuma yayi umarni da tsarkin Zuciya da jiki saboda haka ya halatta Aure, Kamar yadda ya Umarci Annabawa -Amincin Allah a gare su- da hakan, saboda su suna Umarni ne da dukkan abu mai kyau 34. Musulunci ya haramta dukkan Tushen dukkan Haramun kamar Shirka da bautar Gumaka, da shaci faxi ga Allah bada Ilimi ba, da kashe 'ya'ya. da kashe ran da Allah ya haramta, da varna a bayan qasa, da Sihiri da Al-fasha ta Fili da ta Voye da Zina da Liwaxi, kuma ya haramta Riba, da cin Mushe, da abunda aka yanka ga Gumaka da Dodanni, da kuma cin Naman Alade, da sauran Najasa da Kazanta, kuma ya Haramta cin Dukiyar Maraya da tauye Mudu da ma'auni, kuma ya haramta yanke Zumunci kuma Annabawa -Amincin Allah a gare su- baki xayansu sun haxu kan haramcin waxan nan Abubuwan 35. Musulunci ya hana Munanan Halaye Kamar Qarya da Ha'inci da Yaudara da Ha'inci da Danfara, da Hassada da Mummunan kaidi da Sata da Zalunci, kuma ya na hana dukkan wani Mummunan Hali 36. Musulunci ya hana Muna nan Mua'amalolin kuxi waxanda cikinsu akwai riba ko cutarwa ko kuma garari ko zalunci ko Al-gus, ko kuma yana kaiwa zuwa ga Masifu, ko Cutarwa da zata game baki xayan Kasashe da kuma Mutane da xaixaiku 37. Musulunci ya zo da kiyaye Hankula da Haramta dukkan abunda zai vata shi kamar Shan Giya, kuma Musulunci ya xaga Darajar Hankali kuma ya sanya shi doron dora nauyi, kuma ya 'Yantashi daga dabaibayin Taysuniyoyo da bautar gumaka kuma a Musulunci babu wasu Voyayyun abubuwa ko hukunce Hukunce da suka kevanci Wasu Mutane koma bayan Wasu, kuma baki xayan hukunce Hukuncen sa da Shari'unsa sunyi daidai da hankula Ingantattu, kuma ita ce daidai da Adalci da Hikima 38. kuma Addinann Vata idan Mabiyansu basu gamsu da abunda yake cikinsu ba na kwangaba kwanbaya, da Al-amuran da hankali ba zai xauka ba sai Malaman Mabiya Addinin sai su ruxi Mabiyan da cewa ai Addini sama yake da Hankali. kuma cewa Hankali ai dole sai da shi wajen fahimtar Addini da kuma riqeshi wanda ko Musulunci ya sanya Hankali wani Haske ne da yake Haskawa Hankali Hanya; saboda Ma'abota Addinan Qarya sunason Mutum ne ya bar Hankalinsa ya bi su, kuma Musulunci yana son Mutum ne da ya farkar da hankalinsa, don yasan haqiqanin Al-amura kamar yadda yake 39. Musulunci yana girmama Ingantaccen Ilimi, kuma yana kwaxaitarwa kan binciken Ilimi wanda yake babu son rai a cikinsa, kuma yana kira zuwa Nazari da Tunani cikin Kawunanmu da kuma halittu da suke kewaye da mu, da kuma sakamakon Ilimi ingantacce don Ilimi waxanda basa cin karo da Musulunci. 40. kuma Allah baya Karvar aiki ko ya bada lada akansa a lahira sai daga waxanda sukai Imani da Allah kuma suka gasgata Manzanninsa -Amincin Allah a gare su- kuma Allah baya karvar ibadu sai da abunda ya Shar'anta, saboda mai zai sa Mutum ya kafircewa Allah kuma ya qaunaci ladansa? kuma Allah baya karvar Imani wani Mutum sai idan yayi Imani da Annabawa -Amincin Allah a gare su baki xaya- Kuma yayi Imani da Saqon Annabi Muhammad SAW. 41.Lallai Manufar Sakonnin Allah baki xayansu shi ne: cewa lallai Addinin Gaskiya ya xaukaka Xan Adam, saboda ya kasance tsantsan Bawan Allah Ubangijin Talikai, kuma ya 'Yanta shi daga bautar Mutane ko kuma wani abun Duniya ko kuma Tatsunuyoyi, saboda Musulunci -Kamar yadda kake ganinsa- baya tsarkake Mutane ya xagasu sama da matsayinsu, kuma baya sanya su Alloli ababan bauta 42.Allah ya Shar'anta tuba a Musulunci wanda shi ne Maida komai da komai xin Xan Adam zuwa ga Ubangijinsa, da barin Zunubai, kuma Musulunci yana rushe abunda yake kafinsa na zunubai, kuma tuba yana wanke abunda ya gabace shi na zunubai, saboda haka babu wata buqata mutum ace sai ya bayyana laifukansa a Mutane. 43.Saboda a cikin Musulunci dangantaka tsakanin Mutum da Allah kai tsaye ta ke, saboda haka baka buqatar wani Mutum da zai kasance tsani tsakaninka da Allah, saboda Musulunci ya hana Mu sanya Mutane su zamanto Alloli ko kuma suna tarayya da Allah cikin Allantakarsa da Bautarsa 44.a qarshen wannan littafin muna tunsarwa cewa Mutane duk da savanin Zamaninsu da Qabilunsu, da garuruwan su kai baki xayan Duniyar Mutane sun sava a wajen Tunanisu da Manufofin su, sun yi hannun riga wajen garuruwansu da Ayyukan su, saboda haka suna da buqatar wani Mai shiryarwa da zai xorasu kan Turba, da wani tasri da haxe kansu, da wani Jagora da zai kare su, kuma Manzanni -Amincin Allah a gare su- sun jivanci hakan da Wahayi daga Allah Maxaukaki suna shiryar da Mutane zuwa Hanyar Al-kairi da Shiriya, kuma ya haxa su akan Shari'ar Allah kuma suna Hukunci da Gaskiya a tsakaninsu, saboda Al-amuransu su tafi daidai dai dai da yadda waxan nan suka amsawa Manzannin, da kuma kusancinsu da waxan nan lokutan na Saqonnin Allah, kuma Allah ya cika Saqonin Manzancin da Manzo Annabi Muhammad SAW kuma ya Hukunta mata Wanzuwa, kuma ya sanyata Shiriya ga Mutane da kuma Rahama da Haske da Shiriyarwa zuwa Tafarki Mai isarwa zuwa ga Allah SWT 45.Saboda haka nake roqonka ya kai Xan Adam ka tsaya ga Allah tsayuwa ta gasliya kana mai tsiraita kanka daga Kwaikwayo da Al-ada, kuma kasani cewa kai bayan Mutuwarka zaka koma ne zuwa ga Ubangijinka, kuma ka kalli kanka, da kuma wasu sassa da suke kewaye da kai, ka Musulunta zaka rabauta a Duniyarka da Lahirar ka, idan kuma kana son shiga Musulunci babu abunda zaka yi sai kawai ka shaida cewa Babu abun bauta da gaskiya sai Allah, kuma cewa Annabi Muhammad Manzon Allah ne, kuma kayi watsi da duk abunda ake bautawa koma bayan Allah, kuma kayi Imani cewa Allah zai tashi waxanda suke cikin Qabari kuma cewa Hisabi da sakamako gaskiya ne, to idan ka shaida da Wannan Shaidawar to haqiqa ka zama Musulmi, saboda haka bayan haka zaka bautawa Allah da abunda ya Shar'anta na Sallah da Zakka da Azumi, da kuma Hajjatar Xakin Allah idan ka samu Iko yin hakan,  MUSULUNCITaqaitaccen Saqo game da Musulunci kamar yadda ya zo cikin Al-qur'ani da Sunnanr Annabi(Kwafi ne da yake qunshe da dalilai daga cikin Al-qur'ani Maigirma da kuma Sunnar Annabi)Littafi ne mai Muhimmanci wanda ya qunshi bayani game da Musulunci da yake bayanin mafi Muhimmancin Tushensa da koyarwarsa da kyawawunsa wanda aka samo su daga Tushe na Asali shi ne Al-qur'ani Maigirma da Kuma Sunnar Annabi da kuma Saqon da aka turashi zuwa ga baki xayan Baligai na Musulmai da Yarukansu a kowane lokaci da kuma ko ina suke duk da savanin Yanayi da kuma Hali 1-Musulunci shi Saqon Allah zuwa ga Mutane baki xayan su shi ne Saqon Allah wanzazzeMusulunci shi ne saqon Allah ga Mutane baki xayansu Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma ba Mu aika ka ba fãce zuwa ga mutãne gabã ɗaya, kanã mai bãyar da bushãra kuma mai gargaɗi, kuma amma mafi yawan mutãne ba su sani ba.(Saba'i: 28)Allah Madaukakin Sarki ya ce:Ya ku mutane ni manzon Allah ne zuwa gare ku baki DayaAl-a'araf: 158Allah Madaukakin Sarki ya ce:Yã kũ mutãne! Haƙĩƙa, Manzo yã je muku da gaskiya daga Ubangijinku. Sabõda haka ku yi ĩmãni yã fi zama alhẽri a gare ku. Kuma idan kun kãfirta, to, Allah Yanã da abin da ke cikin sammai da ƙasa. Kuma Allah Yã kasance Masani, Mai hikima.Al-nisa'a: 170Musulunci shi ne Saqon Allah dawwamamme kuma shi ne cika makin Saqon Ubangiji Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Muhammadu bai kasance uban kõwa ba daga mazanku, kuma amma shĩ yã kasance Manzon Allah kuma cikon Annabãwa. Kuma Allah Ya kasance Masani ga kõme.Al-ahzab: 40 2. Kuma Musulunci ba Addinin wasu kevantattun Mutane ba ne ko jinsi a'a Addinin Allah ne ga Mutane baki xayansuKuma Musulunci ba Addinin wasu kevantattun Mutane bane a'a Addinin Allah na Mutane baki xayansu, kuma farkon Umarni a cikin Al-qur'ani Maigirma shi ne faxin Allah Maxaukakin Sarki:Yã ku mutãne! Ku bauta wa Ubangjinku, Wanda Ya halicce ku, kũ da waɗanda suke daga gabãninku, tsammãninku ku kãre kanku!Al-Baqara:21Allah Madaukakin Sarki ya ce:Ya ku Mutane kuji tsoron Ubangijinku wanda ya halicce ku daga rai kwara xaya kuma ya halitta masa rai kuma ya waatsa daga cikinsu Maza da MataAl-nisa'a: 1Kuma an rawaito daga Ibn Umar -Allah ya yarda da su- cewa Manzon Allah SAW ya yi Huxuba ga Mutane Ranar buxe Makka sai ya ce:"Ya ku Mutane lallai Allah ya kawar muku da haukan Jahilci da jiji da kai da iyaye saboda haka Mutane sun kasu biyu: Mai biyayya ga Allah kuma mai tsonsa da kuma Mai girma a wajen Allah, da kuma fajiri tavavve wulakance a wajen Allah kuma dukkan 'Yan Adam kuma Allah ya halicci Annabi Adam daga tavo Allah ya ce: "Ya ku Mutane lallai mun halicce ku daga Namiji fa Mace kuma muka sanya ku Jama'a da Qabilu don ku san juna lallai mafi tsoron Allah a cikin ku shi ne mafi tsoron Allah, lallai Allah Masani ne kuma mai bada labari" Al-hujrat: 13Tirmizi ne ya rawaito shi (3270)Kuma ba zaku samu ba a cikin Umarnin Al-qurani Maigirma da Umarnin Manzon Allah SAW wani Hukunci da ya keve wasu Mutane ko Qungiya saboda kawai Jininsu ko don Qabilar su ko jinsinsu 3-Musulunci shi ne Saqon Allah wanda ya zo don cika Saqonnin Annabawa da Manzanni waxanda suka gabata -Amincin Allah ya tabbata a gare su- zuwa ga Al-ummansuMusulunci shi ne Saqon Allah wanda ya zo don cika Saqonnin Annabawa da Manzanni waxanda suka gabata -Amincin Allah ya tabbata a gare su- zuwa ga Al-ummansuLalle ne Mu, Mun yi wahayi zuwa gare ka, kamar yadda Muka yi wahayi zuwa ga Nũhu da annabãwa daga bãyansa. Kuma Mun yi wahayi zuwa ga Ibrãhĩma da Ismã'ĩla da Is'hãƙa da Yaƙũbu da jĩkõki da ĩsa da Ayũba da Yũnusa da Hãruna da Sulaimãn. Kuma Mun bai wa Dãwũda zabũra.Al-Nisaa:163Kuma wannan Addinin wanda Allah Allah yayi Wahayinsa ga Manzon Allah SAW shi ne Addini wanda Allah ya Shar'anta ga Annabawa da suka gabata kuma yayi musu Wasiyya da shi Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Ya shar'anta muku, game da addini, abin da Ya yi wasiyya da shi ga Nũhu da abin da Muka yi wahayi da shi zuwa gare ka, da abin da Muka yi wasiyya da shi ga Ibrãhĩm da Mũsã da Ĩsã, cẽwa ku tsayar da addini sõsai kuma kada ku rarrabu a cikinsa. Abin da kuke kira zuwa gare shi, ya yi nauyi a kan mãsu shirki. Allah na zãɓen wanda Yake so zuwa gare Shi, kuma Yanã shiryar da wanda ke tawakkali gare Shi, ga hanyarSa.Al-shura:13Kuma wannan Addinin wanda Allah Allah yayi Wahayinsa ga Manzon Allah SAW shi ne Addini wanda Allah ya Shar'anta ga Annabawa da suka gabata kuma yayi musu Wasiyya da shi Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma abin da Muka yi wahayi zuwa gare ka, daga Littãfi, shi ne gaskiya mai gasgata abunda ya gabace shi lallai Allah mai bada labari ne ga Bayinsa kuma mai haniFaxir: 31 4. Annabawa Amincin Allah a gare su Addininsu xaya ne kuma Shari'unsu sun sha banbanAddinin Annabwa -Amincin Allah a garesu xaya nr sai dai Shari'unsu ne suka sassava, Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma Mun saukar da Littãfi zuwa gare ka da gaskiya yanã mai gaskatãwa ga abin da yake a gaba gare shi daga Littãfi (Attaura da Injĩla), kuma mai halartãwa a kansa sai ka yi hukunci a tsakãninsu da abin da Allah Ya saukar kuma kada ka bĩbiyi son zũciyõyiniu daga abin da ya zo maka daga gaskiya Ga kõwanne daga gare ku Mun sanya sharĩa da hanya (ta bin ta) Kuma dã Allah Yã so, dã Yã sanya ku al'umma guda, kuma amma dõmin Ya jarraba ku a cikin abin da Ya bã ku Sai ku yi tsere ga ayyukan alheri Zuwa ga Allah makõmarku take gabã ɗaya Sa'an nan Ya bã ku lãbãri ga abin da kuka kasance kunã sãɓãwa a cikinsa.Al-Ma'ida: 48Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:"Ni ne mafi cancantar Mutane da Isa Xan Maryam a Duniya da Lahira kuma Annabawa juna ne, sai dai Iyayensu Daban daban Amma Addinisu xaya ne"Bukhari ne ya rawaito shi (3443) 5,Musulunci yana kira -Kamar yadda kowane Annabi yayi: Nuhu da Ibrahim da Musa da Sulaiman da Daud da Isa -Amincin Allah a gare su- zuwa ga Imani cewa Ubanji kaxai shi ne Allah wanda yayi halitta kuma mai raya wa mai kashewa Mai Mulki Mamallaki, kuma shi wanda yake gudanar da Al-amura, kuma shi ne mai jin Qai mai TausasasawaMusulunci yana kira -Kamar yadda kowane Annabi yayi: Nuhu da Ibrahim da Musa da Sulaiman da Daud da Isa -Amincin Allah a gare su- zuwa ga Imani cewa Ubanji kaxai shi ne Allah wanda yayi halitta kuma mai raya wa mai kashewa Mai Mulki Mamallaki, kuma shi wanda yake gudanar da Al-amura, kuma shi ne mai jin Qai mai TausasasawaYã kũ mutãne! Ku tuna ni'imar Allah a kanku. Shin, akwai wani mai halitta wanin Allah da zai azurta ku daga sama da, ƙasã? Bãbu wani abin bautãwa, fãce Shi. To, yãya ake karkatar da ku?Faxir: 3Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Ka ce: "Wãne ne Yake azurtã ku daga sama da ƙasa? Shin kõ kuma Wãne ne Yake mallakar jĩ da ganĩ, kuma Wãne ne Yake fitar da mai rai daga mamaci, kuma Ya fitar da mamaci daga mai rai, Kuma Wãne ne Yake shirya al'amari?" To, zã su ce: "Allah ne." To, ka ce: "Shin fa, bã zã ku yi taƙawa ba?"Yunus: 31Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kõ wãne ne yake fã ra halitta sa'an nan kuma ya mayar da ita, kuma Wãne ne Ya azurta ku daga sama da ƙasa? Ashe, akwai wani abin bautãwa tãre da Allah? Ka ce: "Ku kãwo dalĩlinku idan kun kasance mãsu gaskiya."Al-naml: 64Kuma baki xayan Annabawa da Manzanni -Amincin Allah a gare su- an aiko su ne da Da'awa zuwa ga Bautar Allah shi kaxai Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika a cikin kõwace al'umma da wani Manzo (ya ce): "Ku bauta wa Allah, kuma ku nĩsanci ¦ãgũtu." To, daga gare su akwai wanda Allah Ya shiryar, kuma daga cikinsu akwai wanda ɓata ta wajaba a kansa. Sai ku yi tafiya a cikin ƙasa, sa'an nan ku dũba yadda ãƙibar mãsu ƙaryatãwa ta kasance.Al-Nahl: 36Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma ba Mu aiki wani Manzo ba a gabãninka fãce Munã yin wahayi zuwa gare shi, cẽwa "Lalle ne Shi, bãbu abin bautãwa fãce Nĩ, sai ku bauta Mini."Al-anbiyaa: 25Sai Allah ya bada labari game da Annabi Nuhu -Amincin Allah a gare shi- da cewa:"Yã mutãnẽna! Ku bauta waAllah! Bã ku da wani abin bautãwa waninSa. Lalle ne nĩ, inã yimuku tsõron azãbar wani Yini mai girma."Al-a'araf: 59Kuma ba daxin Allah Annabi Ibrahim -Amincin Allah a gare shi- cewa shi ya ce:Da Ibrãhĩm a lõkacin da ya ce wa mutãnensa, "Ku bautã wa Allah ku bĩ Shi da taƙawa. Wannan Shĩ ne alhẽri a gare ku idan kun kasance kunã sani.Al-ankabut: 16Kuma Annabi Salihu -Amincin Allah a gareshi- ya ce: Kamar yadda Allah ya bada labarinsaYã mutãnena! Ku bauta wa Allah; bã ku da wani abin bauta wa wanninSa. Haƙĩƙa hujja bayyananniya tã zo muku daga Ubangijinku! wannan rãƙumar Allah ce, a gare ku, wata ãyã ce. Sai ku bar ta ta ci, a cikin ƙasar Allah, kuma kada ku shãfe ta da wata cũta har azãba mai raɗaɗi ta kãmã ku."Al-aaraf: 73Kuma Annabi Shuaibu -Amincin Allah a gareshi- ya ce: Kamar yadda Allah ya bada labarinsa"Ya mutãnena! Ku bauta wa Allah; bã ku da wani abin bauta wa waninSa. Lalle ne, wata hujja bayyananniya daga Ubangijinku tã zõ muku! Sai ku cika mũdu da sikeli kumakada ku nakasa wa mutãne kãyansu, kuma kada ku yi fasãdi a cikin ƙasa a bãyan gyaranta. Wannan ne mafi alhẽri a gare ku, idan kun kasance mũminai."Al-a'araf: 85Al-a'araf: 85"Kuma Nĩ Nã zãɓe ka. Sai ka saurãra ga abin da ake yin wahayi."(13)"Lalle, Nĩ Ni ne Allah. Bãbu abin bautawa fãce Ni. Sai ka bauta Mini, kuma ka tsayar da salla dõmin tuna Ni." (14)Xaha: 13-14Kuma Allah ya ce yana bada labarin Annabi Musa -Amincin Allah a gareshi-cewa shi ya nemi tsari da Allah sai ya ce:Kuma Mũsã ya ce: "Lalle nĩ, nã nẽmi tsari da Ubangijĩna kuma Ubangijinku, daga dukan makangari, wanda bã ya ĩmani da rãnar Hisãbi."Ghafir: 27Sai Allah ya bada labari game da Annabi Annabi Isa-Amincin Allah a gare shi- da cewa:"Lallai Allah ne Ubangijina kuma Ubangijinku, sai ku bauta Masa. Wannan shi ne tafarki madaidaici."Aal Imran: 51Sai Allah ya bada labari game da Annabi Annabi Isa-Amincin Allah a gare shi- har wa yau da cewa:Ya ku Banu Isra’ila ku bautawa Allah Ubangiji na kuma Ubangijinku hakika duk wanda ya hada shi da abokin tarayya haqiqa Allah ya haramta masa Aljannah sannan mokomarsa wutaAl-Ma'ida: 72Kai har a Al-taura da linjila qarfafawa ta zo a cikinsu kan Bautar Allah shi kaxai saboda ya zo cikin Sifr Al-Tathniya fadin Annabi Musa -Amincin Allah a gare shi- faxinsa(Ka ji ya kai Isra'il Ubangiji shi ne Ubangijinmu ubangiji qwara xaya)Kuma Qarfafawa kan Tauhidi ta zo a cikin Linjila cewa Marqus lokacin da yake cewa da Annabi Isa -Amncin Allah a gareshi-(Lallai Farkon abunda Wasiyya ta qunsa su ne: Ka ji ya kai Isra'il Ubangiji shi ne Ubangijinmu ubangiji qwara xaya)Kuma Allah yana bayyanawa cewa baki xayan Annabawa an aiko sirma u ne da wannan Sako Mai girma shi ne kra zuwa ga kaxaita Allah, Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika a cikin kõwace al'umma da wani Manzo (ya ce): "Ku bauta wa Allah, kuma ku nĩsanci ¦ãgũtu." To, daga gare su akwai wanda Allah Ya shiryar, kuma daga cikinsu akwai wanda ɓata ta wajaba a kansa. Sai ku yi tafiya a cikin ƙasa, sa'an nan ku dũba yadda ãƙibar mãsu ƙaryatãwa ta kasance.Al-Nahl: 36kuma Allah Maxaukaki ya ceKa ce: "Shin, kun gani, abin da kuke kira, wanda yake baicin Allah? Ku nũna mini, menene suka halitta daga ƙasa? Kõ kuwa sunã da tãrayya a cikin sammai? Ku zo mini da wani littãfi na gabãnin wannan (Alƙur'ãni) kõ wata alãma daga wani ilmi, idan kun kasance mãsu gaskiya."Al-ahqaf: 4Shiekh Al-si'ady -Allah ya yi masa Rahama ya ce:(saboda an sani cewa jayayyar Mushirikai da a cikin shirkarsu bai dogara kan wasu Hujjoji ba ko Dalili, kaxai ya dogara ne kan zato na qarya, da vatattun tunanuka da hankula guvatattu abunda zai nuna maka gurvatarsu bibiyar halayensu da ilimansu da ayyukansu da duba halin waxanda suka qarar da rayuwarsu a bautarsa shin ya anfane su (ai abubuwan da suke bautawa koma bayan Allah) da wani abu a Duniya ko a Lahira? )Taisiru Karimu Al-mannan: 779 6: Allah Maxaukakin Sarki shi ne wanda yayi halitta kuma shi ne wanda ya cancanci Ibada shi kaxai, kuma ba'a bautawa kowa waninsa tare da shiAllah shi ne wanda ya cancanci a bauta masa shi kaxai kuma ba'a bauta masa tare da wani Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Yã ku mutãne! Ku bauta wa Ubangjinku, Wanda Ya halicce ku, kũ da waɗanda suke daga gabãninku, tsammãninku ku kãre kanku! (21)Wanda Ya sanya muku ƙasa shimfiɗa, kuma sama gini, kuma Ya saukar da ruwa daga sama, sa'an nan Ya fitar da abinci daga 'ya'yan itãce game da shi, sabõda ku. Sabõda haka kada ku sanya wa Allah wasu kĩshiyõyi, alhãli kuwa kuna sane. (22)Al-Baqara: 21-22Saboda wanda ya halicce mu kuma ya halicci tsaraikun da suka gabace mu kuma ya sanya Qasa shinfixa a gare mu kuma ya saukar mana da Ruwa daga sama sai ya futar mana da 'ya'yan Itatuwa Arziqi a garemu; to shi ne wanda ya cancanci da bauta shi kaxai Allah Maxaukaki ya ce:Yã kũ mutãne! Ku tuna ni'imar Allah a kanku. Shin, akwai wani mai halitta wanin Allah da zai azurta ku daga sama da, ƙasã? Bãbu wani abin bautãwa, fãce Shi. To, yãya ake karkatar da ku?Faxir: 3Saboda wanda yayi halitta kuma yake Azurtata shi ne wanda ya canxanci Ibada shi kaxai kuma Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Wancan ne Allah Ubangijinku. Bãbu wani abin bautãwa fãce Shĩ, Mahaliccin dukan kõme. Sabõda haka ku bauta Masa kuma Shi ne wakĩli a kan dukan, kõme.Al-an'am: 102Kuma duk abunda aka bautawa koma bayan Allah to bai cancanci bauta ba; saboda bai iya mallakar qwayar zarra ba a Sammai ko a Qasa kuma shi ba abokin tarayya ba ne a cikin wani abu ko kuma mai taimako ko mai Agazawa Allah saboda me to za'a kirawo tare da Allah ko a sanya masa abokin tarayya, Allah Maxaukaki ya ce:Ka ce: "Ku kirãyi waɗanda kuka riya (cẽwa abũbuwan bautãwa ne) baicin Allah, bã su Mallakar ma'aunin zarra a cikin sammai, kuma bã su Mallakarsa a cikin ƙasa kuma bã su da wani rabon tãrẽwa a cikinsu (sammai da ƙasa), kuma bã Shi da wani mataimaki daga gare su.Saba'i: 22Kuma Allah SWT shi ne wanda ya halicci waxan nan Halittun kuma ya samar da su daga babu kuma samuwarsu yana nuna samuwarsa da Allantakarsa Allah Maxaukaki ya ce:Kuma akwai daga ãyõyinSa, Ya halitta ku daga turɓãya, sai gã ku kun zama mutum, kunã wãtsuwa. (20)Kuma akwai daga ãyõyinsa, Ya halitta muku mãtan aure daga kanku, dõmin ku natsu zuwa gare ta, kuma Ya sanya sõyayya da rahama a tsakãninku. Lalle a cikin wancan akwai ãyõyi ga mutãne mãsu yin tunãni.(21).Kuma akwai daga ãyõyinSa halittar sammai da ƙasã da sãɓã, war harsunanku, da launukanku. Lalle a cikin wannan akwai ãyõyi ga mãsu ilmi. (22)Kuma akwai daga cikin ãyõyinSa, barcinku a cikin dare da rãna, da nẽmanku ga falalarsa. Lalle a cikin wannan akwai ãyõyi ga mutãne mãsu saurãrãwa.(23)Kuma akwai daga cikin ãyõyinSa, Ya nũna muku walƙiya a kan tsõro da ɗammãni kuma Ya dinga saukar da ruwa daga sama Sa'an nan Ya rãyar da ƙasã game da shi a bãyan mutuwarta. Lalle a cikin wannan akwai ãyõyi ga mutãne mãsu hankaltawa.(24)Kuma akwai daga ãyõyinsa, tsayuwar sama da asƙã bisa umurninsa, sa'an nan idan Ya kira ku, kira ɗaya, daga ƙasã, sai gã ku kunã fita.(25)Kuma wanda ke cikin sammai da ƙasã Nãsa ne shi kaɗai. Dukansu mãsu tawãli'u ne a gare Shi.(26)Kuma shine ke fara yin halitta ,sa’annan ya sake ta kuma sakewar tafi sauki a gare shiAl-rum: 20-27Namarudu ya Musanta samuwar Ubangijinsa sai Annabi Ibrahin ya ce da shi kamar yadda Allah ya bada labarinsa:"Ibrahin ya ce to lallai Allah yana futo da rana daga gabas to kai ka zo da ita daga yamma sai aka rinjayi wanda ya kafirta kuma Allah baya shiryar da Mutane Al-zalumai"Al-Baqara: 258Kuma haka ne Annabi Ibrahim -Amincin Allah a gare shi ya kafa Dalili ga Mutanensa cewa Allah shi ne wanda ya shiryar da shi kuma ya ciyar da shi kuma ya shayar da shi kuma idan yayi rashin lafiya yake warkar da shi kuma shi ne wanda yake kashe shi kuma ya raya shi sai ya ce: kamar yadda Allah ya bada labari game da shi"Wanda Ya halitta ni, sa'an nan Yanã shiryar da ni."(78)"Kuma Wanda Yake Shĩ ne Yake ciyar da ni, kuma Yanã shãyar da ni."(79)"Kuma idan na yi jiyya, to, Shĩ ne Yake warkar da ni."(80)"Kuma wanda Yake matar da ni, sa'an nan Ya rãyar da ni."(81)Al-Shu'ara'a: 78-81Kuma Allah Maxaukakin Sarki ya bada labarin Annabi Musa cewa shi yayi jayayya da Fir'auna yana mai cewa: Ubangijinsa shi ne:"Shi ne wanda ya bawa kowane abu halittarsa sannan kuma ya shiryar"Xaha: 50Kuma Allah ya hore baki xayan abunda suka Sammai da Qasa ga Mutum kuma ya kewa shi da Ni'amomi; don ya bautawa Allah kuma kada ya kafirce masa, Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Ashe, ba ku gani ba, cẽwa Allah Yã hõre muku abin da ke a cikin sammai da abin da ke a cikin ƙasã, kuma Ya zuba ni'imõminsa a kanku, bayyanannu da ɓõyayyu? Kuma akwai daga mutãne wanda ke yin jidãli ga al'amarin Allah, bã da wani ilmi ba, kuma bã da wata shiriya ba, kumã ba da wani littãfi mai haskakãwa ba.Luqman: 20Kuma Kamar yadda Allah ya sauwaqe duk abunda ke sammai da Qasa to haqiqa shi ya halicce su kuma shi ya tanadar musuda duk abunda suke buqata naji da kuma gani da Zuciya don su koyi Ilimin da zai musu anfani kuma ya nuna musu Ubangijinsu da Mahaliccinsu Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma Allah ne Ya fitar da ku daga cikunan iyãyenku, ba da kunã sanin kõme ba, kuma Ya sanya muku ji da gannai da zukãta, tsammãninku zã ku gõde.Al-nahl: 78Saboda Allah SWT haqiqa ya halicci baki xayan waxan nan Duniyoyi kuma ya halicci Xan Adam kuma ya tanadar masa baki xayan abunda yake buqata na gavvai sannan kuma ya qare shi da duk abunda zai taimaka masa kan tsayuwa da bautar Allah da raya Qasa sannan ya hore masa dukkan abunda ya sammai da QasaKuma Allah ya kafa dalili ga Halittarsa da waxan nan halittu masu Girma, kan Allantakarsa wacce take ta wajibi daga Allantakarsa Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Ka ce: "Wãne ne Yake azurtã ku daga sama da ƙasa? Shin kõ kuma Wãne ne Yake mallakar jĩ da ganĩ, kuma Wãne ne Yake fitar da mai rai daga mamaci, kuma Ya fitar da mamaci daga mai rai, Kuma Wãne ne Yake shirya al'amari?" To, zã su ce: "Allah ne." To, ka ce: "Shin fa, bã zã ku yi taƙawa ba?"Yunus: 31Kuma Alla Maxaukaki ya ce:Ka ce: "Shin, kun gani, abin da kuke kira, wanda yake baicin Allah? Ku nũna mini, menene suka halitta daga ƙasa? Kõ kuwa sunã da tãrayya a cikin sammai? Ku zo mini da wani littãfi na gabãnin wannan (Alƙur'ãni) kõ wata alãma daga wani ilmi, idan kun kasance mãsu gaskiya."Al-ahqaf: 4Allah Madaukakin Sarki ya ce:"Ya halicci sammai ba tare da turaku ba da kuke iya ganinsu kuma ya jefa Duwatsu a bayan Qasa saboda kada ta raurawa da ku kuma ya yaxa kowace irin Dabba a cikinta kuma ya saukar da ruwa daga Sama sai Muka futar a cikinta kowane abu Mace da Namiji Masu daraja, kuma wannan ita ce halittar Allah to kununa mun abunda waxan da suke koma bayansa suka halitta ba haka bane Al-zalumai dai suna Vata bayyananne"Luqman: 10-11Kuma Allah Maxaukaki ya ce:Shin, an halitta su ne bã daga kõme ba, kõ kuwa sũ ne mãsu yin halitta?(35)Shin, sun halitta sammai da ƙasa ne? Ã'a ba su dai yi ĩmãnin yaƙĩni ba.(36).Shin, taskõkin Ubangijinka, sunã a wurinsu ne? Kõ kuwa sũ ne mãsu rinjãya? (37)Al-Xur: 35-37Shiek Al-Si'adi ya ce:(Kuma wannan kafa Dalilin akan su da Umarni da ba zai yi musu ba sai miqa wuya ga gaskiya ko kuma futa daga abunda zai tabbatar da Hankali da Addini)Tafsir Ibn Al-Si'adi:816 7: Allah shi ne Mahalicci ga baki xayan halitta abunda muke iya gani da waxan da bama iya gani, kuma duk wani abu da ba shi ba to shi abun Halitta ne da cikin halittunsa, kuma shi ya halicci Sammai da Qasa cikin kwana Shidda7: Allah shi ne Mahalicci ga baki xayan halitta abunda muke iya gani da waxan da bama iya gani, kuma duk wani abu da ba shi ba to shi abun Halitta ne da cikin halittunsa, kuma shi ya halicci Sammai da Qasa cikin kwana ShiddaKa ce: "Wãne ne Ubangijin sammai da ƙasa?" Ka ce: "Allah". Ka ce: "Ashe fa, kun riƙi waɗansu masõya baicin Shi, waɗanda ba su mallaka wa kansu wani amfãni ba kuma haka bã su tũre wata cũta?" Ka ce: "Shin makãho da mai gani sunã daidaita? Kõ shin duhu da haske sunã daidaita? ko sun sanya ga Allah waɗansu abõkan tãrayya waɗanda suka yi halitta kamar halittarSa sa'an nan halittar ta yi kama da jũna a gare su?" Ka ce: "Allah ne Mai halitta kõme kuma Shĩ ne Maɗaukaki, Marinjãyi."Al-ra'ad: 16 Kuma Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma yana halittar abunda baku sani baAl-nahl: 8Kuma ya halicci Sammai da Qasa cikin kwanaki shida Allah Maxaukaki ya ce:Shĩ ne wanda Ya halitta sammai da ƙasa a cikin wasu kwãnuka shida, sa'an nan Ya daidaitu a kan Al'arshi, Yanã sanin abin da ke shiga cikin ƙasa da abin da ke fita daga gare ta, da abin da ke sauka daga sama da abin da ke hawa cikinta, kuma Shĩ yanã tareda ku duk inda kuka kasance. Kuma Allah Mai gani ne ga abin da kuke aikatãwa.Al-hadid: 4Allah Madaukakin Sarki ya ce:Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun halitta sammai da ƙasã da abin da ke a tsakãninsu, a cikin kwãnaki shida, alhãli wata'yar wahala ba ta shãfe Mu ba.Q: 38 8-Kuma Allah Maxaukakin Sarki bashi da abikin tarayya a cikin Mulkinsa da halittunsa ko BayinsaKuma Allah Maxaukakin Sarki shi ne Mamallaki wanda bashi da Abokin tarayya a cikin halittarsa ko Mulkinsa ko gudanarwarsaKa ce: "Shin, kun gani, abin da kuke kira, wanda yake baicin Allah? Ku nũna mini, menene suka halitta daga ƙasa? Kõ kuwa sunã da tãrayya a cikin sammai? Ku zo mini da wani littãfi na gabãnin wannan (Alƙur'ãni) kõ wata alãma daga wani ilmi, idan kun kasance mãsu gaskiya."Al-ahqaf: 4Imam Ahmad -Allah ya yarda da shi ya ce:Ai ka ce:da waxan nann da suke shirka da Allah wasu Gumaka da kishiyoyi waxanda ba su Mallaki wani anfani ko cutarwa a gare su ba ko Mutuwa ko rayuwa ko kuma tashi daga Kabari to ka ce musu kana mai bayyana musu gajiyawarGumakan na su kuma cewa su basu cancanci da a bauta musu ba (ka nunamun abunda suka halitta a bayan Qasa ko kuma suna da abokan tarayya a cikin sammai) ko sun halicci wasu daga cikin burujan Sama da Qasa? ko kuma sun halicci Qoramai? ko sun samar da Dabbobi? ko sun tsirar da Bishiyoyi? ko kuma suna da masu taimaka musu a tare da su akan wani abu na halitta da cikin hakan? babu wani abu daga cikin wancan da iqirarin su akan su, ga kuma na wasun su to wannan shi ne dalilin Hankali Mai yankan Hanzari kan cewa kowane abu koma bayan Allah bautarsa Batacciya ce.Ka ce: "Shin, kun gani, abin da kuke kira, wanda yake baicin Allah? Ku nũna mini, menene suka halitta daga ƙasa? Kõ kuwa sunã da tãrayya a cikin sammai? Ku zo mini da wani littãfi na gabãnin wannan (Alƙur'ãni) kõ wata alãma daga wani ilmi, idan kun kasance mãsu gaskiya."Tafsir Ibn Al-Si'adi:779Kuma Allah Maxaukakin Sarki shi mamallakin Mulki ba shi da abokin tarayya a cikin mulkinsa Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Ka ce: "Yã Allah Mamallakin mulki, Kanã bayar da mulki ga wanda Kake so, Kanã zãre mulki daga wanda Kake so, kuma Kanã buwãyar da wanda Kake so, kuma Kanã ƙasƙantar da wanda Kake so, ga hannunKa alhẽri yake. Lalle ne Kai, a kan kõwane abu, Mai ĩkon yi ne."Aal Imran: 26Kuma Allah Maxaukakin Sarki ya bayyana cewa cikakken Mulki nasa ne a Ranar Al-qiyamaRãnar da suke bayyanannu, bãbu wani abu daga gare su wanda yake iya bõyuwa ga Allah. "Mulki ga wa ya ke a yau?" Yana ga Allah, Makaɗaici, Mai tĩlastãwa.Ghafir: 16Kuma Allah Maxaukakin Sarki bashi da abikin tarayya a cikin Mulkinsa da halittunsa ko Bayinsa Allah Maxaukakin sarki ya ce:Kuma ka ce: "Gõdiyã ta tabbata ga Allah wanda bai riƙi ɗã ba kuma abõkin tãrayya bai kasance a gare Shi ba a cikin mulkinSa, kuma wani masõyi sabõda wulãkancin bai kasance a gare Shi ba." Kuma ka girmama Shi, girmamãwa.Al-Isra'a: 111Allah Madaukakin Sarki ya ce:wanda Yake da mulkin sammai da ƙasa kuma bai riƙi abin haihuwa ba, kuma abõkin tãrayya bai kasance a gare Shi ba a cikin mulkinSa kuma Ya halitta dukan kowane abu, sa'an nan Ya ƙaddara shi ƙaddarãwa.(Al-furqan: 2)To shi ne Mai Mulki kuma duk abunda yake ba shi abun mallaka ne a gare shi SWT kuma shi ne Mai halitta kuma duk abnda yake ba shi ba to shi halitta ne a gare shi, kuma shi ne mai gudanar da Al-amari kuma duk wanda ya kasance wannan ne Sha'aninsa to ya wajaba a bauta masa kuma bautar waninsa tawaya ce a cikin Hankali da kuma Shirka Duniya da Lahira Allah Maxaukaki ya ce:Kuma suka ce: "Ku kasance Yahũdãwa ko Nasãra, kwã shiryu."Ka ce: "A'a aƙidar Ibrãhĩm dai, maikarkata, zuwa ga gaskiya, kuma bai kasance cikin mãsu shirki ba."Al-Baqara: 135Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma wãne ne ya fi kyau ga addini daga wanda ya sallama fuskarsa ga Allah, alhãli kuwa yanã mai kyautatawa kuma ya bi aƙidar Ibrãhĩm, Yanã mai karkata zuwa ga gaskiya? Allah Yã riƙi Ibrãhĩm badãɗayi.Al-Nisa'a: 125Kuma Allah Maxaukakin sarki ya bayyana cewa duk wanda yabi wanin Tafarkin Annabi Ibrahin ba daxin Allah -Amincin Allah a gare shi- to haqiqa ya wawaitar da kansa, Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma wãne ne yake gudu daga aƙĩdar Ibrãhĩm, fãce wanda ya jãhilta ga ransa? Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun zãɓe shi, a cikin dũniya, kuma lalle ne shi, a cikin Lãhira, haƙĩƙa, yana daga sãlihai.Al-Baqara: 130 9. Allah Maxaukakin Sarki bai Haifa ba kuma ba'a haifeshi ba kuma bashi wani kini ko mai kamanceceniya da shi9. Allah Maxaukakin Sarki bai Haifa ba kuma ba'a haifeshi ba kuma bashi wani kini ko mai kamanceceniya da shiKa ce: "Shi ne Allah Makaɗaĩci."(1)Alla shi ne abun nufi da Buqata (2)"Bai haifa ba, kuma ba a haife Shi ba."(3)"Kuma babu ɗaya da ya kasance kini a gare Shi."(4)Al-Ikhlas: 1-4Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Shi ne Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu. sai ka bauta Masa, kuma ka yi haƙuri ga bautarsa. Shin kã san wani takwara a gare shi?Maryam: 65Allah Maxaukakin Sarki ya ce:(Shĩ ne) Mai ƙãga halittar sammai da ƙasa, Ya sanya muku ma'aura daga jinsinku, kuma (Ya sanya) daga dabbõbi maza da mãtã, Yanã halitta ku a cikinsu, wani abu bai zama kamar tamkarSa ba, kuma Shĩ ne Mai ji, Mai gani.Al-shura:11 10. Allah Maxaukakin Sarki baya sauka a cikin wani abu, ko kuma ya saje da jikin wani abu daga cikin halittunsaKuma Shi Allah SWT ba ya sauka cikin wani jiki kuma baya kamanceceniya da wani daga cikin halittarsa kuma baya haxewa da komai, wancan saboda Allah shi ne Mahalicci kuma duk abunda yake ba shi abun halitta ne kuma shi ne wanzazze kuma duk wanda yake koma bayansa makomarsa shi ne qarewa kuma kowane abu Mulkinsa ne kuma shi ne Mamallakinsa saboda haka babu wani abu da Allah yake sauka a cikinsa daga cikin halittarsa kuma babu wani daga cikin halittarsa da yake sauka cikin zatinsa Maxauakaki, Kuma Allah SWT shi ne mafi girman komai kuma mafi girma daga komai Allah Maxaukaki yana cewa yana mai musantawa waxanda suka raya cewa Allah ya sauka cikin Annabi IsaLalle haƙĩƙa waɗanda suka ce: "Lalle Allah Shĩ ne Masĩhu ɗan Maryama," sun kãfirta. Ka ce: "To, wane ne ke iya mallakar wani abu daga Allah, idan Yã nufi Ya halakar da Masĩhu ɗanMaryama da uwarsa da wanda yake a cikin ƙasa gabã ɗaya?" Kuma Allah ne da mallakar sammai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu, Yanã halitta abin da Yake so. Kuma Allah a kan dukkan kõme, Mai ĩkon yi ne.Al-Ma'ida:17Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma Allah ɗai yake da gabas da yamma sabõda haka, inda duk aka jũyar da ku, to, a can fuskar Allah take. Lalle ne, Allah Mawadãci ne, Mai ilmi.(115)Kuma suka ce: "Allah Yã riƙi ɗã." Tsarki yã tabbata a gare Shi! A'a, Shi ne da abin da yake a cikin sammai da ƙasa, dukansu, a gare Shi, mãsu ƙanƙan da kai ne.(116)Mai kyautata halittar sammai da ƙasa, kuma idan Ya hukunta wani al'amari, sai kawai Ya ce masa: "Kasance." Sai ya yi ta kasancewa.(117)Al-baqara:115-117Allah Madaukakin Sarki ya ce:"Kuma suka ce Allah ya riqi xa" (88)Lalle ne haƙĩƙa kun zo da wani abu mai girman mũni.(89)Sammai sunã kusa su tsattsage sabõda shi, kuma ƙasa ke kẽce kuma duwãtsu su faɗi sunã karyayyu.(90)Saboda sun sanyawa Allah Xa (91)Alhãli bã ya kamata ga Mai rahama ya riƙi wani ɗã.(92)Dukkan wanda yake a cikin sammai da ƙasa bai zama ba fãce mai jẽ wa Mai rahama ne yanã bãwã.(93)Lalle ne haƙĩƙa Yã lissafe su, kuma ya ƙidãye su, ƙidãya.(94)Kuma dukan kõwanensu mai jẽ Masa ne a Rãnar ¡iyãma yanã shi kaɗai.(95)Maryam: 88-95kuma Allah Madaukaki ya ceAllah, bãbu wani Ubangiji fãce Shi, Rãyayye, Mai tsayuwa da kõme, gyangyaɗi bã ya kãma Shi, kuma barci bã ya kãma Shi, Shi ne da abin da yake a cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasa. Wane ne wanda yake yin cẽto a wurinSa, fãce da izninSa? Yana sanin abin da yake a gaba gare su da abin da yake a bãyansu. Kuma bã su kẽwayẽwa da kõme daga ilminSa, fãce da abin da Ya so. KursiyyunSa ya yalwaci sammai da ƙasa. Kuma tsare su bã ya nauyayarSa. Kuma Shi ne Maɗaukaki, Mai girma.[Al-Bakara: 255].To duk wanda wannan shi ne Sha'aninsa kuma wannan shi Sha'anin halittarsa to ta yaya zai sauka cikin wani daga cikin su? ko ya xauke shi a Matsayin Xa? ko ya sanya shi Allah tare da shi? 11-Allah Maxaukakin Sarki Mai rangwame ne muka mai jin Qai ga bayinsa shi yasa ya aiko Manzanni kuma ya saukar da litattafaiKuma Allah SWT shi ne rangwame da jin qai ga bayansa daga cikin rahamarsa ga bayinsa cewa ya aiko Mana manzanni kuma ya saukar musu da litattafai; don ya futar da su daga duhhan Kafirci da shirka zuwa Hasken Tauhidi da shiriya Allah Maxaukaki ya ceLShĩ ne wanda ke sassaukar da ãyõyi bayyanannu ga BãwanSa, dõmin Ya fitar da ku daga duffai zuwa ga haske, kuma lalle Allah haƙĩƙa Mai tausayi ne gare ku, Mai jin ƙai.Al-hadid: 9Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma ba Mu aike ka ba fãce dõmin wata rahama ga talikai.Al-anbiya: 107Kuma Allah yayi Umarni ga Manzonsa da ya bada labari ga bayi cewa shi Mai gafara ne kuma mai jin qai Allah Maxaukaki ya ce:Ka bai wa bãyiNa lãbari cẽwa lalle ne Ni, Mai gãfarane, Mai jin ƙai.Al-hijr: 49Kuma daga cikin jin qansa da rahamarsa shi ne wanda yake yaye cuta kuma yake saukar Al-khairi ga bayinsa Allah Maxaukaki ya ce:Kuma idan Allah Ya shãfe ka da wata cũta, to, bãbu mai yãyẽ ta fãce shi, kuma idan Yanã nufin ka da wani alhẽri, to, bãbumai mayar da falalarSa. Yanã sãmun wanda Yake so daga cikin bãyinSa da shi. Kuma Shĩ ne Mai gãfara, Mai jin ƙai.Yunus: 107 12. Allah shi ne Ubangiji Mai jin qai shi kaxai wanda shi ne zai yi Hisabi ga Halittu a ranar Al-qiyama lokacin da zai tashe su baki xayansu daga Qaburburansu, saboda ya sakawa kowanne Mutum da aikin da yayi na Al-kairi ko sharri, saboda dik wanda yayi aiki nagari kuma yana mai Imani to yana da Ni'ama Matabbaciya, kuma duk wanda ya Kafirta kuma yayi mummunan aiki to yana da Azaba Mai girma a Lahira.Allah shi ne Ubangiji Mai jin qai shi kaxai wanda shi ne zai yiwa halittu Hisabi a ranar Al-qiyama lokacin da ya tashe su baki xayansu daga Qaburburansu, kuma ya sakawa kowane Mutum da abunda ya aikata na Al-kairi ko Sharri saboda duk wanda ya aikata Ayyuka nagari kuma yana Mumini to yana Ni'ama madawwamiya kuma duk wanda ya kafurta kuma yayi aiki Mummuna to yana Azaba Mai girma a Ranar Al-qiyama saboda yana cikar Adalcin Allah SWT da Hikimarsa da Rahamarsa ga Halittarsa cewa ya sanya wannan duniya gidan aiki kuma ya sanya Gida na biyu shi ne gidan sakamako da Hisabi da lada; har wanda ya kyautata ya samu sakamakon kyautatawa kuma wanda ya munana da Azzalumi da Mai Ta'addanci Uqubar Varnarsa da kuma Zaluncin sa; kuma saboda cewa wannan Al-amari sau da yawa wasu rayukan suna nisanta hakan saboda Allah ya kafa Dalilai Masu yawa da suke nuna cewa Lallai tashin Al-qiyama gaskiya ne babu kokwanto a cikinsa Allah Maxaukaki ya ce:Kuma akwai daga ãyõyinSa cẽwa lalle kai kanã ganin ƙasã ƙẽƙasasshiya, to, idan Mun saukar da ruwa a kanta, sai ta girgiza kuma ta kumbura. Lalle wannan da Ya rãya ta, haƙĩƙa, Mai rãyar da matattu ne. Lalle Shĩ Mai ĩkon yi ne a kan kõwane abu.Fussilat: 39Allah Madaukakin Sarki ya ce:Ya ku mutãne! Idan kun kasance a cikin shakka a Tãshin ¡iyãma, to, lalle ne Mũ, Man halittaku daga turɓaya, sa'an nan kuma daga gudãjin jini, sa'an nan kuma daga taõka wadda ake halittãwa da wadda ba a halittawa dõmin, Mu bayyana muku. Kuma Munã tab batar da abin da Muke so a cikin mahaifa zuwa ga wani ajali ambatacce, sa'an nan kuma Munã fitar da ku kunã jãrĩri, sa'an nan kuma dõmin ku kai ga cikar ƙarfinku. Kuma daga cikin ku akwai wanda ke mutuwa, kuma daga gare ku akwai wanda ake mayarwa zuwa ga mafi ƙasƙancin rãyuwa dõmin kada ya san kõme a bãyan ya sani. Kuma kanã ganin ƙasa shiru, sa'an nan idan Muka saukar da ruwa a kanta, sai ta girgiza kuma ta kumbura, kuma ta tsirar da tsirrai daga kõwane nau'i mai ban sha'awa.Al-hajji: 5Sai Allah ya tunatar a cikin waxan nan Ayoyi Dalilab Hankali guda Uku da suke nuni kan tashin Al-qiyama su ne:1. Lallai cewa Mutum Allah ne ya halicce shi tun farko daga Tuvaya kuma wanda ya halicce shi daga Turvaya zai iya Mayar da halittarsa zuwa rayuwa lokacin da yake Turbaya2.lallai cewa wanda ya halicci Mutum daga Maniyyi yana iya dawo da Mutum zuwa rayuwa bayan Mutuwarsa3. lallai cewa wanda ya raya Qasa da Ruwa bayan Mutuwarta yana iya raya Mutane bayan Mutuwarsu kuma a cikin wannan Aya akwai dalili Mai girma kan Mu'ajizar Al-qur'ani saoda ta yaya waxan nan Ayoyin suka haxu -kuma basu da tsawo= Dalilan Hankali guda Uku futattu kan Babbar mas'alaAllah Maxaukakin Sarki ya ce:A rãnar da Muke naɗe sãma kamar neɗẽwar takarda ga abũbuwan rubũtãwa kamar yadda Muka fãra a farKon halitta Muke mãyar da ita. Wa'adi ne a Kanmu. Lalle ne Mun kasance Mãsu aikatãwa.Al-anbiyaaAllah Madaukakin Sarki ya ce:Kuma ya buga Mana wani misãli, kuma ya manta da halittarsa, ya ce: "Wãne ne ke rãyar da ƙasũsuwa alhãli kuwa sunã rududdugaggu?"Ka ce: "Wanda ya ƙãga halittarsu a farkon lõkaci Shĩ ke rãyar da su, kuma Shi, game da kõwace halitta, Mai ilmi ne."Yasin: 78Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.(27)Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.(28)Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.(29)Kuma Qasa bayan haka Muka sanya ta Dunqulalliya (30)Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.(31)Kuma Duwatsu Muka kafe su" (32)Al-Nazi'at: 27-32sai Allah ya yi bayanin cewa halittar Xan Adam bata fi wahalar halittar sama da qasa ba da abunda yake cikin su kuma shi mai iko ne kan ya halicci Sammai da Qasa kuma bai gajiya ba kan ya maida halittar Mutum nan gaba 13. Allah Maxaukakin Sarki ya halicci Xan Adam daga turvaya, kuma ya sanya Zurriyarsa tana yaxuwa bayansa, saboda Mutane a Asalisu daidai suke, kuma babu banbanci a tsakanin jinsi da jinsi ko kuma Mutane kan Mutane sai da tsoron Allah.Allah Maxaukakin Sarki ya halicci Xan Adam daga turvaya, kuma ya sanya Zurriyarsa tana yaxuwa bayansa, saboda Mutane a Asalisu daidai suke, kuma babu banbanci a tsakanin jinsi da jinsi ko kuma Mutane kan Mutane sai da tsoron Allah.Yã kũ mutãne! Lalle ne Mũ, Mun halitta ku daga namiji da mace, kuma Muka sanya ku dangõgi da kabĩlõli, dõmin ku san jũna. Lalle mafĩfĩcinku daraja a wurin Allah, (shĩ ne) wanda yake mafĩfĩcinku a taƙawa. Lalle nẽ Allah Masani ne, Mai ƙididdigẽwa.Al-Hujurat: 13Allah Madaukakin Sarki ya ce:Kuma Allah ne Ya halitta ku daga turɓãya, sa'an nan daga ɗigon maniyyi, sa'an nan Ya sanya ku surkin maza da mãtã. Kuma wata mace bã ta yin ciki, kuma bã ta haihuwa, fãce da saninSa, kuma bã zã a rãyar da wanda ake rãyarwa ba, kuma bã zã a rage tsawon ransa ba fãce yanã a cikin Littãfi. Lalle, wancan mai sauki ne ga Allah.Faxir: 11Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Shĩ ne Wanda Ya halitta ku daga turɓãya, sa'an nan daga maniyyi, sa'an nan daga sãren jini, sa'an nan Ya fitar da ku kunã jãrĩri, sa'an nan dõmin ku isa ga cikar ƙarfinku sa'an nan dõmin ku kasance tsõfaffi, kuma daga cikinku, akwai wanda ake karɓar ransa a gabãnin haka, kuma dõmin ku isa ga ajali ambatacce, kuma dammãninku ko zã ku hankalta.Ghafir: 67Kuma Allah Maxaukaki yai bayani cewa shi ne wanda ya halicci Annabi Isa Umarnin Kasance a da Umarnin kasance kamar yadda ya halicci Adam daga Qasa da umarnin kasance Allah Maxaukaki ya ce:Lalle ne misãlin Ĩsã a wurin Allah kamar misãlin Ãdama ne, (Allah) Yã halitta shi daga turɓãya, sa'an nan kuma Ya ce masa: "Ka kasance: "Sai yana kasancewa.Aal Imran: 59kuma ya gabata na faxa a Sakin layi na (2) cewa Manzon Allah SAW yayi bayanin cewa Mutane daidai suke kuma babu wani fifiko akan wani sai da tsoron Allah 14. Kuma kowane Yaro ana haifarsa ne akan FixraKuma kowane Yaro ana haifarsa ne kan Turba Allah Maxaukaki ya ce:Sabõda haka, ka tsayar da fuskarka ga addini, kanã mai karkata zuwa ga gaskiya, halittar Allah da Ya halitta mutãne a kanta. Bãbu musanyãwa ga halittar Allah, wannan shĩ ne addini madaidaici kuma amma mafi yawan mutãne ba su sani ba.Kuma Hanifiyya ita ce tafarkin Anabi Ibrahim -Amincin Allah a gare shi- Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Sa'an nan kuma Muka yi wahayi zuwa gare ka (cẽwa), "Ka bi aƙĩdar Ibrahĩm, mai karkatã zuwa ga gaskiya, kuma bai kasance daga mãsu shirki ba.'Al-Nahl: 123Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Babu wani Yaro face an haife shi kan Turba ne sai dai Iyayensa suke Mayar da shi Bayahude ko Banasare ko bamajuse Kamar yadda qosashiyar dabba shin zaku.Sannan Abu Huraira -Allah ya yarda da shi- ya ce:Halittar Allah da Ya halitta mutãne a kanta. Bãbu musanyãwa ga halittar Allah, wannan shĩ ne addini madaidaici kuma amma mafi yawan mutãne ba su sani ba.Al-rum: 30Sahih Al-Bukhari: 4775Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Ku saurara Ubangiji na ya Umarceni da in sanar da ku abunda baku sani ba daga cikin abunda ya sanar da ni a wannan rana tawa dukkan dukiyar da na bawa Bawa to halal ce, kuma llali ni na halicci bayi na akan turbar gaskiya baki xayansu sai dai cewa Wasu shaixanu sun zo musu sun kautar da su daga kan Addininsu suka haramta musu abunda na halatta musu suka umarce su da suyi shirka da ni abun da ban saukar musu da wani Dalili ba"Muslim ne ya rawaito shi 2865 15. kuma babu wani Mutum da aka haifeshi da Savo ko ya gaji savon waninsaBabu wani Murum da aka gaifeshi da zunubaiko kuma ya gaji Zunubai daga waninsa kuma Allah Maxaokaki ya bamu labarin cewa Annabi -Amincin Allah a gare shi- yayin da ya sava Umarnin Allah kuma ya ci Bishiya shi da Matarsa cewa shi yayi Nadama kuma ya tuba ya roqi Allah gafara sai Allah ya kimsa Masa wasu kalmomi kyawawa sai ya faxe su sai Allah ya karvi tubansu Allah Maxaukakin ya ce:Kuma muka ce Ya kai Adam Ku zauna kai da Matar ka cikin Aljanna kuma kuci daga cikinta duk yanda kuka so amma kada ku kusanci wannan itaciya to sai ku zamanto cikin Azalumai (35)Sai Shaiɗan ya talãlãɓantar da su ga barinta, sai ya fitar da su daga abin da suka kasance a cikinsa. Kuma muka ce: "ku sauko Sãshenku nã maƙiyi ga sãshe, kuma kuna da a cikin ƙasa matabbata da jin dãɗi zuwa wani lõkaci." (36)To take sai Adam yakarbi kalmomi daga Ubangijinsa to take sai ya karbi tubansa lallai shi ne mai yawan karbar tuba ne kuma mai rahma.(37)Muka ce: "Ku ku sauka daga gare ta gabã ɗaya. To, imma lalle shiriya ta je muku daga gare Ni, to, wanda ya bi shiriya ta to, bãbu tsõro a kansu, kuma bã su yin baƙin ciki."(38)Al-Baqara: 35-38Kuma a lokacin da Allah ya karvi tuban Annabi Adam -Amincin Allah a gare shi- babu sauran wani zunubi a kansa kuma daga nan ma cewa zurriyarsa basu gaji komai ba na Zunubin tuni ya gushe da tuban kuma Asali cewa Mutum baya xaukan laifin waninsa Allah Maxaukaki ya ce:"Kuma ba;a bawa ko wane Rai sai abunda ya aikata, kuma wani rai baya xaukan laifin wani rai, sannan kuma Makomarku zuwa Ubangijinku ce sai ya baku labarin abunda kuke savani a cikinsa"Al-an'am 164Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Wanda ya nẽmi shiryuwa, to, ya nẽmi shiryuwa ne dõminkansa kawai kuma wanda ya ɓace, to, ya ɓace ne a kansa kawai kuma rai mai ɗaukar nauyi bã ya ɗaukar nauyin wani ran, kuma ba Mu zama mãsu yin azãba ba, sai Mun aika wani Manzo.Al-Israa: 15Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma wani rai mai ɗaukar nauyi, bai ɗaukar nauyin wani rai. Kuma idan ran da aka nauyaya wa kãya ya yi kira (ga wani mataimaki) zuwa ga kãyansa, bã zã a dauki kõme ba daga gare shi, kuma kõ dã (wanda ake kiran) yã kasance makusancin zumunta ne. Kanã gargaɗi kawai ne ga waɗanda ke tsoron Ubangijinsu a fake, kuma suka tsayar da salla. Kuma wanda ya tsarkake, to, yanã tsarkaka ne dõmin kansa. Kuma zuwa ga Allah kawai makõma take.Faxir: 18 16. Kuma Manufa na halittar Mutane ita ce bautar Allah shi kaxaiManufar Halittar Mutane ita ce bautar Allah shi kaxai Allah Maxaukaki ya ce:Kuma Ban halitta aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini.Al-thariyat: 56 17. Musilunci ya Karrama Mutum -Maza da Mata- kuma ya xauke masa baki xayan Haqqoqinsa, kuma ya sanya shi abun tambaya akan baki xayan sauran Zaxuxxukansa, da Ayyukansa da kuma Tasarrufinsa, kuma ya xora masa nauyin kowane irin aiki da zai cutar da kansa ko ga wani akansaMusulunci ya Karrama Mutum -Maza da Mata- Saboda Allah Maxauakaki ya halicci Mutum saboda ya zamanto Halifansa a bayan qasa Allah Maxaukaki ya ce:"Ka tuna lokacin da Ubangijinka ya ce da Mala'iku lallai ni zan sanya Halifana a bayan Qasa"Al-Baqara: 30Kuma wannan Karramawar ta haxe baki xayan 'Yan Adam Allah Maxaukaki ya ce:Kuma lalle ne Mun girmama 'yan Adam, kuma Muka ɗauke su a cikin ƙasa da tẽku kuma Muka azurta su daga abũbuwa mãsu dãɗi kuma Muka fĩfĩta su a kan mãsu yawa daga waɗanda Muka halitta, fĩfĩtãwa.Al-Isra'a: 70Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Lalle ne, Mun halitta mutum a cikin mafi kyawon tsayuwa.Al-Teen: 4Kuma Allah ya hana Mutum ya sanya kansa mai bi qasqantacce ga wani abun bauta ko abun bi ko Xa'a koma bayan Allah Allah Maxaukaki ya ce:Kuma akwai daga mutãne wanda yake riƙon kinãye, baicin Allah, suna son su, kamar son Allah, kuma waɗanda suka yi ĩmãni ne mafiya tsananin so ga Allah. Kuma dã waɗanda suka yi zãlunci, suna ganin lõkacin da zã su ga azãba, da cewa lalle ne ƙarfi ga Allah yake duka, da cẽwa lalle neAllah Mai tsananin azãba ne.Al-Baqara: 165-166Kuma Allah Maxaukakin Sarki ya bayyana cewa cikakken Mulki nasa ne a Ranar Al-qiyamaMakangara suka ce wa maraunana, "Ashe, mũ ne muka kange ku daga shiriya a bãyan ya zo muku? Ã, a' kun dai kasance mãsu laifi." (32)Kuma maraunana suka ce wa makangara. "Ã'a, (ku tuna) mãkircin dare da na rãna a lõkacin da kuke umurnin mu da mu kãfirta da Allah, kuma mu sanya Masa abõkan tãrayya." Kuma suka assirtar da nadãma a lõkacin da suka ga azãba. Kuma Muka sanya ƙuƙumma a cikin wuyõyin waɗanda suka kãfirta. Lalle, bã zã a yi musu sakamako ba fãce da abin da suka kasance sunã aikatãwa.(33)Saba'i:32-33Kuma daga cikar Adalcin Allah SWT a ranar Alqiyama cewa zai xora Alhaki ga Masu da jagororin da suka vatar da zunuban waxan da suka vatar da su ba tare da Ilimi ba Allah Maxaukaki ya ce:Dõmin su ɗauki zunubansu cikakku a Rãnar ¡iyãma, kuma daga zunuban waɗanda suke ɓatarwa bã da wani ilmi ba. To, abin da suke ɗauka na zunubi ya mũnana.Al-Nahl: 25kuma Allah ya lamibcewa Mutum baki xayan Haqqoqinsa a Duniya da lahira kuma mafi girman Haqqoqin da Allah da Musulunci ya lamunce kuma ya bayyana su ga Mutane Haqqin Allah kan Mutane da haqqin Mutane kan AllahAn rawaito daga Mu'az -Allah ya yarda da shi- ya ce: na kasance abayan Annabi SAW munyi goyo sai ya ce: "yakai Mu'az ko kasan haqqin Allah akan bayinsa da haqiin Bayi akan Allah sai nace: A'a sai ya ce: "Haqqin Allah akan bayi shi ne su bauta masa kuma kada suyi masa Shirka: sannan yayi tafifa wani lokaci sai ya ce: "ya kai Mu'az" sai nace: Amsawarka bayan Amsawa sai ya ce: "Shin kasan Haqqin bayi akan Allah? wanda idan suka aiki wancan kada yayi musu Azaba"Sahih Al-Bukhari: 6840Kuma Musulunci ya lamunce ga Mutum Addininsa na gaskiya da zuriyarsa da Dukiyarsa da MutuncinsaAnnabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi Ya ce:"Ka ce lallai Allah ya haramta a gare ku jinku da Dukiyoyinku da Mutuncinku kamar haramcin wannan Ranar taku a cikin wannan Watan naku a wannan garin naku"Sahih Al-Bukhari: 6501Kuma haqiqa Manzon Allah SAW ya bayyana wannan Al-qawarin maigirma a cikin Hajjin bankwana wanda ya halarta a tare da sama da Sahabi dubu, kuma ya maimaita wannan Ma'anar kuma ya qarfafata a ranar Layya a hajiin bankwana"Kuma musulunci ya sanya Mutum ya zamanto Mai xauakar nauyin sauran zavuvvukansa da Ayyukansa da kuma tasarrufinsa Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma Kowane Mutum mun lazamta masa wani littafinsa a wuyansa, kuma za'a futo da shi a ranar Alkiyama wani littafi da zai gamu da shi an yada shi, ka karanta Littafinka ya isheka yiwa kanka da kanka HisabiAl-Isra'a: 13A abunda ya aikata na Al-kairi ko Sharri da Allah ya sanya shi yana lizimtarsa kuma baya iya wuce shi zuwa waninsa, saboda ba za'a yi masa hisabi ba da aikin waninsa, kuma ba za'a yiwa waninsa Hisabi ba da aikinsa kuma Allah Maxaukaki ya ce:Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.Al-Inshiqaq: 6kuma Allah Maxaukaki ya ceWanda ya aikata aiki na ƙwarai to sabõda kansa ne, kuma wanda ya mũnanã, to, yanã akansa. Kuma Ubangiwinka, bã Mai zãlunci ga bãyinSa ne ba.Fussilat: 46Kuma Musulunci yana xorawa Mutum Nauyin kowane aiki, ai aikin da ya cutar da kansa ko ya cutar da wasu Allah Maxaukaki ya ce:Kuma wanda ya yi tsirfanci zunubi, to yanã tsirfarsa ne a kan kansa kawai. Kuma Allah Yã kasance Masani, Mai hikima.Al-Nisa'a: 111Allah Maxaukakin Sarki ya ce:"Saboda wancan ne muka wajabtawa Bani Isra'ila cewa duk wanda ya kashe wani rai ba tare da ya kashe wani ba ko yayi varna a bayan qasa to kamar ya kashe Mutane ne baki xaya kuma duk wanda ya raya ta to kamar ya raya Mutane ne baki xayan su"Al-Ma'ida: 32Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Ba'a wani rai da zalunci sai idan ya kasance Xan Annabi Adam na farko yana da Alhaki a cikin sadomin shi ne wanda ya Sunnata kisa"Sahih Muslim: 5150 18. kuma ya Sanya Namiji da Mace daidai da daidai wajen xaukar Alhakim aikinsu da kuma sakamako da bada ladaMusulunci yasanya Mata da Maza daidai wajen aiki da kuma xaukar nauyi da sakamako da Lada Allah Maxaukaki ya ce:Kuma wanda ya yi aiki daga ayyukan ƙwarai, namiji ne ko kuwa mace, alhãli kuwa Yanã mũmini, to, waɗannan sunã shiga Aljanna kuma bã zã a zãlunce su da gwargwadon hancin gurtsun dabĩ no ba.Al-Nisa'a: 124Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Wanda ya aikata aiki na ƙwarai daga namiji kõ kuwa mace, alhãli yanã mũmini, to, haƙĩƙa Munã rãyar da shi, rãyuwa mai dãɗi. Kuma haƙĩƙa Munã sãkã musu lãdarsu da mafi kyãwun abin da suka kasance sunã aikatãwa.Surat Anahl: 97Allah Maxaukakin Sarki ya ce:"Wanda ya aikata mummunan aiki to, ba za a sãka masa ba fãce da misãlinsa, kuma wanda ya aikata aiki na ƙwarai daga namiji kõ mace alhãli kuwa shĩ mũmini ne, to, waɗannan sunã shiga Aljanna, anã ciyar da su a cikinta, bã da lissãfi ba."Ghafir: 40Allah Madaukakin Sarki ya ce:Lalle, Musulmi maza da Musulmi mãtã da muminai maza da muminai mãtã, da mãsu tawãli'u maza da mãsu tawãlĩu mãtãda mãsu gaskiya maza da mãsu gaskiya mãtã, da mãsu haƙuri maza da mãsu haƙuri mãtã, da mãsu tsõron Allah maza da mãsu tsõron Allah mãtã, da mãsu sadaka maza da mãsu sadaka mãtã, da mãsu azumi maza da mãsu azumi mãtã da mãsu tsare farjõjinsu maza da mãsu tsare farjõjinsu mãtã, da mãsu ambaton Allah da yawa maza da mãsu ambatonsa mãtã, Allah Ya yi musu tattalin wata gãfara da wani sakamako mai girma.Al-Ahzab:35 19. Musulunci ya karrama Mace, kuma ya sanya Mata su zamanto abokan tafiyar Maza, kuma ya lazamtawa Mazan ciyar da su idan ya kasance yana da iko, saboda haka ya Wajaba Uba ya ciyar da Xiyarsa, haka Uwa akan Xanta idan ya kasance ya Balaga kuma yana da Iko, haka Mata akan MijintaKuma Musulunci ya xauki Mata a Matsayin 'Yan uwan MazaManzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce"Lallai Mata 'Yan Uwan Maza ne"Tirmizi da Ahmad sun rawaito shi (113)Kuma yana daga cikin Karramawar da Allah yayiwa Mace cewa Musulunci ya wajabta ciyar da Uwa akan Xanta idan yana da IkoManzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce"Hannun da ya bayar shi ne a sama kuma ka fara da Mahaifiyarka da Mahaifinka da 'Yar uwatka sannan mafi kusancin ka"Imam Ahmad ya RawaitoKuma bayanin Matsayin Iyaye zai zo in Allah ya so a sakin layi lamba ta (29)Kuma yana daga cikin Karramawar da Musulunci yayiwa Mace cewa an Wajabtawa Miji ciyar da Matarsa idan ya kasance zai iya Allah Maxaukaki ya ce:Sai mawadãci ya ciyar daga wadãtarsa kuma wanda aka ƙuntata masa arzikinsa, to, sai ya ciyar daga abin da Allah Ya bã shi. Allah bã Ya kallafa wa wani rai fãce abin da Ya bã shi. Allah zai sanya sauƙi a bãyan tsanani.Al-Xalaq: 7Kuma wani Mutum ya tambayi Annabi SAW maye haqqin Mace akan Mijinta ya ce: "Ka ciyar da ita idan kaci kuma ka tufatar da ita idan kayi tufa, kuma kada daketa a fuska kuma kada ka ci nata Mutunci"Imam Ahmad ya Rawaito shiKuma Manzon Allah SAW ya ce: yana mai bayanin wasu haqqoqin Mata kan Mazajensu"Kuma suna da haqiin ciyarwa da tufatarwa akan ku gaawrgawadon iko"Sahih Muslimkuma Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Ya ishi Mutum laifi ya tozarta wanda yake ciyarwa"Imam Ahmad ya Rawaito shiKuma Khaxxabi ya ce:Faxinsa "Wanda yake ciyarwa:yana nufin wanda ya zama dole ya ciyar da shi kuma Ma'ana kamar shi ya ce ga wanda yake sadaka kada kayi sadaka ba da abunda ya ragu ba na Abincin Iyalanka don kana neman lada; sai abun ya juye Alhaki idan ka tozarta su:Kuma yana daga cikin girmamawa da Musulunci yayiwa Mace lallai cewa ya wajabta masa ciyar da Xiya kan Ubanta Allah Maxaukakiin Sarki ya ce:"Iyaye Mata suna shayar da 'Ya'ansu shekara biyu cikakku ga wanda yake son cikar Shayarwa kuma yana kan wanda aka haifa Masa ya ciyar da su da kuma tufatar da su gwargwadon iko"Al-Baqara: 233Sai yayi bayani cewa lallai ne yana kan Uba wanda aka haifa masa Yaro ya ciyar da shi da tufatar da shi gwargwadin iko, Allah Maxaukaki ya ce:"To idan suka shayar muku to ku basu ladan su"Al-Xalaq: 6Sai Allah ya Wajabta ladan shayar da yaro kan Mahaifi; sai hakan ya nuna cewa ciyarwar Xa akan Mahaifinsa take kuma yaro ya haxe Mace da Namiji kuma ya zo a cikin Hadisi mai zuwa dalilin da yake nuna Wajabcin ciyar da Mata da 'Ya'yamta a kan Uba.Saboda an rawaito daga Nana Aisha -Allah ya yarda da ita- cewa Hindu ta ce da manzon Allah SAW lallai Abu Sufyan Mutum ne mai Qauro saboda haka ina da buqatar in riqa xaukar wani abu daga Dukiyarsa sai ya ce:"Ki dauki abunda zai isheki ke da Xanki daidai gwargwado"Bukhari ne ya rawaito shiKuma Annabi yayi bayanin falalar ciyar da 'ya'ya Mata da 'yan Uwa Mata sai Manzon Allah SAW ya ce:"Duk Wanda ya raini 'Yan Mata biyu ko Uku ko 'Yan Mata biyu ko Uku har sukai Aure ko ya Mutu ya barsu to ni da shi zamu shiga Al-janna kafaxa da kafaxa, sai yai nuni da yatsunsa na nuni da na tsakiya"Al-silsila Al-Sahiha: 296 20. kuma Mutuwa ba Karewa bace ta har Abada, a'a ita wata tafiya daga Gidan aiki zuwa gidan Sakamako, kuma Mutuwa yana samun Jiki da Ruhi, Mutuwar Ruhi ita ce rabuwar Ruhi daga jiki, sannan kuma ya dawo zuwa jinkin bayan tashin Al-qiyama, kuma Ruhi baya tafiya zuwa wani jikin bayan Mutuwa, kuma baya sake tsiruwa a wabi jikin dabanMutuwa ba ita ba ce qarewa ta har abada Allah Maxukaki ya ce:Ka ce: "Mala, ikin mutuwa ne. wanda aka wakkala a gare ku, shĩ ne ke karɓar rãyukanku. Sa'an nan zuwa ga Ubangijinku ake mayar da ku."Mutuwa ba ita ba ce qarewa ta har abada Allah Maxukaki ya ce:Kuma Mutuwa tana samun jiki ne da ruhi kuma mutuwar Ruhi shi ne futarsa daga jiki sannan ya dawo zuwa gare shi bayan Tashin Al-qiyama, Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Allah ne ke karɓar rãyuka a lõkacin mutuwarsu, da waɗannan da ba su mutu ba, a cikin barcinsu. Sa'an nan Ya riƙe wanda Ya hukunta mutuwa a kansa kuma Ya saki gudar, har zuwa ga ajali ambatacce. Lalle a cikin wancan, haƙĩƙa, akwai ãyõyi ga mutãne waɗanda ke yin tunãni.Al-Zumar: 42Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Lallai idan aka karve shi sai Idanu su bi shi"Muslim ne ya rawaito shi 920Kuma bayan Mutuwa Mutum daga gidan Aiki yana tafiya zuwa gidan Sakamako Allah Maxaukaki ya ce:zuwa gare Shi makõmarku take gabã ɗaya, wa'adin Allah gaskiya ne. Haƙĩƙa, Shi ne Yake fara halitta, sa'an nan kuma Ya mayar da ita dõmin Ya sãka wa waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka aikata ayyukan ƙwarai da ãdalci, kuma waɗanda suka kãfirta sunã da abin sha daga ruwan zãfi, da azãba mai raɗaɗi, sabõda abin da suka kasance sunã yi na kãfirci.Yunus: 4Kuma rai baya tafiya zuwa wani jikin bayan Mutuwa kuma baya komawa cikin wani saboda haka Da'awar komawar rai cikin wani hankali ma ba zai xauke shi ba ko ji kuma ba'a samu wani Dalili da yake nuna wannan Aqida ba daga Annabawa -Amincin Allah a gare su- 21, kuma Musulunci yana kira ne zuwa Imani da jigajigan Imani Manya, kuma shi ne Imani da Allah da Mala'ikunsa da Imani da litattafan Allah Kamar Al-taura da linjila da Zabuea -kafin jirkita su- da kuma Al-qurani, da kuma Imani da bai xayan Annabawa da Manzanni -Amincin Allah a gare su- kuma yayi Imani da cika makin su shi Annabu Muhaddu Manzon Allah cikamakin Annabawa da Manzanni da Kuma Imani da Ranar Lahira kuma ya sani cewa Rayuwar Duniya da ita ce Qarshe da kuma da Halittu sun zama tsantsar Wasa kuma Imani da Hukuncin Allah da QaddararaMusulunci yana kira zuwa Imani da Babban tushen Imani wanda baki xayan Annabawa da Manzanni sukai kira akansa -Amincin Allah a gare su- kuma su ne:Na farko: Imani da Allah cewa shi ne Ubangiji kuma Mahalicci kuma Mai Azurtawa kuma mai gudanar da wannan halitta kuma cewa shi kaxai ya ke wanda ya cancanci Ibada kuma cewa bautar waninsa Vatacciya ce kuma kowane abun bauta in ba shi ba to Varna ne kuma Ibada bata cancanci wani sai shi kuma Ibada bata inganta ba sai a gare shi, kuma bayanin wannan Mas'alar ya gabata a sakin layi na (8)Kuma Allah SWT ya faxi waxan nan Manyan gishiqai a cikin Ayoyi masu yawa daban daban a cikin Al-qur'ano Maigirma daga cikin su faxin Allah Maxaukaki:Manzon Allah yã yi ĩmãni da abin da aka saukar zuwa gare shi daga Ubangijinsa, da mũminai. Kõwanensu yã yi ĩmãni da Allah, da mala'ikunSa, da littattafanSa, da manzanninSa. Bã mu rarrabẽwa a tsakãnin daya daga manzanninSa. Kuma (mũminai) suka ce: "Mun ji kuma mun yi dã'a; (Muna nẽman) gãfararKa, yã Ubangijinmu, kuma zuwa a gare Ka makõma take "Al-Baqara: 285Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Bai zama addini ba dõmin kun jũyar da fuskõkinku wajen gabas da yamma, kuma amma addini shi ne ga wanda ya yi ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira da malã'iku da Littattafan sama da Annabãwa, kuma ya bãyar da dũkiya, akan yana son ta, ga mai zumunta da marãyu da matalauta da ɗan hanya da mãsu rõƙo, kuma a cikin fansar wuya, kuma ya tsayar da salla, kuma ya bãyar da zakka, da mãsu cika alkawari idan sun ƙulla alkawarin da mãsu haƙuri a cikin tsanani da cũta da lõkacin yãƙi. Waɗannan su ne suka yi gaskiya. Kuma waɗannan su ne mãsu taƙawa.Al-Baqara: 177Kuma Allah Maxaukaki yai kirai zuwa Imani da waxan nan ginshiqan kuma ya bayyana cewa duk wanda ya kafirta da su to haqiqa ya vata vata Mai nisa Allah Maxaukakin sarki ya ce:Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku yi ĩmãni da Allah da Manzonsa, da Littãfin da Ya sassaukar ga ManzonSa da Littãfin nan wanda Ya saukar daga gabãni. To, wanda ya kãfirta da Allah da malã'ikunSa, da LittattafanSa, da ManzanninSa, da Rãnar Lãhira, to, lalle ne yã ɓace, ɓata mai nĩsa.Al-nisa'a: 136Kuma ya zo a cikin Hadisin Umar Bn Khaxxab -Allah ya yarda da shi- ya ce:"wata rana Muna zaune a wajen manzon Allah SAW wata Rana sai wani Mutum ya vullo mana Mai tsananin farin kaya mai tsananin baqin gashin kai kuma ba'a ganin alamar tafiya tare da shi kuma babu wanda ya san shi daga cikin mu, har ya zauna a gaban Manzon Allah SAW sannan ya jingina guiwoyinsa zuwa guiwon yin Guiwoyinsa sannan yana xora Hannayensa akan cinyoyinsa kuma ya ce: ya Muhammad bani labarin game da Musulunci sai Manzon Allah SAW ya ce: ka tsaida sallah ka bada Zakka kuma kayi Azumin watan ramadana da Hajjatar xakin Allah idan kasamu Iko" ya ce: Kayi gaskiya ya ce: sai muka yi mamaki yana tambayarsa kuma yana gasgatashi ya ce: to ka bani labari game da Imani ya ce: "Ka yi Imani da Allah da Mala'ikunsa da litattafansa da Manzanninsa da Ranar lahira da Imani da Qaddara Alkairinsa da Sharrinsa" ya ce: kayi gaskiya, ya ce: to ka bani labarin kyautatawa ya ce: "ka bautawa Allah kamar kana ganinsa saboda in baka ganinsa shi yana ganinka"Sahih Muslim: 8A cikin wannan Hadisin Mala'ika Jibril -Amincin Allah a gare shi- ya zo wajen manzon Allah SAW kuma ya tambaye shi dangane da Mayakan Musulunci kuma sune: Musulunci da imani da Kyautatawa sai Manzon AllaH SAW ya amsa masa, sannan Manzon Allah SAW ya bawa Sahabbansa labari cewa wannan Mala'ika Jibril ne wanda ya zo musu don ya sanar da su Addininsu saboda wannan musuluncin saqon Allah ne wanda Mala'ika Jibril -Amincin Allah a gare shi ya kawo kuma ya isar da shi ga Mutane Manzo SAW kuma Sahabban sa -Allah ya yarda da su- suka kiyaye shi kuma suka isar da shi ga Mutane bayansa.Na biyu: Imani da mala'iku kuma su wata Duniya ce voyayyiya Allah ya halicce su kuma ya sanya su a wata kama ta Musamman kuma ya xora musu wasu ayyuka Masu girma kuma Mafi Girman Ayyukansu shi ne Isar da Saqonnin Manzannin Allah ga Manzanni da Annabawa -Amincin Allah su tabbata a gare su- kuma mafi girman Mala'iku -Amincin Allah a gare su- Allah Maxaukaki ya ce:Yanã sassaukar da malã'iku da Rũhi daga umurninSaa kan wanda Yake so daga bãyinSa, cẽwa ku yi gargaɗi cẽwa: Lalle ne shĩ, bãbu abin bautãwa fãce Ni, sabõda haka ku bĩ Ni da taƙawa.Al-Nahl: 2Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma lalle shi (Alƙur'ãni), haƙĩƙa, saukarwar Ubangijinhalittu ne.(192)Rũhi amintacce ne ya sauka da shi.(193)A zũciyarka, dõmin ka kasance daga mãsu gargaɗi.(194)Da harshe na Larabci mai bayãni.(195)Kuma lalle shin, haƙĩƙa, yanã a cikin litattafan (Manzannin) farko.(196)Al-Shu'araa: 192-196Na Uku: Imani da litattan Allah kamar Altaura da Linjila da zabura -kafin a canza su- da kuma imani da Al-qur'ani Allah Maxaukaki ya ce:Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku yi ĩmãni da Allah da Manzonsa, da Littãfin da Ya sassaukar ga ManzonSa da Littãfin nan wanda Ya saukar daga gabãni. To, wanda ya kãfirta da Allah da malã'ikunSa, da LittattafanSa, da ManzanninSa, da Rãnar Lãhira, to, lalle ne yã ɓace, ɓata mai nĩsa.Al-nisa'a: 136Allah Madaukakin Sarki ya ce:Yã sassaukar da Littãfi a gare ka da gaskiya, yana mai gaskatãwa ga abin da ke gaba gare shi, kuma Allah Yã saukar da Attaura da Linjĩlã(3)A gabãni, suna shiryar da mutãne, kuma Ya saukar da littattafai mãsu rarrabẽwa. Lalle ne waɗanda suka kãfirta da ãyõyin Allah, suna da azãba mai tsanani. Kuma Allah Mabuwayi ne, Ma'abucin azãbar rãmuwa.(4)Ali-Imran: 3-4Allah Madaukakin Sarki ya ce:Manzon Allah yã yi ĩmãni da abin da aka saukar zuwa gare shi daga Ubangijinsa, da mũminai. Kõwanensu yã yi ĩmãni da Allah, da mala'ikunSa, da littattafanSa, da manzanninSa. Bã mu rarrabẽwa a tsakãnin daya daga manzanninSa. Kuma (mũminai) suka ce: "Mun ji kuma mun yi dã'a; (Muna nẽman) gãfararKa, yã Ubangijinmu, kuma zuwa a gare Ka makõma take "Al-Baqara: 285kuma Allah Madaukaki ya ceKa ce: "Mun yi ĩmãni da Allah kuma da abin da aka saukar mana da abin da aka saukar wa Ibrãhĩma da Isma'ĩla da Is'hãƙa da Yãƙũba da jĩkõki, da abin da aka bai wa Mũsã da ĩsã da annabãwa daga Ubangijinsu, bã mu bambantãwa a tsakãnin kõwa daga gare su. Kuma mũ, zuwa gare Shi mãsu sallamãwa ne."Aal Imran: 84Na Huxu: Imani da bai xayan Annabawa da Manzanni -Amincin Allah a gare su- saboda ya wajaba ayi Imani da baki xayan Annabawa da manzanni -Amincin Allah a gare su- da kuma Qudurcewa cewa su baki xayan su Manzanni ne daga Allah don su isarwa da Al-umman su saqonnin Allah da Addininsa da Shari'arsa Allah Maxaukaki ya ce:Ku ce: "Mun yi ĩmãni da Allah, da abin da aka saukar zuwa gare mu, da abin da aka saukar zuwa ga Ibrãhĩm da Ismã'ĩla da Is'hãka da Ya'aƙũbu da jĩkõki, da abin da aka bai wa Mũsã da Ĩsã, da abin da aka bai wa annabãwa daga Ubangijinsu, bã mu rarrabẽwa a tsakãnin kõwa daga gare su, kuma mu, a gare Shi, mãsu miƙa wuya ne."Al-Baqara: 136Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Manzon Allah yã yi ĩmãni da abin da aka saukar zuwa gare shi daga Ubangijinsa, da mũminai. Kõwanensu yã yi ĩmãni da Allah, da mala'ikunSa, da littattafanSa, da manzanninSa. Bã mu rarrabẽwa a tsakãnin daya daga manzanninSa. Kuma (mũminai) suka ce: "Mun ji kuma mun yi dã'a; (Muna nẽman) gãfararKa, yã Ubangijinmu, kuma zuwa a gare Ka makõma take "Al-Baqara: 285Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Ka ce: "Mun yi ĩmãni da Allah kuma da abin da aka saukar mana da abin da aka saukar wa Ibrãhĩma da Isma'ĩla da Is'hãƙa da Yãƙũba da jĩkõki, da abin da aka bai wa Mũsã da ĩsã da annabãwa daga Ubangijinsu, bã mu bambantãwa a tsakãnin kõwa daga gare su. Kuma mũ, zuwa gare Shi mãsu sallamãwa ne."Aal Imran: 84Kuma yayi Imani da cikamakin su shi ne Annabi Muhammad Manzon Allah cika makin Annabwa da Manzanni -Amincin Allah a gare su- Allah Maxaukaki ya ce:Kuma a lõkacin da Allah Ya riƙi alkawarin Annabãwa: "Lalle ne ban bã ku wani abu ba daga Littãfi da hikima, sa'an nan kuma wani manzo ya je muku, mai gaskatãwa ga abin da yake tãre da ku; lalle ne zã ku gaskata Shi, kuma lalle ne zã ku taimake shi." Ya ce: "Shin, kun tabbatar kuma kun riƙi alkawarĩNa a kan wannan a gare ku?" suka ce: "Mun tabbatar." Ya ce: "To, ku yi shaida, kuma Nĩ a tãre da ku Inã daga mãsu shaida."Aal Imran: 81Saboda Musulunci ya wajabta imani da baki xayan Annabawa da Manzanni baki xaya kuma ya Wajabta Imani da na qarshen su, shi ne Manzon Allah Muhammad SAW Allah Maxaukakin Sarki ya ce:"Kace ya ku ma'abota littafi ku ba komai bane har sai tsaida Al-taura da Linjila da abun da aka saukar gareku daga Ubangijinku"Al-Ma'ida: 68Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Ka ce: "Yã ku Mutãnen Littãfi! Ku tafo zuwa ga kalma mai daidaitãwa a tsakã ninmu da ku; kada mu bauta wa kõwa fã ce Allah. Kuma kada mu haɗa kõme da Shi, kuma kada sãshenmu ya riƙi sãshe Ubangiji, baicin Allah." To, idan sun jũya bã ya sai ku ce: "ku yi shaida cẽwa, lalle ne mu masu sallamã wa ne."Aal Imran: 64Kuma duk wanda ya kafurta da Annabi xaya to haqiqa ya kafuta da baki xayan Annabawa da Manzanni -Amincin Allah a gare su- saboda da haka Allah ya ce yana mai bada labari game da hukuncinsa ga Mutanen annabi Nuhu -Amincin Allah a gare shi-Mutãnen Nũhu sun ƙaryata Manzanni.Al-Shu'araa:105Kuma abu ne sananne cewa Annabi Nuhu -Amincin Allah a gare shi- babu wani Manzo da ya gabace shi kuam duk da hakan yayin da Mutanensa suka qaryata shi wannan qaryatawar ta su ta kasance qaryatawa ne ga baki xayan Annabawa da Manzann; saboda Da'awar su xaya ce kuma manufar su xaya ce.Na Biyar: Imani da Ranar lahira kuma ita cd Ranar Aqiyama kuma a qarshen wannan Duaniyar ce Allah zai Umarci Mala'ika Israfil -Amincin Allah a gare shi- sai yai busa busar Mutuwa kuma sai duk wanda Allah ya so Mutuwa Allah Maxaukaki ya ce:Kuma aka busa a cikin ƙaho, sai waɗanda ke a cikin sammai da ƙasã suka sũma sai wanda Allah Ya so (rashin sumansa) sa'an nan aka hũra a cikinsa, wata hũrãwa, sai gã su tsaitsaye, sunã kallo.Al-zumar: 68kuma baki xayan waxanda suke sammai da waxanda suke Qasa sai wanda Allah ya so to lallai cewa Allah zai naxe Sammai da Qasa kamar yadda Maxaukaki ya ce:A rãnar da Muke naɗe sãma kamar neɗẽwar takarda ga abũbuwan rubũtãwa kamar yadda Muka fãra a farKon halitta Muke mãyar da ita. Wa'adi ne a Kanmu. Lalle ne Mun kasance Mãsu aikatãwa.Al-anbiyaa 104Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma ba su ƙaddara Allah a kan haƙĩƙanin ĩkon yinsa ba: ¡asã duka damƙarSa ce, a Rãnar ¡iyãma, kuma sammai abũbuwan naɗewa ne ga dãmanSa. Tsarki ya tabbata a gare Shi, kuma Ya ɗaukaka daga barin abin da suke shirki da shi.Al-zumar: 67Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Allah Maxaukaki zai naxe sammai da a ranar Al-qiyama sannan ya xaukesu da Hannunsa na Dama sannan ya ce: Ni ne Mai Mulki ina masu jabberanci? kuma sannan sai naxe qasa ma da Hannunsa na Hagu sannan ya ce: Ni ne Mai Mulki ina masu jabberanci?"Muslim ya rawaito shiSannan sai Allah ya Umarci Mala'ika da yai busa ta biyu to yayin nan su zasu tashi suna kallo Allah Maxauki ya ce:Sannan sai ayi Busa acikin Kaho to yayin nan su Alkiyama kawai suke sauraroAl-zumar: 68Saboda idan Allah ya tashi Halitta zai tashe su don Hisabi Allah Maxaukaki ya ce:Rãnar da ƙasã ke tsattsãgẽwa daga gare su, sunã mãsu gaggãwa. Wancan tãrãwar mutãne ne, mai sauƙi a gare Mu.Qaaf: 44Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Rãnar da suke bayyanannu, bãbu wani abu daga gare su wanda yake iya bõyuwa ga Allah. "Mulki ga wa ya ke a yau?" Yana ga Allah, Makaɗaici, Mai tĩlastãwa.Ghafir: 16Kuma a cikin Wannan rana Allah zai yiwa Mutane Hisabi baki xayansu kuma ya xauki fansa ga wanda aka zalunta daga wanda ya zalunce shi kuma ya sakawa kowane Mutum da abunda ya aikata Allah Maxaukaki ya ce:Yau anã sãka wa kõwane rai a game da abin da ya aikata, bãbu zãlunci a yau. Lalle Allah Mai gaggawar hisãbi ne.Ghafir: 17Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Lalle ne, Allah bã Ya zãluncin gwargwadon nauyin zarra, idan ta kasance alhẽri ce, zai riɓanya ta, kuma Ya kãwo daga gunsa ijãra mai girma.Al-nisa'a: 40Kuma Allah Maxaukakin Sarki ya ce: "To duk wanda ya ya aikata Alkairi kwatankwacin qwayar Zarra na Al-khairi zai ganshi" (7)Kuma wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi.(6)Al-zalzalah: 7-8Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma Munã aza ma'aunan ãdalci ga Rãnar ¡iyãma, sabõda haka ba a zãluntar rai da kõme. Kuma kõ dã ya kasance nauyin ƙwãya daga kõmayya ne Mun zo da ita. Kuma Mun isa zama Mãsu hisãbi.Al-anbiya'a: 47Kuma bayan tashin Al-qiyama da Hisabi sakamako zaiKasance, saboda duk wanda ya aikata wani Alkairi to yana da Ni'ama dawwamammiya wacce bata gushewa kuma duk wanda ya aikata Sharri da kafirci to yana da Azaba, Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Mulki a rãnar nan ga Allah yake, Yanã hukunci a tsakãninsu. To, waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã a cikin gidãjen Aljannar ni'ima.(56)Kuma waɗandra suka kãfirta kuma suka ƙaryata, game da ãyõyinMu, to, waɗannan sunã da azãba mai wulãkantarwa.(57)Alhajj: 56-57Kuma mun san cewa Rayuwar Duniya da ita ce qarshen rayuwa; da Rayuwa da Halittu sun zamanto tsantsan Wasa Allah Maxaukakin Sarki ya ce:"Shin, to, kun yi zaton cẽwa Mun halitta ku ne da wãsa kuma lalle ku, zuwa gare Mu, bã zã ku kõmo ba?"Al-Mua'Munun: 115Na Shida: Imani da Hukuncin Allah da Qaddara kuma shi ne cewa ya Wajaba Imani da Allah cewa haqiqa ya san dukkan abunda ya Kasance da kuma wanda zai Kasance, a wannan Halitta kuma cewa Allah ya Wajabta dukkan Wancan kafin ya Halicci Sammai da Qasa Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma a wurinSa mabũdan gaibi suke, babu wanda yake sanin su fãce Shi, kuma Yanã sanin abin da ke a cikin tudu da ruwa, kuma wani ganye ba ya fãɗuwa, fãce Yã san shi, kuma bãbu wata ƙwãya a cikin duffan ƙasã, kuma babu ɗanye, kuma babu ƙẽƙasasshe, fãce yanã a cikin wani Littãfi mai bayyanãwa.Al-An'am: 59Haqiqa Ya kewaye dukkan komai da sani, Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Allah, wanda Ya halitta bakwai ɗin sammai kuma daga ƙasã kwatankwacinsu, umuruinSa yanã ta sauka a tsakaninsu dõmin ku san lalle Allah Mai ĩkon yi ne akan dukan kõme, kuma lalle Allah, haƙĩƙa Ya kẽwaye ga dukan kõme da sani.Al-Xalaq:12Kuma cewa shi babu wani abu da zai faru a wannan Duniya na wani abu face sai da nufin Allah da kuma da Mashi'arsa, kuma shi ya halicce shi kuma ya sauqaqe Sababansa Allah Maxaukakin Sarki ya ce:wanda Yake da mulkin sammai da ƙasa kuma bai riƙi abin haihuwa ba, kuma abõkin tãrayya bai kasance a gare Shi ba a cikin mulkinSa kuma Ya halitta dukan kowane abu, sa'an nan Ya ƙaddara shi ƙaddarãwa.(Al-furqan: 2)Kuma yana Babbar Hikima cikin yin hakan wacce Mututane ba zasu iya saninsu ba.Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Hikima cikakka! Sai dai abũbuwan gargaɗi bã su amfãni.Al-qamar: 5Allah Madaukakin Sarki ya ce:Kuma Shĩ ne Wanda Ya fãra halitta, sa'an nan Ya sãke ta kuma sakẽwarta tã fi sauƙi a gare shi. Kuma Yanã da misãli wanda ya fi ɗaukaka a cikin sammai da ƙasã kuma Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.Al-Rum: 27Kuma Allah ya siffanta kansa da Hikima kuma ya kirawo kansa da Mai Hikima Allah Maxaukakin sarki ya ce:Allah Ya shaida cẽwa: Lalle ne bãbu abin bautãwa fãce Shi kuma malãiku da ma'abũta ilmi sun shaida, yana tsaye da ãdalci, bãbu abin bautãwa face Shi, Mabuwãyi, Mai hikima.Aal Imran: 18Kuma Allah Maxaukakin Sarki ya ce ya na bada labarin Annabi Isa -Amincin Allah a gare shi- cewa ashi yana Magana da Allah Ranar Al-qiyama yana mai cewa:"Idan Ka azabta su, to lalle ne su, bãyinKa ne, kuma idan Ka gãfarta musu, to, lalle ne Kai ne Mabuwayi Mai hikima."Al-Ma'ida: 118Kuma Allah Maxaukakin sarki ya ce Annabi Musa -Amincin Allah a gare shi- yayin da ya kirawo shi yana gefen Dutsen Al-xur"Yã Mũsã lalle ne shi, Nĩ ne Allah, Mabuwãyi, Mai hikima."Al-Naml: 9Kuma Allah ya siffanta Al-qur'ani maigirma da hikima sai yake cewa:A. L̃.R. Littãfi ne an kyautata ãyõyinsa, sa'an nan an bayyanã su daki-daki, daga wurin Mai hikima, Mai ƙididdigewa.Hud: 1Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Wancan yãnã daga abin da Ubangijinka Ya yi wahayi zuwa gare ka na hikima. Kuma kada ka sanya wani abin bautãwa na daban tãre da Allah har a jẽfa ka a cikin Jahannama kanã wanda ake zargi, wanda ake tunkuɗẽwaAl-Isra'a: 39 22. kuma Annabwa Ma'asumai ne -Amincin Allah a gare su- cikin abunda suka isar da shi daga Allah, kuma Ma'asumai ne ga barin dukkanin abunda ya sava da Hankali, ko kuma kyawawan halaye su kyamace shi, kuma Annabawa an xira musu isar da Umarnin Allah ga bayinsa, kuma Annabawa basu da wani abu na abunda ya kevanxi Allantaka; aa suma Mutane kamar sauran Mutane Allah yai Musu wahayi da ManzantakarsaKuma Annabawa Ma'asumai ne -Amincin Allah a gare su- cikin abunda suka isar daga Allah; Saboda Allah ya zavi zavavvun Halittarsa don su isar da Saqonninsa, Allah Maxaukakin ya ce:Allah nã zãɓen Manzanni daga malã'iku kuma daga mutãne. Lalle Allah, Mai ji ne, Mai gani.Al-hajj: 75kuma Allah Maxaukaki ya ceLalle ne Allah Yã zãɓi Ãdama da Nũhu da Gidan Ibrãhĩma da Gidan Imrãna a kan tãlikai.Aal Imran: 33kuma Allah Madaukaki ya ceYa ce: "Ya Mũsã! Lalle ne Nĩ, Nã zãɓe ka bisa ga mutãne da manzanciNa, kuma da maganãTa. Sabõda haka ka riƙi abin da Nã bã ka, kuma ka kasance daga mãsu gõdiya."Al-a'araf: 144Kuma Manzanni -Amincin Allah a gare su- sunsan abunda aka saukar Musu na Wahayin Allah kuma suna ganin Mala'iku da suke saukar musu da Wahayi, Allah Maxaukakin Sarki ya ce:"Shi ɗai ne Masanin fake sabõda haka, bã Ya bayyana gaibinSa ga kowa."(26)"Fãce ga wanda Yã yarda da shi, wato wani manzo sa'an nan lalle ne, zai sanya gãdi a gaba gare shi da bãya gare shi."(27)"Dõmin Ya san lalle, sun iyar da sãƙonnin Ubangijinsu, kuma (Shi Ubangijin) Yã kẽwaye su da sani, kuma Yã lissafe dukan kõme da ƙididdiga." (28)Al-Jinn: 26-28Kuma Allah ya Umarce su da isar da saqonninsa, Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Yã kai Manzo! Ka iyar da abin da aka saukar zuwa gare ka daga Ubangijinka. Kuma idan ba ka aikata ba, to, ba ka iyar da manzancinSa ba ke nan. Kuma Allah Yanã tsare ka daga mutãne. Lalle ne, Allah bã Ya shiryar da mutãne kãfirai.Al-Ma'ida: 67kuma Allah Maxaukaki ya ceManzanni mãsu bãyar da bushãra kuma mãsu gargaɗi dõmin kada wata hujja ta kasance ga mutãne a kan Allah bãyan Manzannin. Kuma Allah yã kasance Mabuwãyi, Mai hikima.Al-nisa'a: 165, Kuma Manzanni Amincin Allah a gare su- suna tsoron Allah Matuqa jin tsoro kuma suna jin tsoro basa qarin a kan saqonninsa kuma basa ragewa. Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu.(44)Dã Mun kãma shi da dãma.(45)sa'an nan, lalle ne, dã Mun kãtse masa lakã.(46)Kuma daga cikinku bãbu wasu mãsu iya kãre (azãbarMu) daga gare shi.(47)Al-haqah: 44-47Imam Dan Qayyim Allah ya yi masa Rahama ya ce:"Allah Maxauakaki ya ce: (kuma da qirqirar Qarya a gare mu) ai: Muhammad SAW kuma da ya kasance kamar yadda suka raya akanmu cewa yayi qari acikin Saqon ko tawaya daga cikisu ko kamar yadda wani abu daga gare shi sai ya danganta shi zuwa gare mu kuma abun da ba haka ba da munyi masa gaggawar Uquba kuma saboda wannan ya ce (da mun kamashi da damarmu) sai aka ce: Ma'anarsa da mun munyi masa Azaba da Damarmu' saboda tafi tsananin Kamu kuma aka ce da munkashi da Damarsakuma Allah Maxaukaki ya ce"Kuma ka yuna lokacin da Allah ya ce da Annabi Isa Xan Maryam ko kaine ka ce da Mutane ku riqe ni Allaoli biyu koma bayan Allah sai ya ce tsaeki ya tabbata a gareka ba zai kasance ni faxi abunda ba gaskiya ba ne a gare ni, in nine na faxa to haqiqa ka sani kuma kasan abunda yake cikin raina kuma ni ban san abunda yake cikin ranka ba, lallai kai ne Masani fake, ban gaya musu ba sai abunda ka Umarce ni da shi cewa su bautawa allah Ubangijina kuma Ubangijinku Kuma na kasance mai shaida a lokacin da nake cikin su to yayin da ka karvi raina kaine mai gadin su kuma kai ne Mai shaida akan komai"Al-Maida: 116-117Kuma yana dagasarwarsu daga Falalar Allah ga Annabawansa da Manzanninsa -Amincin Allah a gare su- cewa Allah zai tabbatar da su wajen isarwarsu da Saqonninsa Allah Maxaukaki ya ce:"ya ce lallai ina shadawa da Allah kuma ku shaida cewa ni na barranta da abunda kuke yin Shirka (54) Koma bayansa saboda haka kuyo mun tanadi baki xayanku sannan kada ku saurara mun (55)"Haƙĩƙa, ni na dõgara ga Allah, Ubangijĩna kuma Ubangijinku. Bãbu wata dabba fãce Shi ne Mai riko ga kwarkwaɗarta. Haƙĩƙa, Ubangijĩna Yanã (kan) tafarki madaidaici."Hud: 54-56Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma lalle ne sun yi kusa haƙĩƙa, su fitinẽ ka daga abin da Muka yi wahayi zuwa gare ka, dõmin ka ƙirƙira waninsa a gare Mu, a lõkacin, haƙĩƙa, dã sun riƙe ka masoyi.(73)Kuma bã dõmin Mun tabbatar da kai ba, lalle ne, haƙĩƙa, dã kã yi kusa ka karkata zuwa gare su ta wani abu kaɗan.(74)A lõkacin, lalle ne, dã Mun ɗanɗana maka ninkin azãbar rãyuwa da ninkin azãbar mutuwa, sa'an nan kuma bã zã ka sãmi mataimaki ba a kanMu.(75)Al-Isa'a: 73-75Kuma waxan nan Ayoyi da waxan da suka gabace su shaida ne kuma Dalili ne kan cewa Al-qur'ani saukakke ne daga Ubangijin Talikai; saboda da ya kasance daga Manzo Muhammad SAW ne da bai tare wannan zancen da aka fuskantasa zuwa gare shiKuma Allah SWT ya kare manzanninsa daga Mutane Allah Maxaukaki ya ce:Yã kai Manzo! Ka iyar da abin da aka saukar zuwa gare ka daga Ubangijinka. Kuma idan ba ka aikata ba, to, ba ka iyar da manzancinSa ba ke nan. Kuma Allah Yanã tsare ka daga mutãne. Lalle ne, Allah bã Ya shiryar da mutãne kãfirai.Al-Ma'ida: 67Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma ka karanta musu lãbãrin Nũhu, a lõkacin da ya ce wa mutãnensa, "Ya mutãnẽna! Idan matsayĩna da tunãtarwata ameda ãyõyin Allah sun kasance sun yi nauyi a kanku, to, ga Allah na dõgara. Sai ku tãra al'amarinku, kũ da abũbuwan shirkinku, sa'annan kuma kada al'amarinku ya kasance rufaffe a kanku, sa'an nan kuma ku kashe ni, kada ku yi mini jinkiri."Yunus: 71Kuma Allah Maxaukaki yana bada Labarin Annabi Musa -Amincin Allah a gare shi-"Suka ce Ubangijinmu lallai mu muna jin tsoro kada ya yi banza da mu ko kuma yayi mana Shishigi, ya ce kada kuji tsoro lallai ni ina tare da ku ina jio kuma ina gani"Xaha: 45-46Sai Allah SWT yayi bayanin kiyayewarsa ga Manzanninsa -Amincin Allah a gare su- daga abokan gabarsu basa tava iya cimmusu da wata cuta kuma Allah SWT ya bada labarin cewa shi yana kiyaye Wahayinsa ba'a iya qari a cikin ko rage wani abu daga ciki Allah Maxaukaki ya ce:Lalle Mũ ne, Muka saukar da Ambato (Alƙur'ãni), kuma lale Mũ, haƙĩƙa, Mãsu kiyayẽwane gare shi.Al-Hijr: 9Kuma Annabawa -Amincin Allah a gare su- Ma'asumai ne daga dukkan abunda ya savawa Hankali ko kyawawan Halaye; Allah Maxaukakin Sarki ya ce: yana mai tsarkake suKuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.Al-qalam: 4Kuma ya ce dai:Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.Al-Takweer: 22Kuma Wancan har su iya bada wannan Saqo mafi kyawun tsayuwa kuma Annabawa -Amincin Allah a gare shi- su ne waxanda aka xorawa da Umarnin Allah ga Bayinsa waxan da ba su da komai daga cikin abubuwan da ya kevan ci Ubangiji ko kuma Allantaka a'a su Mutane ne kamar sauran Mutane Allah yana yi musu wahayi da saqonsa Allah Maxaukaki ya ce:Manzanninsu suka ce musu, "Bã mu zama ba fãce mutãne misã, linku, kuma amma Allah Yanã yin falala a kan wanda Yake so daga bãyinsa, kuma bã ya kasancẽwa a gare mu, mu zo muku da wani dalĩli fãce da iznin Allah. Kuma ga Allah sai mũminai su dõgara.Ibrahim: 11Kuma Allah Maxaukakin sarki ya ce: yana Mai Umartar Manzonsa Muhammad SAW kan ya cewa Mutanensa:Ka ce: "Nĩ, mutum ne kawai kamarku, anã yin wahayi zuwa gare ni cewa: Lalle ne, Abin bautawarku, Abin bautawa Guda ne, sabõda haka wanda ya kasance yanã fãtan haɗuwa da Ubangijinsa, to, sai ya yi aiki na ƙwarai. Kuma kada ya haɗa kõwa ga bauta wa Ubangijinsa."Al-Kahf: 110 23. Kuma Musulunci yana kira zuwa ga bautar Allah shi kaxai da ginshiqan Ibada Manya, sune Sallah wacce ita ce tsayuwa da Ruku'u da Sujada da anbaton Allah da yabonsa da kuma Addu'a, kuma Mutum yana sallatarta sau biyar a wuni, kuma a cikinta babu banbanci tsakanin Mawadaci da talaka da shugaba da kuma Talaka a sahu qwara xaya a cikin Sallah da kuma Zakka wacce taje wani yanki ne kaxan daga cikin Dukiya -daidai da sharaxai da kuma gwargwado wanda Allah ya qaddara,kuma tana wajaba ne a Dukiyar Mawadata kuma a bada ita ga Talakawa da wasunsu, kuma sau xaya ce a Shekara, da kuma Azumi wanda shi ne kamewa ga barin ci da sha da rana a watan Azumi, kuma yana koyawa Mutum Dauriya da haquri, da kuma Hajji wanda shi ne: Nufar Xakin Allah a Makka Mai Alfarma sau xaya a rayuwa ga Mai Iko wanda zai iya, kuma a cikin wannan Hajjin akwai daidaito ga kowa da kowa wajen fuskanta zuwa ga Mahalicci SWT, kuma Banbance banbance da Nuna wani fifiko duka ya kau a cikin sa.Musulunci yana kira ziwa Bautar Allah da Manya manyan Ibadu haka da wasun su na Ibadu kuma waxan Ibadu Masu girma haqiqa Allah ya Wajabta su a kan kowane Annabi da Manzanni -Amincin Allah a gare su- kuma Mafi girman Ibadu sune:Na farko: Sallah Allah ya farlantata akan Musulmai kamar yadda ya farlantata akan sauran Annabawa da Manzanni -Amincin Allah a gare su- kuma Allah ya Umarci Annabinsa Ibrahim -Amincin Allah a gare shi- cewa ya tsarkake shi ga masu Xawafi da masu Sallah da ruku'u da Sujada Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma a lõkacin da Muka sanya dakin Allah ya zama urin zama ga mutãne, da aminci, kuma ku riƙi wurin salla daga Maƙãmu Ibrãhĩm, kuma Muka dau alƙawari daga Ibrãhĩm, da Ismã'ila da cẽwa: "Ku tsarkake dãki Na dõmin mãsu ɗawãfi da mãsu E'itikafi da mãsu rukũ'i, mãsu sujada."Al-Baqara: 125Kuma Allah ya wajabtatata akan Annabi Musa afarkon kiran da yayiwa Annabi Musa -Amincin Allah a gare shi- Allah Maxaukakin Sarki ya ce:"Lalle ne, Nĩ ne Ubangijnka, sai ka ɗẽbe takalmanka Lalle ne kanã a rãfin nan abin tsarkakẽwa, ¦uwa."(12)"Kuma Nĩ Nã zãɓe ka. Sai ka saurãra ga abin da ake yin wahayi."(13)"Lalle, Nĩ Ni ne Allah. Bãbu abin bautawa fãce Ni. Sai ka bauta Mini, kuma ka tsayar da salla dõmin tuna Ni."(14)Xaha: 12-14Kuma Annabi Isa -Amincin Allah a gareshi- ya bada labarin cewa Allah ya umarce shi da Sallah da Zakka kamar yadda Allah Maxaukaki ya faxa:"Kuma Yã sanya ni mai albarka a inda duk na kasance kuma Ya umurce ni da yin salla da zakka matuƙar inã da rai."Maryam: 31Kuma Sallah a Musulunci ita ce tsayuwa da ruku'u da Sujada da Anbaton Allah da yabonsa da kuma Addu'a kuma Mutum zai sallace ta ne sau biyar a Rana Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Ku tsare lõkatai a kan sallõli da salla mafificiya. Kuma ku tsayu kuna mãsu ƙanƙan da kai ga Allah.Al-Baqara: 238Allah Madaukakin Sarki ya ce:Ka tsayar da salla a karkatar rãnã zuwa ga duhun dare da lõkacin fitar alfijir lalle ne karãtun fitar alfijir ya kasance wanda ake halarta.Al-Isra'a: 78kuma Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Amma aruku’u to ku girmama Ubangiji a cikinsa. Ita kuma sujjada, to ku yi kokari matukar kokari wajen addu’a a cikinta, lallai ya dace a amsa muku".Sahih MuslimNa biyu: Zakka Allah ya farlanta ta ga Musulmai kamat yadda ya farlantata ga Annabawa da Manzanni da suka gabata -Amincin Allah a gare su- kuma ita wani gwargwado ne kaxan daga cikin Dukiya -daidai da Sharaxai da kuma wani Ma'auni da Allah ya qaddara shi- kuma wajibi ce a cikin Dukiyar Mawadata da zasu riqa bayarwa ga Talakawa da wasunsu sau xaya a Shekara Allah Maxaukaki ya ce:Ka karɓi sadaka daga dũkiyõyinsu kana tsarkake su, kuma kana tabbatar da kirkinsu da ita. Kuma ka yi musu addu'a. Lallai addu'õ'inKa natsuwã ne a gare su. Kuma Allah ne Mai ji, Masani.Al-Taubah: 103Kuma yayin da Annabi SAW ya aika Mu'az -Allah ya yarda da shi zuwa Yamen ya ce da shi:"Lallai kai zaka je wajen wasu Mutane Ahlulkitab ka kirawo su zuwa shaidawa babu abun bauta da gaskiya sai Allah kuma ni manzon Allah ne, idan suka bika kan hakan ka sanar da su cewa Allah Maxaukaki ya farlanta musu salloli biyar a cikin dare da rana to idan suka bika kan hakan to ka sanar da su cewa Allah ya farlanta musu Sadaka a cikin Dukiyoyinsu wacce za'a larva daga Mawadatansu a bawa Talakawansu, Idan suka bika kan hakan to na haneka ga barin tava mafi tsadar dunkiyoyin su kuma kaji tsoron Addu'ar wanda aka zalunta saboda ita bata da Hijaboi tskaninta da Allah.Tirmizi da Ahmad sun rawaito shi (625)Na uku: Azumi Allah ya wajabta shi kan Musulmai kamar yadda ya farlanta shi ga Annabawa da Manzanni -Amincin Allah a garesu- Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! An wajabta azumi a kanku kamar yadda aka wajabta shi a kan waɗanda suke daga gabãninku, tsammãninku, zã ku yi taƙawa,Al-Baqara: 183Kuma shi ne: Kamewa ga barin ci da Sha ga barin ci da sha a Ranar watan Ramadana kuma Azumi yana renon Haquri da juriya a Zuciya.Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi Ya ce:"Allah Maxaukakin Sarki yana cewa: Azumi nawa ne, kuma nine zanyi sakamako da shi saboda ya bar Sha'awarsa da cinsa da shansa saboda ni kuma Azumi garkuwa ne, kuma mai Azumi yana da farin ciki guda biyu: Farin ciki lokacin da zai buxe baki da farin ciki lokacin da zai gamu da Ubangijinsa"Sahih Al-Bukhari: 7492Na Huxu: Hajji Allah ya farlanta shi ne ga Musulmai kamar yadda yadda Allah ya farlanta shi ga Annabawa da Manzanni da suka gabata -Amincin Allah a gare su- cewa yayi kira a lokacin aikin Hajji Allah Maxaukakin Sarki ya ce:"Kuma ka yi yẽkuwa ga mutãne da wajabcin Hajji su je maka suna mãsu tafiya da ƙafãfu da kuma a kan kõwane maɗankwarin rãƙumi mãsu zuwa daga kõwane rango mai zurfi."Al-Hajj: 27Kuma ya Umarce shi da ya tsarkake Xakin Allah ga Alhazai sai ya ce:Kuma a lõkacin da Muka iyãkance wa Ibrãhim wurin ¦akin (Muka ce masa), "Kada ka haɗa kõme da Ni ga bauta, kuma ka tsarkake ¦ãkiNa dõmin mãsu ɗawãfi da mãsu tsayuwa da mãsu ruku'u da mãsu sujada..( Suratul Hajj 26)Kuma Hajji shi ne fuskantar Xakin Allah a Makkah Maigirma ga Ayyuka sanannu sau xaya a rayuwa ga Mai iko Allah Maxaukakin Sarki ya ce:"Kuma Allah ya wajabta Hajjatar Xakinsa ga wanda ya Samu ikon haka, kuma duk wanda ya Kafirce to lallai Allah Mawadaci ne ga barin Talikai"Aal Imran: 97Kuma a cikin Hajji Alhazai Musulmai sukan atru a waje xaya suna masu tsarkake Ibada ga Allah Mahalicci kuma baki xayan Alhazai suna yin aikin Hajji hanya iri xaya wacce take kore banbancen gari ko Ilimi ko matsayin Rayuwa 24. kuma daga cikin mafi girman abunda Ibada ta kevanta da shi a Musulunci cewa yadda ake yinta da lokutanta da sharaxanta Allah SWT ne ya Shar'anta ta su kuma ya isar da ita ga Manzonsa SAW, kuma babu wani Mutum da ya da yayi shigege a cikin su ta hanyar qari ko ragi har zuwa wannan rana, kuma baki xayan Manyan Ibadu baki xayan Annabwa sunyi kira zuwa gare su -Amincin Allah a gare su-24. kuma daga cikin mafi girman abunda Ibada ta kevanta da shi a Musulunci cewa yadda ake yinta da lokutanta da sharaxanta Allah SWT ne ya Shar'anta ta su kuma ya isar da ita ga Manzonsa SAW, kuma babu wani Mutum da ya da yayi shigege a cikin su ta hanyar qari ko ragi har zuwa wannan rana Allah Maxaukakin sarki ya ce:"Yau ne na cika muku Addininku kuma na cika ni'amata a gare ku kuma na yarje muku cewa Musulunci shi ne Addini"[Al-Maa'ida: 3].Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Sabõda haka, ka yi riƙo ga abin da aka yi wahayi da shi zuwa gaie ka. Lalle ne kai, kanã a kan hanya madaidaiciyl.Al-zukhruf: 43Allah Madaukakin Sarki ya ce game da MushrikaiSa'an nan idan kun ƙãre salla, to ku ambaci Allah tsaye da zaune da a kan sãsanninku. Sa'an nan idan kun natsu, to, ku tsayar da Salla. Lalle ne salla tã kasance a kan mũminai, farilla mai ƙayyadaddun lõkuta.Al-Nisa'a: 103Allah maxaukakin sarki ya ce; dangane dawaxanda za'a bawa ZakkahAbin sani kawai, dũkiyõyin sadaka na faƙĩrai ne da miskinai da mãsu aiki a kansu, da waɗanda ake lallãshin zukãtansu, kuma a cikin fansar wuyõyi, da mabarta, da a cikin hanyar Allah da ɗan hanya (matafiyi). Farilla daga Allah. Kuma Allah ne Masani, Mai hikima.Al-Taubah: 60Allah Ta’ala Ya ce akan Azumi:Watan Ramalãna ne wanda aka saukar da Alƙur'ãni a cikinsa yana shiriya ga mutãne da hujjõji bayyanannu daga shiriya da rarrabẽwa. To, wanda ya halarta daga gare ku a watan, sai ya azumce shi, kuma wanda ya kasance majinyaci ko kuwa a kan tafiya, sai ya biya adadi daga wasu kwanuka na dabam. Allah Yana nufin sauƙi gare ku, kuma ba Ya nufin tsanani gare ku, kuma dõmin ku cika adadin, kuma dõmin ku girmama Allah a kan Yã shiryar da ku, kuma tsammãninku, zã ku gõde.(Al-Bakara, aya ta: 185).Allah Maxaukaki ya ce game daHajjiHajji watanni ne sanannu. To, wanda ya yi niyyar hajji a cikinsu to bãbu jimã'i kuma bãbu fãsiƙanci, kuma bãbu jãyayya a cikin hajji. Kuma abin da kuka aikata daga alhẽri, Allah Ya san shi. Kuma ku yi guzuri. To, mafi alhẽrin guzuri yin taƙawa. Kuma ku bi Ni da taƙawa, ya ma'abuta hankula.Al-Baqara: 197Kuma dukkan waxan nan ibadu Masu girma Dukkanin Annawa sunyi kira zuwa gare su 25, Manzon Musulunci shi ne Muhammad Bn Abdullahi daga cikin Zuriyar Annabi Isma'ila Xan Annabi Ibrahim -Amincin Allah a garesu- an haife shi Makka a shekara ta 571 Miladiyya, kuma yai Hijita zuwa madina, kuma baiyi tarayya sa Mutanensa ba a Al-amuran bautar Gunki, sai dai shi ya kasance yana tarayya da su a Ayyukan kirki, kuma ya kasance kan kyawawan Halaye tun kafin a aiko shi, kuma Mutanensa sun kasance suna kiransa Amintacce, kuma Allah ya aiko shi yayin da ya cika Shekara Arba'in kuma Allah ya Qarfafe shi da da Ayoyi (Mu'ajizozi) Masu girma, kuma girmansu shi ne Al-qur'ani Mai girma, kuma shi ne mafi girman Ayoyin Annabawa, kuma shi ne Ayoyin Annabwa har zuwa yau xin nan, kuma yayin da Allah ya cika wannan Addinin, kuma Manzon Allah SAW ya isar da shi matuqar isarwa sai ya yi wafati she, Kuma Manzon Allah karunsa suna Sittin da Uku, kuma aka binne shi a garin Madina SAW Kuma manzon Allah Muhammad SAW shi cika makin Annabawa da Manzanni Allah ya aiko shi da shiriya da Addini na gaskiya don ya futar da Mutane daga duhun Bautar Gumaka da Kafirci da Jahilci zuwa hasken Kaxaita Allah da Imani, da Kuma Allah yai masa shida cewa shi ne ya aiko shi yana mai kira zuwa gare shi da umarninsaManzon Musulunci shi Muhammad Bn Abdullahi daga Zuriyar Isma'il Bn Ibrahim -Amincin Allah a gare shi- kuma an haife shi a Makkah a Shekara ta 571 Miladiyya, kuma an aiko shi a cikinta kuma yayi hijira zuwa Madina kuma Mutanensa suna kiransa Amintacce, kuma bai tava tarayya da Mutanensa ba cikin Al-amuran bautar gumaka sai dai shi ya kasance yana tarayya yare da su a cikin Ayyukan Alkairi kuma ya kasance akan kyawawan Xabi'u Masu girma kafin a aiko shi kuamya siffanta shi da Manyan kyawan Xabiu sai Allah Maxaukaki ya ce game da shi:Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.Al-qalam: 4Kuma yayin da ya cika shekara Arba'in Allah ya aiko shi kuma ya qarfafeshi da ayoyi (Mu'ajizozi) Masu girma kuma mafi girmansu shi ne Al-qur'ani MaigirmaAnnabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:Babu wani Annabi daga cikin Annabawa face an bashi daga cikin Ayoyi wadan da mutane za su yi Imani da shi Ni kuma abinda aka bani shi ne wahayi Allah yana yi min wahayi ina fatan na fisu mabiya ranar tashin AlqiyamaSahih Al-BukhariKuma Al-qur'ani mai girma shi wahayin Allah zuwa ga manzonsa SAW Allah Maxaukakin Sarki ya ce game da shi:wancan littafi ne wanda babu kokwantoa cikinsa kuma cikinsa akwai shiriya ga Masu jin tsoron AllahAl-baqara: 2Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Shin, bã su kula da Alƙur'ãni, kuma dã yã kasance daga wurin wanin Allah haƙĩƙa, dã sun sãmu, a cikinsa, sãɓã wa jũnamai yawa?Al-Nisa'a: 82Kuma Allah ya qure Al-jannu da Mutane kan su zo kwatankwacinsa Allah Maxaukakin sarki ya ce:Ka ce: "Lalle ne idan mutãne da aljannu sun tãru a kan su zo da misãlin wan nan Alƙur'ãni bã zã su zo da misãlinsa ba, kuma kõ dã sãshinsu yã kasance, mataimaki ga sãshi."Al-israa: 88Kuma ya qure su kan su zo da Surori goma kamarsa Allah Maxaukakin sarki ya ce:Kõ sunã cewa: "Yã ƙirƙira shi ne."Ka ce: "Sai ku zo da sũrõri gõma misãlinsa ƙirƙirarru, kuma ku kirãyi wanda kuke iyãwa, baicin Allah, idan kun kasance mãsu gaskiya."Hud: 13Kuma ya qure su kan su zo da Surori goma kamarsa Allah Maxaukakin sarki ya ce:Idan kun kasance cikin kokkwanton abunda muka saukarwabawanmu to kuzo da Sura kwara daya kwatankwacinta kuma ku kirawo Shaidunku koma bayan Allah indai kunkasan ce masu gaskiyaAl-baqara: 23Kuma Al-qur'ani mai girma shi wahayin Allah zuwa ga manzonsa SAW Allah Maxaukakin Sarki ya ce game da shi:wancan littafi ne wanda babu kokwantoa cikinsa kuma cikinsa akwai shiriya ga Masu jin tsoron AllahAl-baqara: 2Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Shin, bã su kula da Alƙur'ãni, kuma dã yã kasance daga wurin wanin Allah haƙĩƙa, dã sun sãmu, a cikinsa, sãɓã wa jũnamai yawa?Al-Nisa'a: 82Kuma Allah ya qure Al-jannu da Mutane kan su zo kwatankwacinsa Allah Maxaukakin sarki ya ce:Ka ce: "Lalle ne idan mutãne da aljannu sun tãru a kan su zo da misãlin wan nan Alƙur'ãni bã zã su zo da misãlinsa ba, kuma kõ dã sãshinsu yã kasance, mataimaki ga sãshi."Al-israa: 88Kuma ya qure su kan su zo da Surori goma kamarsa Allah Maxaukakin sarki ya ce:Kõ sunã cewa: "Yã ƙirƙira shi ne."Ka ce: "Sai ku zo da sũrõri gõma misãlinsa ƙirƙirarru, kuma ku kirãyi wanda kuke iyãwa, baicin Allah, idan kun kasance mãsu gaskiya."Hud: 13Kuma ya qure su kan su zo da Surori goma kamarsa Allah Maxaukakin sarki ya ce:Idan kun kasance cikin kokkwanton abunda muka saukarwabawanmu to kuzo da Sura kwara daya kwatankwacinta kuma ku kirawo Shaidunku koma bayan Allah indai kunkasan ce masu gaskiyaAl-baqara: 23Kuma Al-qur'ani Mai girma shi Aya qwaya xaya matabbaciya daga cikin Mu'ajizozin Annabawa har zuwa yau kuma yayin da Allah ya cikawa Manzo SAW Addini kuma ya isar da shi Matuqar Isarwa Sai manzon Allah SAW yayi Wafati kuma shekararsa tana Sittin kuma ka Binne shi a birnin Madina SAWKuma Manzon Allah Muhammad SAW shi ne cika makin Annabawa da manzanni Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Muhammadu bai kasance uban kõwa ba daga mazanku, kuma amma shĩ yã kasance Manzon Allah kuma cikon Annabãwa. Kuma Allah Ya kasance Masani ga kõme.Al-ahzab: 40Da hadisin Abi huraira Allah ya yarda dashi daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Lallai ni kwatankwacina da sauran Annabawa da suka gabaceni kamar Mutum ne da ya gina gida sai ya kyautatashi yai masa qawa sai wurin Bulo xaya a wani lungu sai mutane suka riqa kewaye shi suna mamakinsa suna cewa ina ma za'a saka wannan bulo xin ? to ni ne wannan Bulo xin kuma ni ne cika makin Annabawa"Sahih Al-BukhariKuma a cikin linjila Annabi Isa -Amincin Allah a gare shi- yayi bushara da Manzon Allah SAW(Dutsen wanda masu gini suka qi ginawa shi ne ya isa kan zawiyyar baku karanta ba a cikin litattafai: Yasu'a ya ce da su daga Ubangiji wannan yake kuma shi abun Mamaki ne a Idanuwan mu) kuma a cikin Sifirn Al-taura wacce ake samu a yau kuma a cikinta faxin Annabi Musa -Amincin Allah a gare shi: (San samar musu da Annabi a cikin su kamarka kuma na sanya Magana ta a cikin bakinsa sai yayi magana da su da baki xayan abunda nayi masa wasiyya da shi)Kuma Manzon Allah Muhammad SAW Allah ya aiko shi da shiriya da kuma Addinin gaskiya kuma Allah yai masa shaida da cewa shi yana kan gaskiya kuma cewa shi ne ya aiko shi yana mai kira zuwa gare shi da umarninsa Allah Maxaukakin sarki ya ce:Amma Allah Yanã shaida da abin da Ya saukar zuwa gare ka. Yã saukar da shi da saninSa. Kuma malã'iku sunã shaida. Kuma Allah Yã isa Ya zama shaida.Al-Nisa'a: 166Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Shĩ ne wanda Ya aiki ManzonSa da shiriya da addinin gaskiya dõmin Ya rinjãyar da shi a kan addinai dukansu. Kuma Allah Ya isa Ya zama Mai shaida.Al-Fath: 28Allah ya aiko shi da shiriya don ya futar da Mutane daga duhun bautar gumaka da kafirci da Jahilci zuwa Hasken Tauhidi da Imani Allah Maxaukakin sarki ya ce:Dashĩ, Allah Yanã shiryar da wanda ya bi yardarsa zuwa ga hanyõyin aminci, kuma Yanã fitar da su daga duffai zuwa ga haske da izninsa, kuma Yanã shiryar da su zuwa ga hanya madaidaiciya.Al-Ma'ida: 16Allah Maxaukakin Sarki ya ce:A. L̃.R. Littãfi ne mun saukar da shi zuwa gare ka dõmin ka fitar da mutãne daga duhunhuna zuwa ga haske, da iznin Ubangijinsu, zuwa ga tafarkin Mabuwãyi, Abin gõdẽwa.Ibrahim: 1Muhammadu bai kasance uban kõwa ba daga mazanku, kuma amma shĩ yã kasance Manzon Allah kuma cikon Annabãwa. Kuma Allah Ya kasance Masani ga kõme.Al-ahzab: 40Da hadisin Abi huraira Allah ya yarda dashi daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Lallai ni kwatankwacina da sauran Annabawa da suka gabaceni kamar Mutum ne da ya gina gida sai ya kyautatashi yai masa qawa sai wurin Bulo xaya a wani lungu sai mutane suka riqa kewaye shi suna mamakinsa suna cewa ina ma za'a saka wannan bulo xin ? to ni ne wannan Bulo xin kuma ni ne cika makin Annabawa"Sahih Al-BukhariKuma a cikin linjila Annabi Isa -Amincin Allah a gare shi- yayi bushara da Manzon Allah SAW(Dutsen wanda masu gini suka qi ginawa shi ne ya isa kan zawiyyar baku karanta ba a cikin litattafai: Yasu'a ya ce da su daga Ubangiji wannan yake kuma shi abun Mamaki ne a Idanuwan mu) kuma a cikin Sifirn Al-taura wacce ake samu a yau kuma a cikinta faxin Annabi Musa -Amincin Allah a gare shi: (San samar musu da Annabi a cikin su kamarka kuma na sanya Magana ta a cikin bakinsa sai yayi magana da su da baki xayan abunda nayi masa wasiyya da shi)Kuma Manzon Allah Muhammad SAW Allah ya aiko shi da shiriya da kuma Addinin gaskiya kuma Allah yai masa shaida da cewa shi yana kan gaskiya kuma cewa shi ne ya aiko shi yana mai kira zuwa gare shi da umarninsa Allah Maxaukakin sarki ya ce:Amma Allah Yanã shaida da abin da Ya saukar zuwa gare ka. Yã saukar da shi da saninSa. Kuma malã'iku sunã shaida. Kuma Allah Yã isa Ya zama shaida.Al-Nisa'a: 166Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Shĩ ne wanda Ya aiki ManzonSa da shiriya da addinin gaskiya dõmin Ya rinjãyar da shi a kan addinai dukansu. Kuma Allah Ya isa Ya zama Mai shaida.Al-Fath: 28Allah ya aiko shi da shiriya don ya futar da Mutane daga duhun bautar gumaka da kafirci da Jahilci zuwa Hasken Tauhidi da Imani Allah Maxaukakin sarki ya ce:Dashĩ, Allah Yanã shiryar da wanda ya bi yardarsa zuwa ga hanyõyin aminci, kuma Yanã fitar da su daga duffai zuwa ga haske da izninsa, kuma Yanã shiryar da su zuwa ga hanya madaidaiciya.Al-Ma'ida: 16Allah Maxaukakin Sarki ya ce:A. L̃.R. Littãfi ne mun saukar da shi zuwa gare ka dõmin ka fitar da mutãne daga duhunhuna zuwa ga haske, da iznin Ubangijinsu, zuwa ga tafarkin Mabuwãyi, Abin gõdẽwa.Ibrahim: 1 26. Kuma Shari'ar Musulunci wacce Manzon Allah Muhammad SAW ya zo da ita ita ce cika makin Saqonnin Allah da kuma shari'ar Ubangiji; kuma ita ce Shari'ar cikawa, kuma a cikinta akwai gyaruwar Addinin Mutane da Duniyarsu, kuma tana tsarewa a mataki na farko ga Addinin Mutane da Jininsu da Dukiyarsu da Hankulansu da Zuriyarsu, kuma ta shafe kowa ce Shari'a da ta gabace ta na daga Shari'u, kamar yadda ta soke vangaren wasun da suka gabaceta.Shari'ar Musulunci wacce Manzon Allah ya zo da ita uta ce cika makin Saqonnim Allah d a Sharo'un Ubangiji, kuma Allah ya cika wannan saqon Addinin kuma Ni'amar ta cika ga Mutane aiko Manzon Allah SAW Allah Maxaukaki ya ce:"Kuma yaune muka cika muku Addininku kuma muka cika muku ni'amarku kuma muka yarje muku Musulun a Matsayin Addini"[Al-Maa'ida: 3].Kuma Shari'ar Musulunci ita e cikakkiyar Shari'a kuma a cikinta gyaruwar Addinin Mutane da Duniyarsu suke cikinta; saboda ita ce ta tare baki xayan Shari'un da suka gabata kuma mafi cikar su Allah Maxaukakin sarki ya ce:Lalle ne wannan Alƙur'ãni yanã shiryarwa ga (hãlayen) waɗanda suke mafi daidaita kuma yanã bãyar da bushãra ga mũminai waɗanda suke aikata ayyuka na ƙwarai (cẽwa) "Lalle ne sunã da wata ijãra. mai girma."Al-Isra'a:9Kuma ya sanya Shari'ar Musulunci daga Mutane wahalhalun da suke a cikin Al-umman da suka gabata Allah Maxaukakin Sarki ya ce"Waɗanda suke sunã bin Manzo, Annabi, Ummiyyi wanda suke sãmun sa rubũce a wurinsu, a cikin Attaura da Linjĩla yana Umartarsu da kyawawan ayyuka kuma yana hanasu daga Mummuna kuma yana halarta musu daxaxan abubuwa kuma yana haramta aaamusu munana kuma yana sauke musu abunda ya dame su da ququmqi waxanda suke kansu saboda haka waxanda sukai Imani da shi kuma suka qarfafe shi kuma suka taimake shi kuma suka bi hasken da ya saukar tare da shi waxan nan sune masu rabauta"Al-a'araf: 157:Kuma Shari'ar musulunci ta goge dukkan Shari'un da suka gabata Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma Mun saukar da Littãfi zuwa gare ka da gaskiya yanã mai gaskatãwa ga abin da yake a gaba gare shi daga Littãfi (Attaura da Injĩla), kuma mai halartãwa a kansa sai ka yi hukunci a tsakãninsu da abin da Allah Ya saukar kuma kada ka bĩbiyi son zũciyõyiniu daga abin da ya zo maka daga gaskiya Ga kõwanne daga gare ku Mun sanya sharĩa da hanya (ta bin ta) Kuma dã Allah Yã so, dã Yã sanya ku al'umma guda, kuma amma dõmin Ya jarraba ku a cikin abin da Ya bã ku Sai ku yi tsere ga ayyukan alheri Zuwa ga Allah makõmarku take gabã ɗaya Sa'an nan Ya bã ku lãbãri ga abin da kuka kasance kunã sãɓãwa a cikinsa.Al-Ma'ida: 48Saboda Al-qurani ya qunshiShari'ar abunda ya zo yana mai gasgata abunda ya gabace shi na litattafan Allah kuma yana Mai hukunci akan su kuma ya shafe su."Kuma yaune muka cika muku Addininku kuma muka cika muku ni'amarku kuma muka yarje muku Musulun a Matsayin Addini"[Al-Maa'ida: 3].Kuma Shari'ar Musulunci ita e cikakkiyar Shari'a kuma a cikinta gyaruwar Addinin Mutane da Duniyarsu suke cikinta; saboda ita ce ta tare baki xayan Shari'un da suka gabata kuma mafi cikar su Allah Maxaukakin sarki ya ce:Lalle ne wannan Alƙur'ãni yanã shiryarwa ga (hãlayen) waɗanda suke mafi daidaita kuma yanã bãyar da bushãra ga mũminai waɗanda suke aikata ayyuka na ƙwarai (cẽwa) "Lalle ne sunã da wata ijãra. mai girma."Al-Isra'a:9Kuma ya sanya Shari'ar Musulunci daga Mutane wahalhalun da suke a cikin Al-umman da suka gabata Allah Maxaukakin Sarki ya ce"Waɗanda suke sunã bin Manzo, Annabi, Ummiyyi wanda suke sãmun sa rubũce a wurinsu, a cikin Attaura da Linjĩla yana Umartarsu da kyawawan ayyuka kuma yana hanasu daga Mummuna kuma yana halarta musu daxaxan abubuwa kuma yana haramta aaamusu munana kuma yana sauke musu abunda ya dame su da ququmqi waxanda suke kansu saboda haka waxanda sukai Imani da shi kuma suka qarfafe shi kuma suka taimake shi kuma suka bi hasken da ya saukar tare da shi waxan nan sune masu rabauta"Al-a'araf: 157:Kuma Shari'ar musulunci ta goge dukkan Shari'un da suka gabata Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma Mun saukar da Littãfi zuwa gare ka da gaskiya yanã mai gaskatãwa ga abin da yake a gaba gare shi daga Littãfi (Attaura da Injĩla), kuma mai halartãwa a kansa sai ka yi hukunci a tsakãninsu da abin da Allah Ya saukar kuma kada ka bĩbiyi son zũciyõyiniu daga abin da ya zo maka daga gaskiya Ga kõwanne daga gare ku Mun sanya sharĩa da hanya (ta bin ta) Kuma dã Allah Yã so, dã Yã sanya ku al'umma guda, kuma amma dõmin Ya jarraba ku a cikin abin da Ya bã ku Sai ku yi tsere ga ayyukan alheri Zuwa ga Allah makõmarku take gabã ɗaya Sa'an nan Ya bã ku lãbãri ga abin da kuka kasance kunã sãɓãwa a cikinsa.Al-Ma'ida: 48Saboda Al-qurani ya qunshiShari'ar abunda ya zo yana mai gasgata abunda ya gabace shi na litattafan Allah kuma yana Mai hukunci akan su kuma ya shafe su. 27. Kuma Alla SWT baya karvar wani Addini in ba Musulunci ba wanda shi ne wanda Annabi Muhammad SAW ya zo da shi, kuma duk wanda ya riqi wanin Musulunci Addini to ba za'a larva baKuma Alla SWT baya karvar wani Addini in ba Musulunci ba wanda shi ne wanda Annabi Muhammad SAW ya zo da shi, kuma duk wanda ya riqi wanin Musulunci Addini to ba za'a karva baAllah Maxaukakin Sarki ya ceKuma wanda ya nẽmi wanin Musulunci ya zama addini, to, bã zã a karɓa daga gare shi ba. Kuma shi a Lãhira yana daga cikin mãsu hasãra.Aal Imran: 85Allah Madaukakin Sarki ya ce:Lalle ne, addini a wurin Allah, Shi ne Musulunci. Kuma waɗanda aka bai wa Littafi ba su sãɓã ba, fãce a bãyan ilmi ya je musu, bisa zãlunci a tsakãninsu. Kuma wanda ya kãfirta da ãyõyin Allah, to, lalle ne Allah Mai gaugãwar sakamako ne.Aal Imran: 19Kuma wannan Musuluncin shi ne tafarkin Anabi Ibrahim -Amincin Allah a gare shi- Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma wãne ne yake gudu daga aƙĩdar Ibrãhĩm, fãce wanda ya jãhilta ga ransa? Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun zãɓe shi, a cikin dũniya, kuma lalle ne shi, a cikin Lãhira, haƙĩƙa, yana daga sãlihai.Al-Baqara: 130Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma wãne ne ya fi kyau ga addini daga wanda ya sallama fuskarsa ga Allah, alhãli kuwa yanã mai kyautatawa kuma ya bi aƙidar Ibrãhĩm, Yanã mai karkata zuwa ga gaskiya? Allah Yã riƙi Ibrãhĩm badãɗayi.Al-Nisa'a: 125Kuma Allah Maxaukakin sarki yana Umartar Manzonsa Muhammad SAW kan ya cewa:Ka ce: "Lalle nĩ, Ubangijina Yã shiryar da ni zuwa ga tafarki madaidaici, addĩni, ƙĩmantãwa (ga abũbuwa), mai aƙĩdar Ibrãhĩm, mai karkata zuwa ga gaskiya, kuma bai kasance daga mãsu shirki ba."Al-an'am: 161Allah Maxaukakin Sarki ya ceKuma wanda ya nẽmi wanin Musulunci ya zama addini, to, bã zã a karɓa daga gare shi ba. Kuma shi a Lãhira yana daga cikin mãsu hasãra.Aal Imran: 85Allah Madaukakin Sarki ya ce:Lalle ne, addini a wurin Allah, Shi ne Musulunci. Kuma waɗanda aka bai wa Littafi ba su sãɓã ba, fãce a bãyan ilmi ya je musu, bisa zãlunci a tsakãninsu. Kuma wanda ya kãfirta da ãyõyin Allah, to, lalle ne Allah Mai gaugãwar sakamako ne.Aal Imran: 19Kuma wannan Musuluncin shi ne tafarkin Anabi Ibrahim -Amincin Allah a gare shi- Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma wãne ne yake gudu daga aƙĩdar Ibrãhĩm, fãce wanda ya jãhilta ga ransa? Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun zãɓe shi, a cikin dũniya, kuma lalle ne shi, a cikin Lãhira, haƙĩƙa, yana daga sãlihai.Al-Baqara: 130Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma wãne ne ya fi kyau ga addini daga wanda ya sallama fuskarsa ga Allah, alhãli kuwa yanã mai kyautatawa kuma ya bi aƙidar Ibrãhĩm, Yanã mai karkata zuwa ga gaskiya? Allah Yã riƙi Ibrãhĩm badãɗayi.Al-Nisa'a: 125Kuma Allah Maxaukakin sarki yana Umartar Manzonsa Muhammad SAW kan ya cewa:Ka ce: "Lalle nĩ, Ubangijina Yã shiryar da ni zuwa ga tafarki madaidaici, addĩni, ƙĩmantãwa (ga abũbuwa), mai aƙĩdar Ibrãhĩm, mai karkata zuwa ga gaskiya, kuma bai kasance daga mãsu shirki ba."Al-an'am: 161 28. Al-qu'ani maigirma shi ne littafin da Allah yai wahayinsa ga Manzo Muhammad SAW kuma shi ne zancen Ubangijin Talikaia aikowa Manzon Allah SAW kuma shi ne zancen Ubangijin Talikai wanda Allah ya qure Mutum da Al-jann kan su zo da kwatankwacin sa, ko Sura kwatankawcinsa, kuma har yau qurewa bata qare ba, Kuma Al-qurani yana bada Amsar Muhimmai masu yawa da Muliyoyin Mutane suka gaza, Kuma Al-qurani Maigirma abun kiyayewa ne har zuwa yau xin nan da yaren larabci da ya sauka da shi, kuma ba'a rage ko harafi xaya ba, kuma yana nan a buge ana yaxa shi, Kuma littafi ne Maigirma Mai gajiyarwa wanda ya dace da a Karanta shi ko a karanta Fassararsa, Kamar yadda Sunnar manzon Allah SAW da koyarwarsa da Tarihinsa ababan kiyayewa ne kuma ababan rawaito ne daidai da tsanin jerin Masu riwaya da aka yarda da su, kuma an buga ta da Larabci wanda Manzon Allah SAW yayi magana da shi kuma an fassara ta a Yaruka da yawa, kuma Al-qur'ani da Sunnar Manzon Allah su ne Tushen qwara xaya na Hukunce hukuncen Musulunci da Shari'unsa, saboda Musulunci, saboda ba'a xaukar Musulunci daga aiyukan xaixaikun Mutane da suke danganta kansu da Musulunci; kawai ana xauka ne daga Wahayin Allah a Al-qur'ani Maigirma da Sunnar AnnabiAl-qur'ani maigirma shi ne littafin da Allah yai Wahayinsa zuwa ga Manzo Balarabe Muhammad SAW da Yaren Larabci kuma shi ne zancen Ubangijin Talikai, Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma lalle shi (Alƙur'ãni), haƙĩƙa, saukarwar Ubangijinhalittu ne.(192)Rũhi amintacce ne ya sauka da shi.(193)A zũciyarka, dõmin ka kasance daga mãsu gargaɗi.(194)Da harshe na Larabci mai bayãni.(195)Al-Shu'araa: 192-195Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma lalle ne haƙĩƙa, anã haɗa ka da Alƙur'ãni daga gun Mai hikima, Masani.Al-Naml: 6Kuma wannan Al-qur'ani saukakke ne daga Allah kuma mai gasgatawa ne da abunda ya gabace shi na litattafan Allah Allah Maxaukakin sarki ya ce:Kuma wannan Alƙur'ãni bai kasance ga a ƙirƙira shi ba daga wanin Allah, kuma amma shi gaskatawar wannan ne da yake a gabãninsa da bayãnin hukuncin littãffan Allah, Bãbu shakka a cikinsa, daga Ubangijin halittu yake.Yunus: 37Kuma Al-qur'ani maigirma ya fayyace mafi yawan Mas'alolin da Yahudu da Nasara sukai Savani akansu a cikin Addinansu Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Lalle ne wannan Alƙur'ãni yanã gaya wa Banĩ Isrãĩla mafi yawan abin da sũ suke sãɓa wa jũnansu a ciki.Al-Naml: 76Kuma Al-qurani Maigirma ya qunshi Dalilai da hujjoji da zasu iya tsayawa Hujja a kan Mutane baki xaya wajen Sanin haqiqoqi da suke da Alaqa da Allah SWT da Addinsa da sakamakonsa Allah Maxaukakin sarki ya ce:Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun buga wa mutãne a, cikin wannan Alƙur'ãni, daga kõwane misãli, ɗammãninsu su yi tunãni.Al-Zumar: 27kuma Allah Maxaukaki ya ce"Kuma mun saukar maka da Littafin mai bayani ga komai kuma shiriya ne da rahama ga Musulmai"Surat Annahl 89Kuma Al-qurani maigirma yana Amsa tambayoyi Masu yawa da suka kiximar da Miliyoyin Mutane saboda Al-qur'ani maigirma yana bayani yadda Allah ya halicci sammai da da qasa Allah Maxaukaki ya ce:Shin kuma waɗanda suka kãfirta ba, su gani da cẽwa lalle sammai da ƙasa sun kasance ɗinke, sai Muka bũɗe su, kuma Muka sanya dukan kome mai rai daga ruwa? Shin, bã zã su yi ĩmãni ba?Al-anbiyaa: 30Da kuma yadda Allah ya halicci Mutum Allah Maxaukaki ya ce:Ya ku mutãne! Idan kun kasance a cikin shakka a Tãshin ¡iyãma, to, lalle ne Mũ, Man halittaku daga turɓaya, sa'an nan kuma daga gudãjin jini, sa'an nan kuma daga taõka wadda ake halittãwa da wadda ba a halittawa dõmin, Mu bayyana muku. Kuma Munã tab batar da abin da Muke so a cikin mahaifa zuwa ga wani ajali ambatacce, sa'an nan kuma Munã fitar da ku kunã jãrĩri, sa'an nan kuma dõmin ku kai ga cikar ƙarfinku. Kuma daga cikin ku akwai wanda ke mutuwa, kuma daga gare ku akwai wanda ake mayarwa zuwa ga mafi ƙasƙancin rãyuwa dõmin kada ya san kõme a bãyan ya sani. Kuma kanã ganin ƙasa shiru, sa'an nan idan Muka saukar da ruwa a kanta, sai ta girgiza kuma ta kumbura, kuma ta tsirar da tsirrai daga kõwane nau'i mai ban sha'awa.[Al-hajji: 5] kuma ina ne Makomarsa kuma maye sakamakon wanda ya kyautata da wanda ya Munana a wannan Rayuwar kuma bayanin dalilan akan wanna Mas'alar ya gabata a sakin layi na (20) kuma shin waxan nan halittun sun samu ne haka kawai ko an samar da su saboda wata Manufa babba?Allah Maxaukakin Sarki ya ceShin, ba su yi dũbi ba a cikin mulkin sammai da ƙasa, da kuma abin da Allah Ya halitta daga kõme, kuma akwai tsammãni kasancewar ajalinsu, haƙĩƙa, ya kusanta? To, da wane lãbãri a bãyansa suke yin ĩmãni?Al-a'araf: 185kuma Allah Maxaukaki ya ce"Shin, to, kun yi zaton cẽwa Mun halitta ku ne da wãsa kuma lalle ku, zuwa gare Mu, bã zã ku kõmo ba?"Al-Mua'Munun: 115Kuma Al-qur;ani Maigirma kiyayye ne har zuwa yau da yaeren larabci wanda ya sauka da shi Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Lalle Mũ ne, Muka saukar da Ambato (Alƙur'ãni), kuma lale Mũ, haƙĩƙa, Mãsu kiyayẽwane gare shi.Al-Hijr: 9Ba'a tauye wani harafi daga cikinsa ba, kuma ya kuru da kwangaba kwan baya ya faru a cikinsa ko kuma tawaya ko canji Allah Maxaukaki ya ce:Shin, bã su kula da Alƙur'ãni, kuma dã yã kasance daga wurin wanin Allah haƙĩƙa, dã sun sãmu, a cikinsa, sãɓã wa jũnamai yawa?Al-Nisa'a: 82Kuma shi yana nan a buge kuma a ko ina kuma shi littafi ne maigirma Mai Mu;jiza, wanda kuma ya dace da a karanta shi ko a sauarare shi ko kuma a fassara Ma'anoninsa Kamar yadda cewa Sunnar Manzon Allah SAw take da komyarwarsa da tarihinsa a kiyaye suke kuma an rawaito su daidai da Jerin Masu riwaya waxanda aka amince da su kuma yana nan a buge da yaren larabci wand Manzon Allah SAW yayi Magana da shi kuma an fassara shi a yaruka da yawa, kuma Al-qur'ani da Sunnar mazon Allah SAW sune Tushe kwara xaya na Hukunce Hukuncen Musulunci da Shari'arsa saboda Musulunci ba'a koyarsa ta hanyar ayyukan wasu xaixaiku waxanda suke danganta kansu da Musuluncin; Kuma kaxai ana samun sa ne ta hanyar Wahayi daga Allah wanda yake Kiyayye, su ne Al-qur'ani maigirma da Sunnar Annabi Allah Maxaukakin ya ce a game da Sha'anin Al-qur'ani."Kuma lallai waxanda suka Kafirta da Ambato yayin da ya zo musu kuma cewa shi littafi ne cewa shi littafi ne Mabuwayi, kuma Varna bata shiga cikinsa ta gaba ne ko ta baya ne kuma saukakke ne daga Mai Hikima kuma abun godewa"Fussilat: 41-42Kuma Allah Maxaukaki ya ce game da sha'anin Sunnanr Manzon Allah kuma cewa ita ma Wahayi ce daga Allah"Kuma abunda Manzo ya zo muku da sho to ku karve shi kuma abunda ya haneku to ku hanu kuji tsoron Allah lallai Allah Mai tsananin Uquba ne"(Surat Al'hashr 7)Kuma lalle shi (Alƙur'ãni), haƙĩƙa, saukarwar Ubangijinhalittu ne.(192)Rũhi amintacce ne ya sauka da shi.(193)A zũciyarka, dõmin ka kasance daga mãsu gargaɗi.(194)Da harshe na Larabci mai bayãni.(195)Al-Shu'araa: 192-195Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma lalle ne haƙĩƙa, anã haɗa ka da Alƙur'ãni daga gun Mai hikima, Masani.Al-Naml: 6Kuma wannan Al-qur'ani saukakke ne daga Allah kuma mai gasgatawa ne da abunda ya gabace shi na litattafan Allah Allah Maxaukakin sarki ya ce:Kuma wannan Alƙur'ãni bai kasance ga a ƙirƙira shi ba daga wanin Allah, kuma amma shi gaskatawar wannan ne da yake a gabãninsa da bayãnin hukuncin littãffan Allah, Bãbu shakka a cikinsa, daga Ubangijin halittu yake.Yunus: 37Kuma Al-qur'ani maigirma ya fayyace mafi yawan Mas'alolin da Yahudu da Nasara sukai Savani akansu a cikin Addinansu Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Lalle ne wannan Alƙur'ãni yanã gaya wa Banĩ Isrãĩla mafi yawan abin da sũ suke sãɓa wa jũnansu a ciki.Al-Naml: 76Kuma Al-qurani Maigirma ya qunshi Dalilai da hujjoji da zasu iya tsayawa Hujja a kan Mutane baki xaya wajen Sanin haqiqoqi da suke da Alaqa da Allah SWT da Addinsa da sakamakonsa Allah Maxaukakin sarki ya ce:Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun buga wa mutãne a, cikin wannan Alƙur'ãni, daga kõwane misãli, ɗammãninsu su yi tunãni.Al-Zumar: 27kuma Allah Maxaukaki ya ce"Kuma mun saukar maka da Littafin mai bayani ga komai kuma shiriya ne da rahama ga Musulmai"Surat Annahl 89Kuma Al-qurani maigirma yana Amsa tambayoyi Masu yawa da suka kiximar da Miliyoyin Mutane saboda Al-qur'ani maigirma yana bayani yadda Allah ya halicci sammai da da qasa Allah Maxaukaki ya ce:Shin kuma waɗanda suka kãfirta ba, su gani da cẽwa lalle sammai da ƙasa sun kasance ɗinke, sai Muka bũɗe su, kuma Muka sanya dukan kome mai rai daga ruwa? Shin, bã zã su yi ĩmãni ba?Al-anbiyaa: 30Da kuma yadda Allah ya halicci Mutum Allah Maxaukaki ya ce:Ya ku mutãne! Idan kun kasance a cikin shakka a Tãshin ¡iyãma, to, lalle ne Mũ, Man halittaku daga turɓaya, sa'an nan kuma daga gudãjin jini, sa'an nan kuma daga taõka wadda ake halittãwa da wadda ba a halittawa dõmin, Mu bayyana muku. Kuma Munã tab batar da abin da Muke so a cikin mahaifa zuwa ga wani ajali ambatacce, sa'an nan kuma Munã fitar da ku kunã jãrĩri, sa'an nan kuma dõmin ku kai ga cikar ƙarfinku. Kuma daga cikin ku akwai wanda ke mutuwa, kuma daga gare ku akwai wanda ake mayarwa zuwa ga mafi ƙasƙancin rãyuwa dõmin kada ya san kõme a bãyan ya sani. Kuma kanã ganin ƙasa shiru, sa'an nan idan Muka saukar da ruwa a kanta, sai ta girgiza kuma ta kumbura, kuma ta tsirar da tsirrai daga kõwane nau'i mai ban sha'awa.[Al-hajji: 5] kuma ina ne Makomarsa kuma maye sakamakon wanda ya kyautata da wanda ya Munana a wannan Rayuwar kuma bayanin dalilan akan wanna Mas'alar ya gabata a sakin layi na (20) kuma shin waxan nan halittun sun samu ne haka kawai ko an samar da su saboda wata Manufa babba?Allah Maxaukakin Sarki ya ceShin, ba su yi dũbi ba a cikin mulkin sammai da ƙasa, da kuma abin da Allah Ya halitta daga kõme, kuma akwai tsammãni kasancewar ajalinsu, haƙĩƙa, ya kusanta? To, da wane lãbãri a bãyansa suke yin ĩmãni?Al-a'araf: 185kuma Allah Maxaukaki ya ce"Shin, to, kun yi zaton cẽwa Mun halitta ku ne da wãsa kuma lalle ku, zuwa gare Mu, bã zã ku kõmo ba?"Al-Mua'Munun: 115Kuma Al-qur;ani Maigirma kiyayye ne har zuwa yau da yaeren larabci wanda ya sauka da shi Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Lalle Mũ ne, Muka saukar da Ambato (Alƙur'ãni), kuma lale Mũ, haƙĩƙa, Mãsu kiyayẽwane gare shi.Al-Hijr: 9Ba'a tauye wani harafi daga cikinsa ba, kuma ya kuru da kwangaba kwan baya ya faru a cikinsa ko kuma tawaya ko canji Allah Maxaukaki ya ce:Shin, bã su kula da Alƙur'ãni, kuma dã yã kasance daga wurin wanin Allah haƙĩƙa, dã sun sãmu, a cikinsa, sãɓã wa jũnamai yawa?Al-Nisa'a: 82Kuma shi yana nan a buge kuma a ko ina kuma shi littafi ne maigirma Mai Mu;jiza, wanda kuma ya dace da a karanta shi ko a sauarare shi ko kuma a fassara Ma'anoninsa Kamar yadda cewa Sunnar Manzon Allah SAw take da komyarwarsa da tarihinsa a kiyaye suke kuma an rawaito su daidai da Jerin Masu riwaya waxanda aka amince da su kuma yana nan a buge da yaren larabci wand Manzon Allah SAW yayi Magana da shi kuma an fassara shi a yaruka da yawa, kuma Al-qur'ani da Sunnar mazon Allah SAW sune Tushe kwara xaya na Hukunce Hukuncen Musulunci da Shari'arsa saboda Musulunci ba'a koyarsa ta hanyar ayyukan wasu xaixaiku waxanda suke danganta kansu da Musuluncin; Kuma kaxai ana samun sa ne ta hanyar Wahayi daga Allah wanda yake Kiyayye, su ne Al-qur'ani maigirma da Sunnar Annabi Allah Maxaukakin ya ce a game da Sha'anin Al-qur'ani."Kuma lallai waxanda suka Kafirta da Ambato yayin da ya zo musu kuma cewa shi littafi ne cewa shi littafi ne Mabuwayi, kuma Varna bata shiga cikinsa ta gaba ne ko ta baya ne kuma saukakke ne daga Mai Hikima kuma abun godewa"Fussilat: 41-42Kuma Allah Maxaukaki ya ce game da sha'anin Sunnanr Manzon Allah kuma cewa ita ma Wahayi ce daga Allah"Kuma abunda Manzo ya zo muku da sho to ku karve shi kuma abunda ya haneku to ku hanu kuji tsoron Allah lallai Allah Mai tsananin Uquba ne"(Surat Al'hashr 7) 29. Kuma Musulunci yana Umarni da kyautatawa Iyaye, koda kuwa sun kasance ba Musulmai ba ne, kuma ya na wasiyya da 'Ya'ya.Musulunci yana Umarni da a kyautatawa Iyaye Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma Ubangijinka Ya hukunta kada ku bauta wa kõwa fãce Shi, kum game da mahaifa biyu ku kyautata kyautatawa, ko dai ɗayansu ya kai ga tsũfa a wurinka ko dukansu biyu, to, kada ka ce musu 'tir' kuma kada ka tsãwace su kuma ka faɗa musu magana mai karimci.Al-Isra'a: 23Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma Mun yi wasiyya ga mutum game da mahaifansa biyu; uwarsa tã ɗauke shi a cikin rauni a kan wani rauni, kuma yãyensa a cikin shekaru biyu (Muka ce masa) "Ka gõde Mini da kuma mahaifanka biyu. Makõma zuwa gare Ni kawai take."Luqman:14Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma Mun yi wasiyya ga mutum game da mahaifansa biyu da kyautatãwa, uwarsa tã yi cikinsa wahala, kuma ta haife shi wahala. cikinsa da yãyensa watã talãtin. Har a lõkacin da ya kai ga mafi ƙarfinsa, kuma ya kai shẽkara arba'in, ya ce: "Ya Ubangijĩna! Ka kange nidõmin in gõde wa ni'imarKa, wadda Ka ni'imta a kaina da kuma a kan mahaifãna biyu, kuma dõmin in aikata aikin ƙwarai wanda Kake yarda da shi, kuma Ka kyautata mini a cikin zuriyata. Lalle nĩ, nã tũba zuwa gare Ka, kuma lalle ni, inã daga mãsu sallamãwa (ga umurninKa)."Al-ahqaf: 15Kuma an rawaito daga Abu Huraira -Allah ya yarda da shi- ya ce: wani Mutum ya zo wajen Manzon Allah SAW sai ya ce: ya Manzon Allah waye mafi cancantar Mutane da kyakkyawar kusantata ? sai yace: "Mahaifiyarka" sai ya ce: sannan kuma wa? sai ya ce: "mahaifiyarka" sai ya ce: sannan kuma wa? sai ya ce: "mahaifiyarka" sai ya ce: sannan kuma wa? sai ya ce: "Mahaifinka"Sahih MuslimKuma wannan Umarni da Wasiyya ga Iyaye dai dai ne musulmai ne ko ba Musulmai ba neAn rawaito daga Asmaa Bint Abubakar ta ce: "Mahaifiya ta ta zo kuma ita Mushirika ce a lokacin Quraishawa kuma a lokacin su sunyiwa Annabi SAW Al-qawari tare da Xanta sai na tambayi Manzon Allah SAW sai na ce: Lallai Mahaifiyata ta zo tana son ganina, ko na iya zuwan mata? sai ya ce: "Ey kina iya zuwa ga Mahaifiyarki"Sahih Al-BukhariBa haka ba da za'a ce Mahaifa zasu yi qoqari cikin su juyar da Yaro daga Musulunci zuwa Kafurci saboda Musulci ya na Yana Umarninsa -Kuma hali a wannan lokacin- cewa shi ba zai bi su ba, kuma ya zauna a Matsayin Mai Imani da Allah kuma ya kayutata Musu kuma kuma ya zauna da su lafiya Allah Maxaukaki ya ce:"Kuma idan mahaifanka suka tsananta maka ga ka yi shirki game da Ni, ga abin da bã ka da ilmi gare shi, to, kada ka yi musu ɗã'a. Kuma ka abũce su a cikin dũniya gwargwadon sharĩ'a, kuma ka bi hanyar wanda ya mayar da al'amari zuwa gare Ni, sa'an nan zuwa gare Ni makõmarku take sa'an nan In bã ku lãbãri game da abin da kuka kasance kunã aikatãwa."Luqman: 15Kuma Musulunci baya hana Musulmi ya kyautatawa Makusantansa Mushirikai ko wasun Makusantansa indai basu zamanto abokan faxa ba a gare shi Allah Maxaukaki ya ce:{Allah bã Ya hana ku, daga waɗanda ba su yãƙe ku ba sabõda addini kuma ba su fitar da ku ba daga gidãjenku, ga ku kyautata musu kuma ku yi musu ãdalci. Lalle Allah Yanã son mãsu ãdalci}.[Al-Mumtahina: 8].Kuma Musulunci yana umarni da wasiyya ga 'ya'yansa kuma shi ne mafi girman abunda Musulunci yayi Umarni da Mahaifin ya koyar da Yaransa haqqokin Ubangijinsu kamar yada Manzon Allah SAW ya ce ga Xan Baffansa Abdullahi Bn Abbas -Allah ya yarda da su"Ya kai Yarp ko kai Xan Qaramin Yaro bana sanar da kai wasu kalmomi da zasu amfabeka da su? sai na ce E ya Manzon Allah sai ya ce: "Ka kiyaye Allah sai ya kiyaye ka ka kiyaye ka sai ka same shi a gabanka, ka tuna da Allah a lokacin yalwa sai ya tuna da kai a lokacin tsanani kuma idan zakayi roqo to ka roqi Allah, kuma idan zaka nemi taimako to ka nemi taimakon Allah"Ahmad ne ya rawaito shi 4/287Kuma Allah yayi Umarni ga Iyaye su koyawa 'Ya'yansu abunda zai anfanar da su a Al-amuran Addininsu da duniyarsu Allah Maxaukaki ya ce:Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku kãre wa kanku (da iyãlinku wata wuta makãmashinta mutãne da duwãtsu ne. A kanta akwai waɗansu malã'iku mãsu kauri, mãsu ƙarfi. Bã su sãɓã wa Allah ga abin da Ya umurce su, kuma sunã aikata abin da ake umunin su.Surat Al-tahrim: 6Kuma daga Ali -Allah ya yarda da shi- game da faxin Allah Maxaukaki:"Ku tsare Kanku da Iyalanku daga Wuta""Ku tsare Kanku da Iyalanku daga Wuta"Kuma Annabi SAW yayi Umarni ga Iyaye su koyawa Yaran su Sallah; don su tashi akan ta sai Manzon Allah SAW ya ce:"Ku Umarci 'Ya'yanku da Sallah suna 'yan Shekara Bakwai"Abu Daud Ya Rawaito shikuma Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Duukanku Masu Kiwi ne kuma dukkanku sai an tambayeku abunda kuke kiwo, Shugaba mai gadi akan talakawansa Mutum Mai kiwo akan Iyalansa kuma shi ne abun tambaya akan abunda aka bashi kiwon, kuma mace ma Mai kiwo ce a cikin gidan Mijinta kuma abar tambaya ce akan abunda aka bata kiwon kuma Xan aiki Mai gadi akan Dukiyar Mai gidansa kuma za'a tambaye shi kan abunda aka bashi kuma bai xayanku masu gadi kuma baki xayanku Masu kiwo ne kuma za'a tambaye ku kan abunda aka baku kiwonsa"Sahihin Ibn Hibban: 4490Kuma Musulunci ya Umarci Mahaifi da ciyar da 'Ya'yansa da kuma Mutanen gidansa kuma bayanin wani abu daga cikin wancan a sakin layi Mai lamba (18) kuma Annabi SAW yayi bayani falalar ciyarwa akan 'ya'ya sai ya ce:"Mafificin Dinare da Mtum zai ciyar shi wanda ya ciyar da Iyalansa da kuma Dinaren da Mutum ya ciyar da Dabbarsa a tafarkin Allah da kuma Dinaren da ya ciyar ga Abokansa a tafarkin Allah" Abu Qilaba ya ce: "sai ya fara Iyali sannan Abu Qilaba ya ce: Kuma wane Mutum ne ya fi girman lada kamar Mutum da ya ciyar da Iyali qanana don ya rufa musu Asiri kuma Allah ya anfanar da su da shi kuma ya wadata su"Sahih Muslim: 994Kuma Ubangijinka Ya hukunta kada ku bauta wa kõwa fãce Shi, kum game da mahaifa biyu ku kyautata kyautatawa, ko dai ɗayansu ya kai ga tsũfa a wurinka ko dukansu biyu, to, kada ka ce musu 'tir' kuma kada ka tsãwace su kuma ka faɗa musu magana mai karimci.Al-Isra'a: 23Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma Mun yi wasiyya ga mutum game da mahaifansa biyu; uwarsa tã ɗauke shi a cikin rauni a kan wani rauni, kuma yãyensa a cikin shekaru biyu (Muka ce masa) "Ka gõde Mini da kuma mahaifanka biyu. Makõma zuwa gare Ni kawai take."Luqman:14Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma Mun yi wasiyya ga mutum game da mahaifansa biyu da kyautatãwa, uwarsa tã yi cikinsa wahala, kuma ta haife shi wahala. cikinsa da yãyensa watã talãtin. Har a lõkacin da ya kai ga mafi ƙarfinsa, kuma ya kai shẽkara arba'in, ya ce: "Ya Ubangijĩna! Ka kange nidõmin in gõde wa ni'imarKa, wadda Ka ni'imta a kaina da kuma a kan mahaifãna biyu, kuma dõmin in aikata aikin ƙwarai wanda Kake yarda da shi, kuma Ka kyautata mini a cikin zuriyata. Lalle nĩ, nã tũba zuwa gare Ka, kuma lalle ni, inã daga mãsu sallamãwa (ga umurninKa)."Al-ahqaf: 15Kuma an rawaito daga Abu Huraira -Allah ya yarda da shi- ya ce: wani Mutum ya zo wajen Manzon Allah SAW sai ya ce: ya Manzon Allah waye mafi cancantar Mutane da kyakkyawar kusantata ? sai yace: "Mahaifiyarka" sai ya ce: sannan kuma wa? sai ya ce: "mahaifiyarka" sai ya ce: sannan kuma wa? sai ya ce: "mahaifiyarka" sai ya ce: sannan kuma wa? sai ya ce: "Mahaifinka"Sahih MuslimKuma wannan Umarni da Wasiyya ga Iyaye dai dai ne musulmai ne ko ba Musulmai ba neAn rawaito daga Asmaa Bint Abubakar ta ce: "Mahaifiya ta ta zo kuma ita Mushirika ce a lokacin Quraishawa kuma a lokacin su sunyiwa Annabi SAW Al-qawari tare da Xanta sai na tambayi Manzon Allah SAW sai na ce: Lallai Mahaifiyata ta zo tana son ganina, ko na iya zuwan mata? sai ya ce: "Ey kina iya zuwa ga Mahaifiyarki"Sahih Al-BukhariBa haka ba da za'a ce Mahaifa zasu yi qoqari cikin su juyar da Yaro daga Musulunci zuwa Kafurci saboda Musulci ya na Yana Umarninsa -Kuma hali a wannan lokacin- cewa shi ba zai bi su ba, kuma ya zauna a Matsayin Mai Imani da Allah kuma ya kayutata Musu kuma kuma ya zauna da su lafiya Allah Maxaukaki ya ce:"Kuma idan mahaifanka suka tsananta maka ga ka yi shirki game da Ni, ga abin da bã ka da ilmi gare shi, to, kada ka yi musu ɗã'a. Kuma ka abũce su a cikin dũniya gwargwadon sharĩ'a, kuma ka bi hanyar wanda ya mayar da al'amari zuwa gare Ni, sa'an nan zuwa gare Ni makõmarku take sa'an nan In bã ku lãbãri game da abin da kuka kasance kunã aikatãwa."Luqman: 15Kuma Musulunci baya hana Musulmi ya kyautatawa Makusantansa Mushirikai ko wasun Makusantansa indai basu zamanto abokan faxa ba a gare shi Allah Maxaukaki ya ce:{Allah bã Ya hana ku, daga waɗanda ba su yãƙe ku ba sabõda addini kuma ba su fitar da ku ba daga gidãjenku, ga ku kyautata musu kuma ku yi musu ãdalci. Lalle Allah Yanã son mãsu ãdalci}.[Al-Mumtahina: 8].Kuma Musulunci yana umarni da wasiyya ga 'ya'yansa kuma shi ne mafi girman abunda Musulunci yayi Umarni da Mahaifin ya koyar da Yaransa haqqokin Ubangijinsu kamar yada Manzon Allah SAW ya ce ga Xan Baffansa Abdullahi Bn Abbas -Allah ya yarda da su"Ya kai Yarp ko kai Xan Qaramin Yaro bana sanar da kai wasu kalmomi da zasu amfabeka da su? sai na ce E ya Manzon Allah sai ya ce: "Ka kiyaye Allah sai ya kiyaye ka ka kiyaye ka sai ka same shi a gabanka, ka tuna da Allah a lokacin yalwa sai ya tuna da kai a lokacin tsanani kuma idan zakayi roqo to ka roqi Allah, kuma idan zaka nemi taimako to ka nemi taimakon Allah"Ahmad ne ya rawaito shi 4/287Kuma Allah yayi Umarni ga Iyaye su koyawa 'Ya'yansu abunda zai anfanar da su a Al-amuran Addininsu da duniyarsu Allah Maxaukaki ya ce:Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku kãre wa kanku (da iyãlinku wata wuta makãmashinta mutãne da duwãtsu ne. A kanta akwai waɗansu malã'iku mãsu kauri, mãsu ƙarfi. Bã su sãɓã wa Allah ga abin da Ya umurce su, kuma sunã aikata abin da ake umunin su.Surat Al-tahrim: 6Kuma daga Ali -Allah ya yarda da shi- game da faxin Allah Maxaukaki:"Ku tsare Kanku da Iyalanku daga Wuta""Ku tsare Kanku da Iyalanku daga Wuta"Kuma Annabi SAW yayi Umarni ga Iyaye su koyawa Yaran su Sallah; don su tashi akan ta sai Manzon Allah SAW ya ce:"Ku Umarci 'Ya'yanku da Sallah suna 'yan Shekara Bakwai"Abu Daud Ya Rawaito shikuma Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Duukanku Masu Kiwi ne kuma dukkanku sai an tambayeku abunda kuke kiwo, Shugaba mai gadi akan talakawansa Mutum Mai kiwo akan Iyalansa kuma shi ne abun tambaya akan abunda aka bashi kiwon, kuma mace ma Mai kiwo ce a cikin gidan Mijinta kuma abar tambaya ce akan abunda aka bata kiwon kuma Xan aiki Mai gadi akan Dukiyar Mai gidansa kuma za'a tambaye shi kan abunda aka bashi kuma bai xayanku masu gadi kuma baki xayanku Masu kiwo ne kuma za'a tambaye ku kan abunda aka baku kiwonsa"Sahihin Ibn Hibban: 4490Kuma Musulunci ya Umarci Mahaifi da ciyar da 'Ya'yansa da kuma Mutanen gidansa kuma bayanin wani abu daga cikin wancan a sakin layi Mai lamba (18) kuma Annabi SAW yayi bayani falalar ciyarwa akan 'ya'ya sai ya ce:"Mafificin Dinare da Mtum zai ciyar shi wanda ya ciyar da Iyalansa da kuma Dinaren da Mutum ya ciyar da Dabbarsa a tafarkin Allah da kuma Dinaren da ya ciyar ga Abokansa a tafarkin Allah" Abu Qilaba ya ce: "sai ya fara Iyali sannan Abu Qilaba ya ce: Kuma wane Mutum ne ya fi girman lada kamar Mutum da ya ciyar da Iyali qanana don ya rufa musu Asiri kuma Allah ya anfanar da su da shi kuma ya wadata su"Sahih Muslim: 994 30-. Musulunci yana Umarni da Adalci a cikin Magana da kuma Aiki koda kuwa tare da Abokan gaba neAllah SWT ya sifantu da Adalci a cikin Ayyukansa da gudanar sa a tsakanin bayinsa kuma shi ne akan tafarki madaidaici a cikin abunda yayi Umarni da shi da kuma abunda ya hana a abunda yake cikin halittarsa Allah Maxaukaki ya ce:Allah Ya shaida cẽwa: Lalle ne bãbu abin bautãwa fãce Shi kuma malãiku da ma'abũta ilmi sun shaida, yana tsaye da ãdalci, bãbu abin bautãwa face Shi, Mabuwãyi, Mai hikima.Aal Imran: 18Kuma Allah yana Umarni da Adalci Allah Maxaukaki ya ce:"Ka ce Ubangiji na ya yi umarni da Adalci"Al-a'araf: 29Kuma baki xayan Manzanni da Annabawa -Amincin Allah a gare su sun zo da Adalci Allah Maxaukaki ya ce:Haƙĩƙa, lalle Mun aiko ManzanninMu da hujjõji bayyanannu, kuma Muka saukar da Littãfi da sikeli tãre da su dõmin mutãne su tsayu da ãdalciAl-hadid: 25Kuma Ma'auni shi ne Adalci a cikin Maganganu da Ayyikakuma Musulunci yana Umarni da Adalci a cikin magana da aiki har a wajen Abokan Gaba Allah Maxaukaki ya ce:Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku kasance mãsu tsayuwa da ãdalci, mãsu shaida sabõda Allah, kuma kõ dã a kanku ne kõ kuwa, mahaifa da mafi kusantar zumunta, ko (wanda ake yi wa shaida kõ a kansa) ya kasance mawadãci kõ matalauci, to, Allah ne Mafi cancanta da al'amarinsu. Sabõda haka, kada ku bĩbiyi son zũciya, har ku karkata. Kuma idan kuka karkatar da magana, kõ kuwa kuka kau da kai, to lalle ne Allah Yã kasance Masani ga abubuwan da kuke aikatãwa.Al-nisa: 135Allah Madaukakin Sarki ya ce:"Kuma kada qyamar wasu Mutane don sun hanaku zuwa Xakin Allah ya sanya ku cewa kuyi Ta'addanci, kuyi taimakekeniya kan biyayya da tsoron Allah kuma kada kuyi taimakekeniya kan savo da Ta'addanci, kuji tsoron Allah lallai Allah Mai tsananin uquba ne"Al-Ma'[da: 2Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku kasance mãsu tsayin daka dõmin Allah mãsu shaida da ãdalci. Kuma kada ƙiyayya da wasu mutane ta ɗauke ku a kan bã zã ku yi ãdalci ba. Ku yi ãdalci Shĩ ne mafi kusa ga taƙawa. Kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle Allah Masani ne ga abin da kuke aikatãwa.Alma'da:8Shi ka tava samu a cikin dokokin wasu al-ummai a yau ko a cikin Addinan Mutane kwatankwacin wannan Al-amari ? na shaidar gaskiya da faxin gaskiya har da kuwa ko akan ka ne ko Iyayenka ko makusantanka da kuma Umarni da Adalci har ga abokan gaba da AbokiAnnabi -tsira da amincin Allah- ya yi Umarni da Adalci a tsakanin 'Ya'yaAn rawaito daga Amir ya ce: naji Al-nu'aman Bn Bashir -Allah ya yarda da su- kuma shi yana kan Munbari yana cewa: baba na ya bani kyauta, sai Amrah Bint Rawahah ta ce: ni ba zan yarda ba har sai Manzon Allah ya shaida sai taje wajen Manzon Allah SAW sai ya ce: Ni na bawa Xana da Amrah Bint Rawaha ta haifa kyauta sai ta Umarce ne cewa in shaidar da kai ya Manzon Allah sai ya ce: "Ka bawa sauran 'Ya'yanka irinta?" ya ce: A'a sai ya ce: "to kuji tsoron Allah kuma ku daidaita tsakanin 'Ya'yanku" sai ya ce: sai na dawo sai ya Mayar da kyautarsa"Sahih Al-Bukhari: 2587Allah Ya shaida cẽwa: Lalle ne bãbu abin bautãwa fãce Shi kuma malãiku da ma'abũta ilmi sun shaida, yana tsaye da ãdalci, bãbu abin bautãwa face Shi, Mabuwãyi, Mai hikima.Aal Imran: 18Kuma Allah yana Umarni da Adalci Allah Maxaukaki ya ce:"Ka ce Ubangiji na ya yi umarni da Adalci"Al-a'araf: 29Kuma baki xayan Manzanni da Annabawa -Amincin Allah a gare su sun zo da Adalci Allah Maxaukaki ya ce:Haƙĩƙa, lalle Mun aiko ManzanninMu da hujjõji bayyanannu, kuma Muka saukar da Littãfi da sikeli tãre da su dõmin mutãne su tsayu da ãdalciAl-hadid: 25Kuma Ma'auni shi ne Adalci a cikin Maganganu da Ayyikakuma Musulunci yana Umarni da Adalci a cikin magana da aiki har a wajen Abokan Gaba Allah Maxaukaki ya ce:Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku kasance mãsu tsayuwa da ãdalci, mãsu shaida sabõda Allah, kuma kõ dã a kanku ne kõ kuwa, mahaifa da mafi kusantar zumunta, ko (wanda ake yi wa shaida kõ a kansa) ya kasance mawadãci kõ matalauci, to, Allah ne Mafi cancanta da al'amarinsu. Sabõda haka, kada ku bĩbiyi son zũciya, har ku karkata. Kuma idan kuka karkatar da magana, kõ kuwa kuka kau da kai, to lalle ne Allah Yã kasance Masani ga abubuwan da kuke aikatãwa.Al-nisa: 135Allah Madaukakin Sarki ya ce:"Kuma kada qyamar wasu Mutane don sun hanaku zuwa Xakin Allah ya sanya ku cewa kuyi Ta'addanci, kuyi taimakekeniya kan biyayya da tsoron Allah kuma kada kuyi taimakekeniya kan savo da Ta'addanci, kuji tsoron Allah lallai Allah Mai tsananin uquba ne"Al-Ma'[da: 2Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku kasance mãsu tsayin daka dõmin Allah mãsu shaida da ãdalci. Kuma kada ƙiyayya da wasu mutane ta ɗauke ku a kan bã zã ku yi ãdalci ba. Ku yi ãdalci Shĩ ne mafi kusa ga taƙawa. Kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle Allah Masani ne ga abin da kuke aikatãwa.Alma'da:8Shi ka tava samu a cikin dokokin wasu al-ummai a yau ko a cikin Addinan Mutane kwatankwacin wannan Al-amari ? na shaidar gaskiya da faxin gaskiya har da kuwa ko akan ka ne ko Iyayenka ko makusantanka da kuma Umarni da Adalci har ga abokan gaba da AbokiAnnabi -tsira da amincin Allah- ya yi Umarni da Adalci a tsakanin 'Ya'yaAn rawaito daga Amir ya ce: naji Al-nu'aman Bn Bashir -Allah ya yarda da su- kuma shi yana kan Munbari yana cewa: baba na ya bani kyauta, sai Amrah Bint Rawahah ta ce: ni ba zan yarda ba har sai Manzon Allah ya shaida sai taje wajen Manzon Allah SAW sai ya ce: Ni na bawa Xana da Amrah Bint Rawaha ta haifa kyauta sai ta Umarce ne cewa in shaidar da kai ya Manzon Allah sai ya ce: "Ka bawa sauran 'Ya'yanka irinta?" ya ce: A'a sai ya ce: "to kuji tsoron Allah kuma ku daidaita tsakanin 'Ya'yanku" sai ya ce: sai na dawo sai ya Mayar da kyautarsa"Sahih Al-Bukhari: 2587Wancan cewa shi Al-amarin Mutane ba zai daidaita ba haka ma na Qasashe kuma mutane ba zasu aminta ba akan Addinansu da jinanensu da Zuriyarsu da Mutuncin su da Dukiyoyin su da Qasashen su sai da Adalci kuma saboda wannan ne muke samun cewa Annabi SAW yayin da Kafiran Makkah suka matsantawa Musulmai a Makkah sai ya Umarce su SAW cewa da su yi Hijira zuwa Habasha; kuma ya dogara kan haka da cewa a can akwai wani Sarki Mai Adalci ba'a zaluntar kowa a garinsa. 31, Kuma Musulunci yana Umarnini da a kyautatawa halitta baki xaya, kuma yana kira zuwa kyawawan Halaye, da kuma kyawawan AyyukaMusulunci yana Umarni da a kyautatawa Iyaye Allah Maxaukakin Sarki ya ce:"Lallai Allah yana Umarni da Adalci da kyautatawa da kuma bawa Ma'aboda kusanci"Al-Nahl: 90Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Waɗanda suke ciyarwa a cikin sauƙi da tsanani kuma suke mãsu haɗiyẽwar fushi, kuma mãsu yãfe wa mutãne laifi. Kuma Allah Yana son mãsu kyautatãwa.Aal Imran: 134Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:Lallai cewa Allah ya rubuta kyautaye akan kowane abu, to idan zakuyi kisa to ku kyautata kisan kuma idan zakuyi yanaka to ku kyautata yankan kuma dayaku ya wasa wukar tasa, kuma don ya hutar da abin yankansaSahih Muslim: 1955Kuma Musulunci yana kira zuwa ga Kyawawan Halaye Allah Maxaukaki Sarki ya ce a cikin Siffar Manzon Allah Muhammad SAW a cikin litattafan da suka gabata."Waɗanda suke sunã bin Manzo, Annabi, Ummiyyi wanda suke sãmun sa rubũce a wurinsu, a cikin Attaura da Linjĩla yana Umartarsu da kyawawan ayyuka kuma yana hanasu daga Mummuna kuma yana halarta musu daxaxan abubuwa kuma yana haramta aaamusu munana kuma yana sauke musu abunda ya dame su da ququmqi waxanda suke kansu saboda haka waxanda sukai Imani da shi kuma suka qarfafe shi kuma suka taimake shi kuma suka bi hasken da ya saukar tare da shi waxan nan sune masu rabauta"Al-a'araf: 157:Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Ya ke Aisha Lallai Allah Mai tausasawa ne kuma yana bayarwa kan tausasawa abunda bai bayar ba akan tsanantawa, kuma da abunda bai bayar ba ga waninsa"Sahih Muslim: 2593Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Lallai Allah ya haramta muku Savata iyae Mata da Binne 'ya'ya Matakuma ya hana take haqqi kuma ya hanaku qila wa qala da yawan tambaya da kuma tozarta Dukiya"Sahih Al-Bukhari: 2408Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Ba zaku shiga Al-janna ba har sai kunyi Imani kuma ba zaku yi Imani ba har sai kunso Juna kuma ba na nuna muku wani abu ba wanda in kuka aikayashi zaku so junanku? ku yaxa Sallama a tsakaninku"Sahih Muslim: 54"Lallai Allah yana Umarni da Adalci da kyautatawa da kuma bawa Ma'aboda kusanci"Al-Nahl: 90Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Waɗanda suke ciyarwa a cikin sauƙi da tsanani kuma suke mãsu haɗiyẽwar fushi, kuma mãsu yãfe wa mutãne laifi. Kuma Allah Yana son mãsu kyautatãwa.Aal Imran: 134Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:Lallai cewa Allah ya rubuta kyautaye akan kowane abu, to idan zakuyi kisa to ku kyautata kisan kuma idan zakuyi yanaka to ku kyautata yankan kuma dayaku ya wasa wukar tasa, kuma don ya hutar da abin yankansaSahih Muslim: 1955Kuma Musulunci yana kira zuwa ga Kyawawan Halaye Allah Maxaukaki Sarki ya ce a cikin Siffar Manzon Allah Muhammad SAW a cikin litattafan da suka gabata."Waɗanda suke sunã bin Manzo, Annabi, Ummiyyi wanda suke sãmun sa rubũce a wurinsu, a cikin Attaura da Linjĩla yana Umartarsu da kyawawan ayyuka kuma yana hanasu daga Mummuna kuma yana halarta musu daxaxan abubuwa kuma yana haramta aaamusu munana kuma yana sauke musu abunda ya dame su da ququmqi waxanda suke kansu saboda haka waxanda sukai Imani da shi kuma suka qarfafe shi kuma suka taimake shi kuma suka bi hasken da ya saukar tare da shi waxan nan sune masu rabauta"Al-a'araf: 157:Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Ya ke Aisha Lallai Allah Mai tausasawa ne kuma yana bayarwa kan tausasawa abunda bai bayar ba akan tsanantawa, kuma da abunda bai bayar ba ga waninsa"Sahih Muslim: 2593Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Lallai Allah ya haramta muku Savata iyae Mata da Binne 'ya'ya Matakuma ya hana take haqqi kuma ya hanaku qila wa qala da yawan tambaya da kuma tozarta Dukiya"Sahih Al-Bukhari: 2408Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Ba zaku shiga Al-janna ba har sai kunyi Imani kuma ba zaku yi Imani ba har sai kunso Juna kuma ba na nuna muku wani abu ba wanda in kuka aikayashi zaku so junanku? ku yaxa Sallama a tsakaninku"Sahih Muslim: 54 32. Kuma Musulunci yana Umarni da kyawawan Halaye Kamar Gaskiya da sauke Amana da kuma kamewa da Kunya da Gwarzanta da Karamci da taimakawa Mabuqaci da kai gudun mawa ga wanda yake cikin wani hali, da ciyar da Mai jin yinwa, da kyautata Makwabtaka, da Sadar da Zumunci, da tausasawa Dabbobima Musulunci yana Umarni da kyawawan Xabi'u Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi-ya ce:"Ni an aiko ni ne kawai don in cika kyawawan Halaye"Sahihu Al-adab Al-mufrad: 207Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:Lallai mafi soyuwar ku a wajena, kuma mafi kusancinku a wajen zama a ranar al-qiyama shi mafi kyawunku Halaye, kuma lallai cewa mafi haushinku a wajena kuma mafi nisantarku zama kusa ni a ranar Al-qiyama su ne Masu yawan surutu, da Masu tsanantawa, da masu Jiji da kai, sai suka ce munsan Masu Masu yawan Magana da Masu tsanantawa kai, to su waye Masu Jiji da kai? Sai ya ce: Masu girman kai"Al-silsila Al-Sahiha: 791An rawaito daga Abdullahi Bn Amr Bn Al--Aas -Allah ya yarda da su- daga Annabi: Annabi bai Kasance Mai Al-fasha ba ko Mai yada Al-fasha ba, kuma ya kasance yana cewa: "Lallai zababbu daga cikinku Mafi kyawunku Halaye"Sahih Al-Bukhari: 3559Zuwa wanin haka na Ayoyi da Hadisai waxanda suke nuna cewa Musulunci Musulunci yana kwaxaitarwa akan Kyawawan Hakaye da kyawawan Ayyuka baki xayaMusulunci yana Umarni da kyawawan Xabi'u Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi-ya ce:"na hore ku da gaskiya saboda gaskiya tana shiryarwa zuwa biyayya, kuma lallai biyayye tana shiryarwa zuwa Al-janna kuma Mutum ba zai gushe ba yana yin gaskiya kuma yana kirdadonta har sai Allah ya rubuta shi a wajensa cikin Masu gaskiyaSahih Muslim: 2607Kuma daga cikin abunda Muslunci yayi umarni da shi shi bayarda Amana Allah MMaxaukaki ya ce:"Lallai Allah yana yana Umartarku da ku Mayar da Amanoni ga Masu su"Al-nisa: 58Musulunci yana Umarni da kamewa Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi-ya ce:"Mutane guda Uku wajibi ne akan Allah ya taimake su, sai ya faxa daga cikinsu Mai neman Aure don kame kansa"Sunan Al-tirmizi: 1655Kuma ya kasance a cikin Addu'arsa SAW cewa shi yana cewa:"Ya Ubangiji ina rokonka Shiriya da tsoron Allah da watadar Zuci da wadata"Sahih Muslim: 2721Musulunci yana Umarni da kunya Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi-ya ce:"kunya bata zuwa sai da Al-kairi"Sahih Al-Bukhari: 6117Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Kowane Addini yana da kyawawan halaye kuma kyawawan halayen Musulunci sune kunya"Baihaqi ne ya rawaito shi a cikin Rassan Imani 6/2619Kuma daga cikin abunda Musulunci yake umarni da shi Sadaukantaka saboda an rawaito daga Anas -Allah ya yarda da shi- ya ce:"Manzon Allah SAW ya kasance shi ne mafi kyawun Mutane kuma mafi sadaukantakarsu kuma mafi kyautarsu kuma haqiqa Mutanen Madina sun furgita saboda haka sai Manzon Allah ya riga kowa zuwa wurin a kan Doki"Sahih Al-Bukhari: 2820Manzon Allah -tsira da aminci su tabbata a gare shi-ya Kasance yana neman tsari dag atsoro saboda haka ya ke cewaYa Ubangiji ina neman tsarinka daga shaidanu maza da shaidanu mataSahih Al-Bukhari: 6374Kuma daga cikin abunda Muslunci yayi umarni da shi shi kyauta da Karamci Allah MMaxaukaki ya ce:Sifar waɗanda suke ciyar da dũkiyõyinsu a cikin hanyar Allah, kamar sifar ƙwãyã ce wadda ta tsirar da zangarniya bakwai, a cikin kõwace zangarniya akwai ƙwãya ɗari. Kuma Allah Yana riɓinyawa ga wanda Ya so. Kuma Allah Mawadãci ne, Masani.Al0baqara: 261Kuma Manzon Allah SAW ya kasance daga cikin halayansa akwai Karamci saboda an rawaito daga Ibn Abbas -Allah ya yarda da shi- ya ce:"Manzon Allah SAW ya kasance Mafi kyautar Mutane da Alkairi, kuma lokacin da yafi kowanne kyauta shi lokacin Azumin Ramadana lokacin da Mala'ika Jibril -Amincin Allah a gare shi - ya ke zuwan masa kowane dare a cikin watan Azumi har sai ya Wuce yana gabatar Masa da Al-qur'ani saboda idan Jibril ya gamu da shi -amincin Allah a gareshi- ya kasance mafi kyauta da Alkairi daga sakakkiyar Iska"Sahih Al-Bukhari: 1902Kuma daga cikin abunda Musulunci taimakon Mabukaci da agazawa wanda ya Matsu da ciyar da mai jin Yinwa da kuma kyautata Maqwaftaka da Sadar da zumunci da tausayawa Dabbobi"Daga Abdullahi Bin Amr -Allah ya yarda da shi- Cewa wani Mutum ya tambayi Manzon Allah -tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi: Wane aiki ne yafi a Musulunci? ya ce ka ciyar da Abinci kuma kayi Sallama ga wanda ka sani da wanda baka sani ba"Sahih Al-Bukhari: 12Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Wata rana wani Mutum yana tafiya a hanya sai qishirwa da kama shi sai ya samu wata rijiya sai ya shiga ciki yasha ruwa sannan ya futo sai ga wani kare yana lallagi yana cin yashi saboda Qishi sai Mutumin ya ce: lallai wannan karen irin abunda ya kamo ni ne ya kamo shi sai ya shiga rijiyar ya ciko Huffinsa sannan ya kama bakinsa ya bashi ruwan sai Allah ya gode masa kuma ya gafarta Masa" suka ce ya manzon Allah shin zamu samu ladan ciyar da Dabbobi, sai ya ce: Ey a cikin kowace hanta akwai lada"Sahihin Ibn Hibban: 544Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Mai kai kawo ga Wacce Mijinta ya Mutu ko Miskini Kamar mai jahadi ne a yafarkin Allah ko Mai tsayuwar dare kuma mai Azumi da Rana"Sahih Al-Bukhari: 5353Kuma Musulunci yana qarfafa kan haqqoqin Makusanta kuma yana wajabta sadar da zumunci Makusanta Allah Maxaukaki ya ce:Annabi ne mafi cancanta ga mũminai bisa ga su kansu, kuma mãtansa uwãyensu ne. Kuma ma'abuta zumunta waɗansunsu sun fi waɗansu a cikin Littãfin Allah bisa ga mũminai da Muhãjirai, fãce fa idan kun aikata wani alhẽri zuwa ga majiɓintanku. Wancan yã kasance a cikin Littafi, rubũtacce.Al-ahzab: 6Kuma ya tsawatar daga Yanke zumunci kuma ya gwamata da Varna a bayan Qasa Allah Maxaukaki ya ce:To, shin, kunã fãtan idan kun jũya (daga umurnin) zã ku yi ɓarna a cikin ƙasã, kuma ku yan yanke zumuntarku?(22)Waɗannan sũ ne waɗanda Allah Ya la'anẽ su, sa'an nan Ya kurumtar da su, kuma Ya makantar da ganinsu.230Muhammad: 22-23Kuma Manzon Allah SAW ya ce: "Ba zai tava shiga Al-janna ba wanda ya yanke zumunci"Sahih Muslim: 2556Kuma Makusantar da sadar da zumuncinsu: Iyaye da 'Yan Uwa Maza da 'yan Uwa Mata da Kawunnai da Goggoye da yakumbobi da YadikkokiKuma Musulunci yana qarfafa haqqin Makwaftaka har ko da kuwa ya kasance Kafiri ne Allah Maxaukaki ya ce:Kuma ku bauta wa Allah kuma kada ku haɗa wani da Shi, kuma ga mahaifa ku yi kyautatãwa, kuma ga ma'abũcin zumunta da marãyu da matalauta, da maƙwabci ma'abũcin kusanta, da maƙwabci manĩsanci, da abõki a gẽfe da ɗan hanya, da abin da hannuwanku na dãma suka mallaka. Lalle ne Allah bã Ya son wanda ya kasance mai tãƙama, mai yawan alfahari.Al-nisa: 36Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Mala'ika bai gushe ba yana yi mun wasiyya da Makwafci har sai da na zaci cewa shi zai gaje ni"Sahihu Abu daud: 5152"Ni an aiko ni ne kawai don in cika kyawawan Halaye"Sahihu Al-adab Al-mufrad: 207Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:Lallai mafi soyuwar ku a wajena, kuma mafi kusancinku a wajen zama a ranar al-qiyama shi mafi kyawunku Halaye, kuma lallai cewa mafi haushinku a wajena kuma mafi nisantarku zama kusa ni a ranar Al-qiyama su ne Masu yawan surutu, da Masu tsanantawa, da masu Jiji da kai, sai suka ce munsan Masu Masu yawan Magana da Masu tsanantawa kai, to su waye Masu Jiji da kai? Sai ya ce: Masu girman kai"Al-silsila Al-Sahiha: 791An rawaito daga Abdullahi Bn Amr Bn Al--Aas -Allah ya yarda da su- daga Annabi: Annabi bai Kasance Mai Al-fasha ba ko Mai yada Al-fasha ba, kuma ya kasance yana cewa: "Lallai zababbu daga cikinku Mafi kyawunku Halaye"Sahih Al-Bukhari: 3559Zuwa wanin haka na Ayoyi da Hadisai waxanda suke nuna cewa Musulunci Musulunci yana kwaxaitarwa akan Kyawawan Hakaye da kyawawan Ayyuka baki xayaMusulunci yana Umarni da kyawawan Xabi'u Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi-ya ce:"na hore ku da gaskiya saboda gaskiya tana shiryarwa zuwa biyayya, kuma lallai biyayye tana shiryarwa zuwa Al-janna kuma Mutum ba zai gushe ba yana yin gaskiya kuma yana kirdadonta har sai Allah ya rubuta shi a wajensa cikin Masu gaskiyaSahih Muslim: 2607Kuma daga cikin abunda Muslunci yayi umarni da shi shi bayarda Amana Allah MMaxaukaki ya ce:"Lallai Allah yana yana Umartarku da ku Mayar da Amanoni ga Masu su"Al-nisa: 58Musulunci yana Umarni da kamewa Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi-ya ce:"Mutane guda Uku wajibi ne akan Allah ya taimake su, sai ya faxa daga cikinsu Mai neman Aure don kame kansa"Sunan Al-tirmizi: 1655Kuma ya kasance a cikin Addu'arsa SAW cewa shi yana cewa:"Ya Ubangiji ina rokonka Shiriya da tsoron Allah da watadar Zuci da wadata"Sahih Muslim: 2721Musulunci yana Umarni da kunya Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi-ya ce:"kunya bata zuwa sai da Al-kairi"Sahih Al-Bukhari: 6117Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Kowane Addini yana da kyawawan halaye kuma kyawawan halayen Musulunci sune kunya"Baihaqi ne ya rawaito shi a cikin Rassan Imani 6/2619Kuma daga cikin abunda Musulunci yake umarni da shi Sadaukantaka saboda an rawaito daga Anas -Allah ya yarda da shi- ya ce:"Manzon Allah SAW ya kasance shi ne mafi kyawun Mutane kuma mafi sadaukantakarsu kuma mafi kyautarsu kuma haqiqa Mutanen Madina sun furgita saboda haka sai Manzon Allah ya riga kowa zuwa wurin a kan Doki"Sahih Al-Bukhari: 2820Manzon Allah -tsira da aminci su tabbata a gare shi-ya Kasance yana neman tsari dag atsoro saboda haka ya ke cewaYa Ubangiji ina neman tsarinka daga shaidanu maza da shaidanu mataSahih Al-Bukhari: 6374Kuma daga cikin abunda Muslunci yayi umarni da shi shi kyauta da Karamci Allah MMaxaukaki ya ce:Sifar waɗanda suke ciyar da dũkiyõyinsu a cikin hanyar Allah, kamar sifar ƙwãyã ce wadda ta tsirar da zangarniya bakwai, a cikin kõwace zangarniya akwai ƙwãya ɗari. Kuma Allah Yana riɓinyawa ga wanda Ya so. Kuma Allah Mawadãci ne, Masani.Al0baqara: 261Kuma Manzon Allah SAW ya kasance daga cikin halayansa akwai Karamci saboda an rawaito daga Ibn Abbas -Allah ya yarda da shi- ya ce:"Manzon Allah SAW ya kasance Mafi kyautar Mutane da Alkairi, kuma lokacin da yafi kowanne kyauta shi lokacin Azumin Ramadana lokacin da Mala'ika Jibril -Amincin Allah a gare shi - ya ke zuwan masa kowane dare a cikin watan Azumi har sai ya Wuce yana gabatar Masa da Al-qur'ani saboda idan Jibril ya gamu da shi -amincin Allah a gareshi- ya kasance mafi kyauta da Alkairi daga sakakkiyar Iska"Sahih Al-Bukhari: 1902Kuma daga cikin abunda Musulunci taimakon Mabukaci da agazawa wanda ya Matsu da ciyar da mai jin Yinwa da kuma kyautata Maqwaftaka da Sadar da zumunci da tausayawa Dabbobi"Daga Abdullahi Bin Amr -Allah ya yarda da shi- Cewa wani Mutum ya tambayi Manzon Allah -tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi: Wane aiki ne yafi a Musulunci? ya ce ka ciyar da Abinci kuma kayi Sallama ga wanda ka sani da wanda baka sani ba"Sahih Al-Bukhari: 12Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Wata rana wani Mutum yana tafiya a hanya sai qishirwa da kama shi sai ya samu wata rijiya sai ya shiga ciki yasha ruwa sannan ya futo sai ga wani kare yana lallagi yana cin yashi saboda Qishi sai Mutumin ya ce: lallai wannan karen irin abunda ya kamo ni ne ya kamo shi sai ya shiga rijiyar ya ciko Huffinsa sannan ya kama bakinsa ya bashi ruwan sai Allah ya gode masa kuma ya gafarta Masa" suka ce ya manzon Allah shin zamu samu ladan ciyar da Dabbobi, sai ya ce: Ey a cikin kowace hanta akwai lada"Sahihin Ibn Hibban: 544Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Mai kai kawo ga Wacce Mijinta ya Mutu ko Miskini Kamar mai jahadi ne a yafarkin Allah ko Mai tsayuwar dare kuma mai Azumi da Rana"Sahih Al-Bukhari: 5353Kuma Musulunci yana qarfafa kan haqqoqin Makusanta kuma yana wajabta sadar da zumunci Makusanta Allah Maxaukaki ya ce:Annabi ne mafi cancanta ga mũminai bisa ga su kansu, kuma mãtansa uwãyensu ne. Kuma ma'abuta zumunta waɗansunsu sun fi waɗansu a cikin Littãfin Allah bisa ga mũminai da Muhãjirai, fãce fa idan kun aikata wani alhẽri zuwa ga majiɓintanku. Wancan yã kasance a cikin Littafi, rubũtacce.Al-ahzab: 6Kuma ya tsawatar daga Yanke zumunci kuma ya gwamata da Varna a bayan Qasa Allah Maxaukaki ya ce:To, shin, kunã fãtan idan kun jũya (daga umurnin) zã ku yi ɓarna a cikin ƙasã, kuma ku yan yanke zumuntarku?(22)Waɗannan sũ ne waɗanda Allah Ya la'anẽ su, sa'an nan Ya kurumtar da su, kuma Ya makantar da ganinsu.230Muhammad: 22-23Kuma Manzon Allah SAW ya ce: "Ba zai tava shiga Al-janna ba wanda ya yanke zumunci"Sahih Muslim: 2556Kuma Makusantar da sadar da zumuncinsu: Iyaye da 'Yan Uwa Maza da 'yan Uwa Mata da Kawunnai da Goggoye da yakumbobi da YadikkokiKuma Musulunci yana qarfafa haqqin Makwaftaka har ko da kuwa ya kasance Kafiri ne Allah Maxaukaki ya ce:Kuma ku bauta wa Allah kuma kada ku haɗa wani da Shi, kuma ga mahaifa ku yi kyautatãwa, kuma ga ma'abũcin zumunta da marãyu da matalauta, da maƙwabci ma'abũcin kusanta, da maƙwabci manĩsanci, da abõki a gẽfe da ɗan hanya, da abin da hannuwanku na dãma suka mallaka. Lalle ne Allah bã Ya son wanda ya kasance mai tãƙama, mai yawan alfahari.Al-nisa: 36Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Mala'ika bai gushe ba yana yi mun wasiyya da Makwafci har sai da na zaci cewa shi zai gaje ni"Sahihu Abu daud: 5152 33. Musulunci ya Halatta abubuwa masu daxi na abun ci da sha, kuma yayi umarni da tsarkin Zuciya da jiki saboda haka ya halatta Aure, Kamar yadda ya Umarci Annabawa -Amincin Allah a gare su- da hakan, saboda su suna Umarni ne da dukkan abu mai kyauMusulunci yana Umarni da kyawawan Xabi'u Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi-ya ce:Daga Abu Huraira daga Annabi ya ce: "Lallai Allah Mai tsarki ne kuma baya karba sai mai Tsarki, kuma ya Umarci Muminai da duk abinda ya Umarci Mazanninsa sai ya ce:{Ya ku Manzanni kuci daga dadadan abubuwa kuma kuyi aiki nagari,lallai ni ina sane da abinda kuke aikatawa} [51] kuma ya ce: {Ya ku Masu Imani kuci daga dadadan abinda muka Azurtaku} [Bakara172] sannan Annabi ya fadi tsawatarwa ga Al'ummarsa daga Haram; sabida ya ambaci wani Mutum da yake yawaita tafiya, kuma acikin ayyukan alheri kamar hajji da Jihadi da kuma neman abinci, gashi budubudu yake gashinsa yayi kura sabida tsawon tafiyarsa a cikin bin Allah, kuma yana daga hannunsa sama da Addua yana rokon Allah da kuma kaskantar da kansa izuwa ga Allah, kuma tare da hakan an nisanta amsa masa wannan Adduar tasa, sabida Munin abinda yayi, ta yadda Abincinsa ya kasance Haram ne abun shansa Haram ne.Sahih Muslim: 1015Allah Madaukakin Sarki ya ce:Ka ce: "Wãne ne ya haramta ƙawar Allah, wadda Ya fitar sabõda bãyinSa, da mãsu dãɗi daga abinci?" Ka ce: "Sũ, dõmin waɗanda suka yi ĩmani suke a cikin rãyuwar dũniya, suna keɓantattu a Rãnar Kiyãma. "Kamar wannan ne Muke bayyana ãyõyi, daki-daki, ga mutãnen da suke sani.Al-a'araf: 32Kuma Musulmi yayi umarni da tsarkin Zuciya da kuma Jikin da Gida saboda wancan ya halatta Aure kamar yadda yayi Umarci Annabawa da manzanni da wancan batu, sabo sune suke umarni da dukkan abunda yake kyakkyawa Allah Maxaukaki ya ce:Kuma Allah Yã sanya muku mãtan aure daga kãwunanku, kuma Ya sanya muku daga mãtan aurenku ɗiyã da jĩkõki, kuma Ya arzũta ku daga abũbuwa mãsu dãɗi. Shin fa, da ƙarya suke yin ĩmãni, kuma da ni'imar Allah sũ, suke kãfirta?Al-Nahl: 72Allah Maxaukakin Sarki ya ce:"Kuma tufafinka to ka tasarlaleta" (4)Kuma Gumaka ka kaurace musu (5)Ak-Mudathir: 4-5Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Babu wanda zai shiga Al-janna wanda yakasance a cikin Zuciyarsa akwai Girman kai gwargwadon qwayar Zarra a Zuciyarsa, sai wani Mutum ya ce: Lallai Mutum yana son ya kasance tufafinsa suyi fesfes kuma Takalmasa ma fesfes sai ya ce: Lallai Allah ai Mai kyau ne kuma yana son kyau, girman kai shi ne take gaskiya da kuma raina Mutane"Sahih Muslim: 91Daga Abu Huraira daga Annabi ya ce: "Lallai Allah Mai tsarki ne kuma baya karba sai mai Tsarki, kuma ya Umarci Muminai da duk abinda ya Umarci Mazanninsa sai ya ce:{Ya ku Manzanni kuci daga dadadan abubuwa kuma kuyi aiki nagari,lallai ni ina sane da abinda kuke aikatawa} [51] kuma ya ce: {Ya ku Masu Imani kuci daga dadadan abinda muka Azurtaku} [Bakara172] sannan Annabi ya fadi tsawatarwa ga Al'ummarsa daga Haram; sabida ya ambaci wani Mutum da yake yawaita tafiya, kuma acikin ayyukan alheri kamar hajji da Jihadi da kuma neman abinci, gashi budubudu yake gashinsa yayi kura sabida tsawon tafiyarsa a cikin bin Allah, kuma yana daga hannunsa sama da Addua yana rokon Allah da kuma kaskantar da kansa izuwa ga Allah, kuma tare da hakan an nisanta amsa masa wannan Adduar tasa, sabida Munin abinda yayi, ta yadda Abincinsa ya kasance Haram ne abun shansa Haram ne.Sahih Muslim: 1015Allah Madaukakin Sarki ya ce:Ka ce: "Wãne ne ya haramta ƙawar Allah, wadda Ya fitar sabõda bãyinSa, da mãsu dãɗi daga abinci?" Ka ce: "Sũ, dõmin waɗanda suka yi ĩmani suke a cikin rãyuwar dũniya, suna keɓantattu a Rãnar Kiyãma. "Kamar wannan ne Muke bayyana ãyõyi, daki-daki, ga mutãnen da suke sani.Al-a'araf: 32Kuma Musulmi yayi umarni da tsarkin Zuciya da kuma Jikin da Gida saboda wancan ya halatta Aure kamar yadda yayi Umarci Annabawa da manzanni da wancan batu, sabo sune suke umarni da dukkan abunda yake kyakkyawa Allah Maxaukaki ya ce:Kuma Allah Yã sanya muku mãtan aure daga kãwunanku, kuma Ya sanya muku daga mãtan aurenku ɗiyã da jĩkõki, kuma Ya arzũta ku daga abũbuwa mãsu dãɗi. Shin fa, da ƙarya suke yin ĩmãni, kuma da ni'imar Allah sũ, suke kãfirta?Al-Nahl: 72Allah Maxaukakin Sarki ya ce:"Kuma tufafinka to ka tasarlaleta" (4)Kuma Gumaka ka kaurace musu (5)Ak-Mudathir: 4-5Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Babu wanda zai shiga Al-janna wanda yakasance a cikin Zuciyarsa akwai Girman kai gwargwadon qwayar Zarra a Zuciyarsa, sai wani Mutum ya ce: Lallai Mutum yana son ya kasance tufafinsa suyi fesfes kuma Takalmasa ma fesfes sai ya ce: Lallai Allah ai Mai kyau ne kuma yana son kyau, girman kai shi ne take gaskiya da kuma raina Mutane"Sahih Muslim: 91 34. Musulunci ya haramta dukkan Tushen dukkan Haramun kamar Shirka da bautar Gumaka, da shaci faxi ga Allah bada Ilimi ba, da kashe 'ya'ya. da kashe ran da Allah ya haramta, da varna a bayan qasa, da Sihiri da Al-fasha ta Fili da ta Voye da Zina da Liwaxi, kuma ya haramta Riba, da cin Mushe, da abunda aka yanka ga Gumaka da Dodanni, da kuma cin Naman Alade, da sauran Najasa da Kazanta, kuma ya Haramta cin Dukiyar Maraya da tauye Mudu da ma'auni, kuma ya haramta yanke Zumunci kuma Annabawa -Amincin Allah a gare su- baki xayansu sun haxu kan haramcin waxan nan AbubuwanMusulunci ya haramta Tushen Haramun Kamar Shirka da Allah da kafirci da Bautar Gumaka da faxi ga Allah ba tare da Ilimi ba da kashe "ya'ya Allah Maxaukaki ya ce:Ka ce: "Ku zo, in karanta abin da Ubangijinku Ya haramta." wãjibi ne a kanku kada ku yi shirkin kõme da Shi, kuma ga mahaifa biyu (ku kyautata) kyautatãwa, kuma kada ku kashe ɗiyanku sabõda talauci, Mũ ne Muke azurta ku, kũ da su, kuma kada ku kusanci abũbuwa alfãsha, abin da ya bayyana daga gare ta da abin da ya ɓõyu, kada ku kashe rai wanda Allah Ya haramta, fãce da hakki. Wannan ne (Allah) Ya yi muku wasiyya da Shi: Tsammãninku, kunã hankalta.Kada ku kusanci dũkiyar marãya fãce da wadda take ita ce mafi kyau, har ya kai ga ƙarfinsa. Kuma ku cika mũdu da sikẽli da ãdalci, bã Mu kallafã wa rai fãce iyãwarsa. Kuma idan kun faɗi magana, to, ku yi ãdalci, kuma ko dã yã kasance ma'abũcin zumunta ne. Kuma da alkawarin Allah ku cika. wannan ne Ya yi muku wasiyya da shi: Tsammãninku, kunã tunãwa.Al-an'am: 151-152Allah Madaukakin Sarki ya ce:Ka ce: "Abin sani kawai, Ubangijina Yã hana abũbuwanalfãsha; abin da ya bayyana daga gare su da abin da ya ɓõyu, da zunubi da rarraba jama'a, bã da wani hakki ba, kuma da ku yi shirki da Allah ga abin da bai saukar da wani dalĩli ba gare shi, kuma da ku faɗi abin da ba ku sani ba, ga Allah."Al-a'araf: 33kuma Musulunci ya Haramta Kashe Rai da baiyi laifin komai ba Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma kada ku kashe rai wanda Allah Ya haramta fãce da haƙƙi, kuma wanda aka kashe, yanã wanda aka zãlunta to, haƙĩƙa Mun sanya hujja ga waliyyinsa, sai dai kada ya ƙẽtare haddi a cikin kashẽwar. Lalle shĩ ya kasance wanda ake taimako.Al-Israa: 33Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma waɗanda bã su kiran wani ubangiji tãre da Allah, kuma bã su kashe rai wanda Allah Ya haramta fãce da hakki kuma bã su yin zina. Kuma wanda ya aikata wancan, zai gamu da laifuffuka,Al-Furqan: 68kuma Musulunci ya Haramta Varna a bayan Qasa Allah Maxaukakin Sarki ya ce:"Kuma kada kuyi Varna a bayan Qasa bayan ai gyara ta"Al-a'araf: 58Kuma Alla Maxaukakin Sarki ya ce game da Annabi Shu'abu -Amincin Allah a gare shi- cewa ya ce da Mutanensa:Kuma zuwa Madayana ɗan'uwansu Shu'aibu, ya ce: "Ya mutãnena! Ku bauta wa Allah; bã ku da wani abin bauta wa waninSa. Lalle ne, wata hujja bayyananniya daga Ubangijinku tã zõ muku! Sai ku cika mũdu da sikeli kumakada ku nakasa wa mutãne kãyansu, kuma kada ku yi fasãdi a cikin ƙasa a bãyan gyaranta. Wannan ne mafi alhẽri a gare ku, idan kun kasance mũminai."Al-a'araf: 85Kuma Allah ya Haramta Sihiri Allah Maxaukakin Sarki ya ce:"Kuma ka jẽfa abin da ke a cikin hannun dãmanka, ta cafe abin da suka aikata. Lalle ne abin da suka aikata mãkircin masihirci ne kuma masihirci bã ya cin nasara a duk inda ya je."Taha: 69Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:Ku guji abubuwa bakwai masu halakarwa suka ce ya Ma'aikin Allah! wadanne ne su? ya ce: Yin shirka da Allah, da sihiri, da kashe rai wacce Allah ya haramta face da gaskiya, da cin riba, da cin dukiyar maraya, da juyawa ranar yaki, da kuma yiwa katangaggiya marafkaniya mumina kazafiSahih Al-Bukhari: 6583Kuma Musulunci ya haramta Alfasha ta fili da voye da Zina da Luwaxi kuma ya gabata a cikin farkon wannan lokaci ya faxi dalilai akan hakan kuma Musulun ya haramta Riba Allah Maxaukaki ya ce:Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku bi Allah da taƙawa kuma ku bar abin da ya rage daga riba, idan kun kasance mãsu ĩmãni.(278)To, idan ba ku aikata ba to, ku sani fa da akwai yãƙi daga Allah da ManzonSa. Kuma idan kun tũba to kuna da asalin dũkiyõyinku, bã ku zãlunta, kuma bã a zãluntar ku.(279)Al-Baqara: 278-279Kuma Allah bai tsawatar da Mai Savo ba da Yaqi kamar yadda ya tsawatar da Ma'abocin Riba; saboda a cikin Riba akawai ruguza Addinai da Qasashe da dukiyoyi da KawunaKuma Musulunci ya haramta cin Mushe da abunda aka yanka ga Gumaka da Dodanni kuma ya haramta naman Alade Allah Maxaukaki ya ce:{An haramta muku mũshe da jini da nãman alade da abin da aka ambaci sũnan wanin Allah a gare shi, da mãƙararriya da jefaffiya da mai gangarõwa da sõkakkiya, da abin da mãsu dãgi suka ci, fãce abin da kuka yanka}.[Al-Maa'ida: 3].Kuma Musulunci ya haramta Sha giya da sauran Najasosi da Munanan abubuwa Allah Maxaukaki ya ce:Ya ku waɗanda suka yi ĩmãni! Abin sani kawai, giya da cãca da refu da kiban ƙuri'a, ƙazanta ne daga aikin shaiɗan, sai ku nĩsance shi, wa la'alla ku ci nasara.(90)Abin sani kawaĩ Shaiɗan yanã nufin ya aukar da adãwa da ƙeta a tsakãninku, a cikin giya da cãca, kuma ya kange ku daga ambaton Allah, kuma daga sallah. To, shin, ku mãsu hanuwa ne?(91)Al-Ma'ida: 90-91Kuma ya gabata a cikin sakin layi mai lamba ta (31) bayanin labarin Allah SWT cewa daga cikin siffofin Manzon Allah SAW a cikin Al-taura cewa shi ya ya haramta Munanan Abubuwa Allah Maxaukaki ya ce:Waɗanda suke sunã bin Manzo, Annabi, Ummiyyi wanda suke sãmun sa rubũce a wurinsu, a cikin Attaura da Linjĩla.yanã umurnin su da alhẽri, kuma yana hana su daga barin abin da bã a so; kuma yana halatta musu abũ- buwa masu dadi, kuma yana haramtarwar mũnana a kansu. Kuma yanã kãyar da nauyinsu daga barinsu, da ƙuƙummai waɗannan da suka kasance a kansu.Al-a'araf: 157:kuma Musulunci ya Haramta cinye Dukiyar Maraya Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma ku bai wa marãyu dũkiyõyinsu, kuma kada ku musanya mummuna da mai kyau. Kuma kada ku ci dũkiyõyinsu zuwa ga dũkiyõyinku. Lalle shi, yã kasance zunubi ne mai girma.Al-Nisa'a: 2Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Lalle ne, waɗanda suke cĩn dũkiyar marãyu da zãlunci, to, wuta kawai suke ci a cikin cikkunansu, kuma za su shiga cikin wata wuta mai tsanani.Al-nisa'a: 10kuma Musulunci ya Haramta Tauye Mudu Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Bone ya tabbata ga Masu tauye Mudu (1)Waɗanda suke idan suka auna daga mutãne suna cika mũdu.(2)Kuma idan sun auna musu da zakka ko da sikẽli, suna ragẽwa(3)Ashe! Waɗancan bã su tabbata cẽwa lalle sũ, ana tãyar da su ba?(4)Al-Muxaffifin: 1-4Ka ce: "Ku zo, in karanta abin da Ubangijinku Ya haramta." wãjibi ne a kanku kada ku yi shirkin kõme da Shi, kuma ga mahaifa biyu (ku kyautata) kyautatãwa, kuma kada ku kashe ɗiyanku sabõda talauci, Mũ ne Muke azurta ku, kũ da su, kuma kada ku kusanci abũbuwa alfãsha, abin da ya bayyana daga gare ta da abin da ya ɓõyu, kada ku kashe rai wanda Allah Ya haramta, fãce da hakki. Wannan ne (Allah) Ya yi muku wasiyya da Shi: Tsammãninku, kunã hankalta.Kada ku kusanci dũkiyar marãya fãce da wadda take ita ce mafi kyau, har ya kai ga ƙarfinsa. Kuma ku cika mũdu da sikẽli da ãdalci, bã Mu kallafã wa rai fãce iyãwarsa. Kuma idan kun faɗi magana, to, ku yi ãdalci, kuma ko dã yã kasance ma'abũcin zumunta ne. Kuma da alkawarin Allah ku cika. wannan ne Ya yi muku wasiyya da shi: Tsammãninku, kunã tunãwa.Al-an'am: 151-152Allah Madaukakin Sarki ya ce:Ka ce: "Abin sani kawai, Ubangijina Yã hana abũbuwanalfãsha; abin da ya bayyana daga gare su da abin da ya ɓõyu, da zunubi da rarraba jama'a, bã da wani hakki ba, kuma da ku yi shirki da Allah ga abin da bai saukar da wani dalĩli ba gare shi, kuma da ku faɗi abin da ba ku sani ba, ga Allah."Al-a'araf: 33kuma Musulunci ya Haramta Kashe Rai da baiyi laifin komai ba Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma kada ku kashe rai wanda Allah Ya haramta fãce da haƙƙi, kuma wanda aka kashe, yanã wanda aka zãlunta to, haƙĩƙa Mun sanya hujja ga waliyyinsa, sai dai kada ya ƙẽtare haddi a cikin kashẽwar. Lalle shĩ ya kasance wanda ake taimako.Al-Israa: 33Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma waɗanda bã su kiran wani ubangiji tãre da Allah, kuma bã su kashe rai wanda Allah Ya haramta fãce da hakki kuma bã su yin zina. Kuma wanda ya aikata wancan, zai gamu da laifuffuka,Al-Furqan: 68kuma Musulunci ya Haramta Varna a bayan Qasa Allah Maxaukakin Sarki ya ce:"Kuma kada kuyi Varna a bayan Qasa bayan ai gyara ta"Al-a'araf: 58Kuma Alla Maxaukakin Sarki ya ce game da Annabi Shu'abu -Amincin Allah a gare shi- cewa ya ce da Mutanensa:Kuma zuwa Madayana ɗan'uwansu Shu'aibu, ya ce: "Ya mutãnena! Ku bauta wa Allah; bã ku da wani abin bauta wa waninSa. Lalle ne, wata hujja bayyananniya daga Ubangijinku tã zõ muku! Sai ku cika mũdu da sikeli kumakada ku nakasa wa mutãne kãyansu, kuma kada ku yi fasãdi a cikin ƙasa a bãyan gyaranta. Wannan ne mafi alhẽri a gare ku, idan kun kasance mũminai."Al-a'araf: 85Kuma Allah ya Haramta Sihiri Allah Maxaukakin Sarki ya ce:"Kuma ka jẽfa abin da ke a cikin hannun dãmanka, ta cafe abin da suka aikata. Lalle ne abin da suka aikata mãkircin masihirci ne kuma masihirci bã ya cin nasara a duk inda ya je."Taha: 69Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:Ku guji abubuwa bakwai masu halakarwa suka ce ya Ma'aikin Allah! wadanne ne su? ya ce: Yin shirka da Allah, da sihiri, da kashe rai wacce Allah ya haramta face da gaskiya, da cin riba, da cin dukiyar maraya, da juyawa ranar yaki, da kuma yiwa katangaggiya marafkaniya mumina kazafiSahih Al-Bukhari: 6583Kuma Musulunci ya haramta Alfasha ta fili da voye da Zina da Luwaxi kuma ya gabata a cikin farkon wannan lokaci ya faxi dalilai akan hakan kuma Musulun ya haramta Riba Allah Maxaukaki ya ce:Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku bi Allah da taƙawa kuma ku bar abin da ya rage daga riba, idan kun kasance mãsu ĩmãni.(278)To, idan ba ku aikata ba to, ku sani fa da akwai yãƙi daga Allah da ManzonSa. Kuma idan kun tũba to kuna da asalin dũkiyõyinku, bã ku zãlunta, kuma bã a zãluntar ku.(279)Al-Baqara: 278-279Kuma Allah bai tsawatar da Mai Savo ba da Yaqi kamar yadda ya tsawatar da Ma'abocin Riba; saboda a cikin Riba akawai ruguza Addinai da Qasashe da dukiyoyi da KawunaKuma Musulunci ya haramta cin Mushe da abunda aka yanka ga Gumaka da Dodanni kuma ya haramta naman Alade Allah Maxaukaki ya ce:{An haramta muku mũshe da jini da nãman alade da abin da aka ambaci sũnan wanin Allah a gare shi, da mãƙararriya da jefaffiya da mai gangarõwa da sõkakkiya, da abin da mãsu dãgi suka ci, fãce abin da kuka yanka}.[Al-Maa'ida: 3].Kuma Musulunci ya haramta Sha giya da sauran Najasosi da Munanan abubuwa Allah Maxaukaki ya ce:Ya ku waɗanda suka yi ĩmãni! Abin sani kawai, giya da cãca da refu da kiban ƙuri'a, ƙazanta ne daga aikin shaiɗan, sai ku nĩsance shi, wa la'alla ku ci nasara.(90)Abin sani kawaĩ Shaiɗan yanã nufin ya aukar da adãwa da ƙeta a tsakãninku, a cikin giya da cãca, kuma ya kange ku daga ambaton Allah, kuma daga sallah. To, shin, ku mãsu hanuwa ne?(91)Al-Ma'ida: 90-91Kuma ya gabata a cikin sakin layi mai lamba ta (31) bayanin labarin Allah SWT cewa daga cikin siffofin Manzon Allah SAW a cikin Al-taura cewa shi ya ya haramta Munanan Abubuwa Allah Maxaukaki ya ce:Waɗanda suke sunã bin Manzo, Annabi, Ummiyyi wanda suke sãmun sa rubũce a wurinsu, a cikin Attaura da Linjĩla.yanã umurnin su da alhẽri, kuma yana hana su daga barin abin da bã a so; kuma yana halatta musu abũ- buwa masu dadi, kuma yana haramtarwar mũnana a kansu. Kuma yanã kãyar da nauyinsu daga barinsu, da ƙuƙummai waɗannan da suka kasance a kansu.Al-a'araf: 157:kuma Musulunci ya Haramta cinye Dukiyar Maraya Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma ku bai wa marãyu dũkiyõyinsu, kuma kada ku musanya mummuna da mai kyau. Kuma kada ku ci dũkiyõyinsu zuwa ga dũkiyõyinku. Lalle shi, yã kasance zunubi ne mai girma.Al-Nisa'a: 2Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Lalle ne, waɗanda suke cĩn dũkiyar marãyu da zãlunci, to, wuta kawai suke ci a cikin cikkunansu, kuma za su shiga cikin wata wuta mai tsanani.Al-nisa'a: 10kuma Musulunci ya Haramta Tauye Mudu Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Bone ya tabbata ga Masu tauye Mudu (1)Waɗanda suke idan suka auna daga mutãne suna cika mũdu.(2)Kuma idan sun auna musu da zakka ko da sikẽli, suna ragẽwa(3)Ashe! Waɗancan bã su tabbata cẽwa lalle sũ, ana tãyar da su ba?(4)Al-Muxaffifin: 1-4kuma Musulunci ya haramta yanke zumunci kuma ya gabata a sakin layi mai lamba (31) faxin Ayoyi da hadisai waxan da suke nuni kan hakan, Kuma baki xayan Annabawa da Manzanni -Amincin Allah a garesu- baki xayan su sun haxu kan haramcin waxan nan haramtattun abubuwan 35. Musulunci ya hana Munanan Halaye Kamar Qarya da Ha'inci da Yaudara da Ha'inci da Danfara, da Hassada da Mummunan kaidi da Sata da Zalunci, kuma ya na hana dukkan wani Mummunan HaliMusulunci ya na hana Munanan Ayyuka baki xaya Allah Maxaukaki ya ce:"Kada ka karkatar da kundukukinka ga mutãne, kada ka yi tafiya a cikin ƙasã kanã mai nũna fãɗin rai. Lalle, Allah bã Ya son dukan mai tãƙama, mai alfahari."Luqman:18Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce"Lallai wanda ya fiku soyuwa a gare ni kuma mafi kusancinku Mazauni a ranar Al-kiyama mafi kyawunku halayya, kuma mafi qinku a gare ni, kuma mafi nisanku dani a wajen zama a ranar Al-qiyama Masu surutu da Masu tsanantawa da Masu girman kai suka ce ya Manzon Allah haqiqa munsan Masu surutu da masu tsanantawa to su waye Masujiji da kai ya ce: Masu girman kai"Al-silsila Al-Sahiha: 791Musulunci yana hani daga Qarya Allah Maxaukakin Sarki ya ce:"Lallai Allah baya shiryar da wanda yake Mai varna kuma Mai yawan Qarya"Ghafir: 28Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"na hane ku da bari qarya saboda qarya tana shiryarwa zuwa fajirci, kuma lallai fajirci yana shiryarwa zuwa Wuta kuma Mutum ba zai gushe ba yana yin gaskiyaQarya kuma yana kirdadonta har sai Allah ya rubuta shi a wajensa Maqaryaci"Sahih Muslim: 2607Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Alamomin Munafuki Uku ne: Idan yai zance sai yayi qarya, kuma idan yayi Al-qawari sai ya sava, kuma idan aka amince masa sai yayi ha'inci"Sahih Al-Bukhari: 6095"Musulunci yana hana Al-gus"Kuma ya zo a cikin Hadisi cewa Manzon Allah SAW ya wuce a wata shinfixar Abinci sai ya shigar da Hannunsa a cikinta sai ya ji Danshi sai ya ce: "Maye haka ya kai Mai Wannan Abinci?" sai ya ce: Ruwan Sama ne ya same shi ya Manzon Allah sai ya ce: to ba sai kasanya shi ba a saman Abincin don Mutane su gani to duk wanda ya ha'ince mu to baya tare da ni"Sahih Muslim: 102Musulunci yana hani daga yaudara da ha'inci Allah Maxaukaki ya ce:Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku yaudari Allah da ManzonSa, kuma ku yaudari amãnõninku, alhãli kuwa kunã sane.Al-anfal: 27kuma Allah Maxaukaki ya ceSũ ne waɗanda suke cikãwa da alkawarin Allah, kuma bã su warware alkawari.Al-ra'ad: 20"Manzon Allah -tsira da amincin Allah- ya kasance yana cewa da Rundunarsa idan suka futo:"Kuyi yaqi kada kuyi Azarvavi kuma kuyi yaudara kada kuyi Musla kuma kada ku kashe Yaro"Sahih Muslim: 1731Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Abubuwa guda Huxu duk wanda ya kasance a cikinsu ya zamano Munafuki tsantsa kuma duk wanda yake yana da wani Hali daga cikinsu to ya kasance yana da wani abu daga cikin Munafunci har sai ya barshi idan aka Amince masa sai yayi Ha'inci kuma idan yayi zance sai yayi Qarya, kuma idan yayi Al-qawari sai sai yayi Yaudara, kuma idan aka yi faxa da shi sai yayi fajirci"Sahih Al-Bukhari: 34Musulunci yana hani daga Hassada Allah Maxauakaki ya ce:Ko suna hãsadar mutãne ne a kan abin da Allah Ya bã su daga falalarSa? To, lalle ne, Mun bai wa gidan Ibrãhĩm Littãfida hikima kuma Mun bã su mulki mai girma.Al-nisa'a: 54Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Mãsu yawa daga Ma'abuta Littãfi sunã gũrin dã sun mayar da ku, daga bãyan ĩmãninku, kãfirai, sabõda hãsada daga wurin rãyukansu, daga bayãn gaskiya tã bayyana a gare su. To, ku yãfe, kuma ku kau da kai, sai Allah Yã zo da umurninSa. Lalle ne Allah a kan dukkan kõme Mai ĩkon yi ne.Al-Baqara: 109Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Cutar Al-umman da suka gabace ku ya shigo ku Hassada da Qeta ita ce mai Askewa ba ina nufin mai Aske gashin kai ba, sai dai tana Aske Addni Na rantse da wanda raina yake Hannunsa ba zaku tava shiga Al-janna ba har sai kunyi Imani kuma ba zaku tava yin Imani ba har sai kun so junanku kuma bana baku labarin abunda zai tabbatar muku da wancan xin ba? to ku yaxa Sallama a tsakaninku"Sunan Al-tirmizi: 2510Musulunci yana hani dagaMummunan qulli Allah Maxaukaki ya ce:Kuma kamar wancan ne Mun sanya a cikin kõwace alƙarya, shugabanni sũ ne mãsu laifinta dõmin su yi mãkirci a cikinta, alhãli kuwa ba su yin makirci fãce ga rayukansu, kuma ba su sansancẽwa.Al-an'am: 123Kuma Allah ya bada labarin cewa Yahudawa sunyi niyyar Kashe Annabi Isa -Amincin Allah a gare shi- kuma sunyi Makirci sai dai Allah ya Mayar musu da Makircinsu kuma Allah ya bayya cewa Mummunan Makirci baya faxawa ko ina sai ga Mai shi Allah Maxaukaki ya ce:To, a lõkacin da Ĩsa ya gane kãfirci daga gare su, sai ya ce: "Su wãne ne mataimakãna zuwa ga Allah?" Hawãriyãwa suka ce: "Mu ne mataimakan Allah. Mun yi ĩmani da Allah. Kuma ka shaida cẽwa lalle ne mu, mãsu sallamãwa ne."Yã Ubangijinmu! Mun yi imãni da abin da Ka saukar, kuma mun bi ManzonKa, sai Ka rubũta mu tãre da mãsu shaida.(53)Kuma (Kãfirai) suka yi mãkirci, Allah kuma Ya yi musu (sakamakon) makircin, kuma Allah ne Mafi alhẽrin mãsu sãka wamãkirci (34)A lõkacin da Ubangiji Ya ce: "Ya Ĩsa! Lalle NĨ Mai karɓar ranka ne, kuma Mai ɗauke ka ne zuwa gare Ni, kuma Mai tsarkake ka daga waɗanda suka kãfirta, kuma Mai sanya waɗanda suka bĩ ka a bisa waɗanda suka kãfirta har Rãnar ¡iyãma. Sa'an nan kuma zuwa gare Ni makõmarku take, sa'an nan in yi hukunci a tsakãninku, a cikin abin da kuka kasance kuna sãɓã wa jũna.(55)Ali Imran: 52-56Kuma Allah Maxaukaki ya bada labarin cewa Mutanen Annabi Salih -Amincin Allah a gare shi- sunyi nufin kashe shi da Makirci sai sukai mugun shiri sai Allah ya Mayar musu da Makircinsu, kuma ya Ruguzasu da Mutanensu baki xaya, Allah Maxaukaki ya ce:Kuma suka ƙulla mãkirci, kuma Muka ƙulla sakamakon mãkirci, alhãli sũ ba su sani ba.(49)Ka dũba yadda ãƙibar mãkircinsu ta kasance lalle Mũ Mun darkãke su da mutãnensu, gabã ɗaya.(50)Waɗancan, gidãjensu ne, wõfintattu sabõda zãluncin da suka yi, lalle ne a wancan akwai ãyã ga mutãne waɗanda suke sani.(51)Al-naml: 49-51Musulunci yana hani da sata Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi-ya ce:"Mai Zina ba zai tava yin Zina ba a halin yana Mumini, haka Varawo bazai Sata ba lokacin da yake sata yana Mumini kuma Mashayin giya ba zai sha ba a halin yana Mumini kuma tuba yana nan dai"Sahih Al-Bukhari: 6810Musulunci yana hani daga Varna Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi-ya ce:Lalle Allah nã yin umurni da ãdalci da kyautatãwa, da bai wa ma'abũcin zumunta, kuma yanã hani ga alfãsha da abin da aka ƙi da rarrabe jama'a. Yanã yi muku gargaɗi, ɗammãnin ku, kunã tunãwa.Al-Nahl: 90Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:Lallai Allah Madaukakin Sarki yayi mun wahayi cewa ku Kaskantar da kanku, ha yadda babu wani da zai yi alunci kan wani, kuma kada daya ya yi fariya akan waniSahihu Abu daud: 4895Musulunci yana hani daga Zalunci Allah Maxaukakin Sarki ya ce:"Kuma Allah baya son Al-zalumai"Aal Imran: 57kuma Allah Maxaukaki ya ce"Lallai Al-zalumai basa rabauta"Al-an'am: 21kuma Allah Maxaukaki ya ce"Kuma Al-zalumai ya tanadar musu Azaba Mai raxaxi"Aj-Insan: 31Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Mutane uku ba'a Mayar da Adddu'arsu: Shugaba Adali da mai Azumi har sai ya sha ruwa da Addu'ar wanda aka Zalunta ka xorata akan girgije kuma a buxe mata qofofin Sammai kuma yace Ya Ubangiji na rantse da Girmana zan taimakeka koda kuwa bayan Zamani ne"Muslim ne ya rawaito shi (2749) a takaice da xan savani kaxan, da kuma Tirmizi (2526) da xan savani kaxan, kuma Ahmad (8043) kuma lafazin nasa neKuma yayin da Manzo SAW ya tura Mu'az zuwa Yeman ya na mai kira zuwa Musulunci sai ya ce da shi:"Kaji tsoron Addu'ar wanda aka Zalunta saboda cewa ita babai wani Hijabi tsakaninta da Allah"Sahih Al-Bukhari: 1496Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"ku saurara duk wanda ya zalunci Kafirin Amana ko ya Wulaqanta shi ko ya xora masaabunda ya fiqarfinsa ko ya karvi wani abu da da yardar sa ba to nine zan tsaya in yi jayayya da shi a Ranar al-qiyama"Sunan Abi Daud 3052Saboda Musulunci kamar yadda ka gani yana hana kowace irin Mummunan hali ko Mu'amala ta Zalunci ko ta Cuta"Kada ka karkatar da kundukukinka ga mutãne, kada ka yi tafiya a cikin ƙasã kanã mai nũna fãɗin rai. Lalle, Allah bã Ya son dukan mai tãƙama, mai alfahari."Luqman:18Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce"Lallai wanda ya fiku soyuwa a gare ni kuma mafi kusancinku Mazauni a ranar Al-kiyama mafi kyawunku halayya, kuma mafi qinku a gare ni, kuma mafi nisanku dani a wajen zama a ranar Al-qiyama Masu surutu da Masu tsanantawa da Masu girman kai suka ce ya Manzon Allah haqiqa munsan Masu surutu da masu tsanantawa to su waye Masujiji da kai ya ce: Masu girman kai"Al-silsila Al-Sahiha: 791Musulunci yana hani daga Qarya Allah Maxaukakin Sarki ya ce:"Lallai Allah baya shiryar da wanda yake Mai varna kuma Mai yawan Qarya"Ghafir: 28Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"na hane ku da bari qarya saboda qarya tana shiryarwa zuwa fajirci, kuma lallai fajirci yana shiryarwa zuwa Wuta kuma Mutum ba zai gushe ba yana yin gaskiyaQarya kuma yana kirdadonta har sai Allah ya rubuta shi a wajensa Maqaryaci"Sahih Muslim: 2607Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Alamomin Munafuki Uku ne: Idan yai zance sai yayi qarya, kuma idan yayi Al-qawari sai ya sava, kuma idan aka amince masa sai yayi ha'inci"Sahih Al-Bukhari: 6095"Musulunci yana hana Al-gus"Kuma ya zo a cikin Hadisi cewa Manzon Allah SAW ya wuce a wata shinfixar Abinci sai ya shigar da Hannunsa a cikinta sai ya ji Danshi sai ya ce: "Maye haka ya kai Mai Wannan Abinci?" sai ya ce: Ruwan Sama ne ya same shi ya Manzon Allah sai ya ce: to ba sai kasanya shi ba a saman Abincin don Mutane su gani to duk wanda ya ha'ince mu to baya tare da ni"Sahih Muslim: 102Musulunci yana hani daga yaudara da ha'inci Allah Maxaukaki ya ce:Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku yaudari Allah da ManzonSa, kuma ku yaudari amãnõninku, alhãli kuwa kunã sane.Al-anfal: 27kuma Allah Maxaukaki ya ceSũ ne waɗanda suke cikãwa da alkawarin Allah, kuma bã su warware alkawari.Al-ra'ad: 20"Manzon Allah -tsira da amincin Allah- ya kasance yana cewa da Rundunarsa idan suka futo:"Kuyi yaqi kada kuyi Azarvavi kuma kuyi yaudara kada kuyi Musla kuma kada ku kashe Yaro"Sahih Muslim: 1731Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Abubuwa guda Huxu duk wanda ya kasance a cikinsu ya zamano Munafuki tsantsa kuma duk wanda yake yana da wani Hali daga cikinsu to ya kasance yana da wani abu daga cikin Munafunci har sai ya barshi idan aka Amince masa sai yayi Ha'inci kuma idan yayi zance sai yayi Qarya, kuma idan yayi Al-qawari sai sai yayi Yaudara, kuma idan aka yi faxa da shi sai yayi fajirci"Sahih Al-Bukhari: 34Musulunci yana hani daga Hassada Allah Maxauakaki ya ce:Ko suna hãsadar mutãne ne a kan abin da Allah Ya bã su daga falalarSa? To, lalle ne, Mun bai wa gidan Ibrãhĩm Littãfida hikima kuma Mun bã su mulki mai girma.Al-nisa'a: 54Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Mãsu yawa daga Ma'abuta Littãfi sunã gũrin dã sun mayar da ku, daga bãyan ĩmãninku, kãfirai, sabõda hãsada daga wurin rãyukansu, daga bayãn gaskiya tã bayyana a gare su. To, ku yãfe, kuma ku kau da kai, sai Allah Yã zo da umurninSa. Lalle ne Allah a kan dukkan kõme Mai ĩkon yi ne.Al-Baqara: 109Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Cutar Al-umman da suka gabace ku ya shigo ku Hassada da Qeta ita ce mai Askewa ba ina nufin mai Aske gashin kai ba, sai dai tana Aske Addni Na rantse da wanda raina yake Hannunsa ba zaku tava shiga Al-janna ba har sai kunyi Imani kuma ba zaku tava yin Imani ba har sai kun so junanku kuma bana baku labarin abunda zai tabbatar muku da wancan xin ba? to ku yaxa Sallama a tsakaninku"Sunan Al-tirmizi: 2510Musulunci yana hani dagaMummunan qulli Allah Maxaukaki ya ce:Kuma kamar wancan ne Mun sanya a cikin kõwace alƙarya, shugabanni sũ ne mãsu laifinta dõmin su yi mãkirci a cikinta, alhãli kuwa ba su yin makirci fãce ga rayukansu, kuma ba su sansancẽwa.Al-an'am: 123Kuma Allah ya bada labarin cewa Yahudawa sunyi niyyar Kashe Annabi Isa -Amincin Allah a gare shi- kuma sunyi Makirci sai dai Allah ya Mayar musu da Makircinsu kuma Allah ya bayya cewa Mummunan Makirci baya faxawa ko ina sai ga Mai shi Allah Maxaukaki ya ce:To, a lõkacin da Ĩsa ya gane kãfirci daga gare su, sai ya ce: "Su wãne ne mataimakãna zuwa ga Allah?" Hawãriyãwa suka ce: "Mu ne mataimakan Allah. Mun yi ĩmani da Allah. Kuma ka shaida cẽwa lalle ne mu, mãsu sallamãwa ne."Yã Ubangijinmu! Mun yi imãni da abin da Ka saukar, kuma mun bi ManzonKa, sai Ka rubũta mu tãre da mãsu shaida.(53)Kuma (Kãfirai) suka yi mãkirci, Allah kuma Ya yi musu (sakamakon) makircin, kuma Allah ne Mafi alhẽrin mãsu sãka wamãkirci (34)A lõkacin da Ubangiji Ya ce: "Ya Ĩsa! Lalle NĨ Mai karɓar ranka ne, kuma Mai ɗauke ka ne zuwa gare Ni, kuma Mai tsarkake ka daga waɗanda suka kãfirta, kuma Mai sanya waɗanda suka bĩ ka a bisa waɗanda suka kãfirta har Rãnar ¡iyãma. Sa'an nan kuma zuwa gare Ni makõmarku take, sa'an nan in yi hukunci a tsakãninku, a cikin abin da kuka kasance kuna sãɓã wa jũna.(55)Ali Imran: 52-56Kuma Allah Maxaukaki ya bada labarin cewa Mutanen Annabi Salih -Amincin Allah a gare shi- sunyi nufin kashe shi da Makirci sai sukai mugun shiri sai Allah ya Mayar musu da Makircinsu, kuma ya Ruguzasu da Mutanensu baki xaya, Allah Maxaukaki ya ce:Kuma suka ƙulla mãkirci, kuma Muka ƙulla sakamakon mãkirci, alhãli sũ ba su sani ba.(49)Ka dũba yadda ãƙibar mãkircinsu ta kasance lalle Mũ Mun darkãke su da mutãnensu, gabã ɗaya.(50)Waɗancan, gidãjensu ne, wõfintattu sabõda zãluncin da suka yi, lalle ne a wancan akwai ãyã ga mutãne waɗanda suke sani.(51)Al-naml: 49-51Musulunci yana hani da sata Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi-ya ce:"Mai Zina ba zai tava yin Zina ba a halin yana Mumini, haka Varawo bazai Sata ba lokacin da yake sata yana Mumini kuma Mashayin giya ba zai sha ba a halin yana Mumini kuma tuba yana nan dai"Sahih Al-Bukhari: 6810Musulunci yana hani daga Varna Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi-ya ce:Lalle Allah nã yin umurni da ãdalci da kyautatãwa, da bai wa ma'abũcin zumunta, kuma yanã hani ga alfãsha da abin da aka ƙi da rarrabe jama'a. Yanã yi muku gargaɗi, ɗammãnin ku, kunã tunãwa.Al-Nahl: 90Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:Lallai Allah Madaukakin Sarki yayi mun wahayi cewa ku Kaskantar da kanku, ha yadda babu wani da zai yi alunci kan wani, kuma kada daya ya yi fariya akan waniSahihu Abu daud: 4895Musulunci yana hani daga Zalunci Allah Maxaukakin Sarki ya ce:"Kuma Allah baya son Al-zalumai"Aal Imran: 57kuma Allah Maxaukaki ya ce"Lallai Al-zalumai basa rabauta"Al-an'am: 21kuma Allah Maxaukaki ya ce"Kuma Al-zalumai ya tanadar musu Azaba Mai raxaxi"Aj-Insan: 31Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Mutane uku ba'a Mayar da Adddu'arsu: Shugaba Adali da mai Azumi har sai ya sha ruwa da Addu'ar wanda aka Zalunta ka xorata akan girgije kuma a buxe mata qofofin Sammai kuma yace Ya Ubangiji na rantse da Girmana zan taimakeka koda kuwa bayan Zamani ne"Muslim ne ya rawaito shi (2749) a takaice da xan savani kaxan, da kuma Tirmizi (2526) da xan savani kaxan, kuma Ahmad (8043) kuma lafazin nasa neKuma yayin da Manzo SAW ya tura Mu'az zuwa Yeman ya na mai kira zuwa Musulunci sai ya ce da shi:"Kaji tsoron Addu'ar wanda aka Zalunta saboda cewa ita babai wani Hijabi tsakaninta da Allah"Sahih Al-Bukhari: 1496Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"ku saurara duk wanda ya zalunci Kafirin Amana ko ya Wulaqanta shi ko ya xora masaabunda ya fiqarfinsa ko ya karvi wani abu da da yardar sa ba to nine zan tsaya in yi jayayya da shi a Ranar al-qiyama"Sunan Abi Daud 3052Saboda Musulunci kamar yadda ka gani yana hana kowace irin Mummunan hali ko Mu'amala ta Zalunci ko ta Cuta 36. Musulunci ya hana Muna nan Mua'amalolin kuxi waxanda cikinsu akwai riba ko cutarwa ko kuma garari ko zalunci ko Al-gus, ko kuma yana kaiwa zuwa ga Masifu, ko Cutarwa da zata game baki xayan Kasashe da kuma Mutane da xaixaikuMusulunci ya hana Muna nan Mua'amalolin kuxi waxanda cikinsu akwai riba ko cutarwa ko kuma garari ko zalunci ko Al-gus, ko kuma yana kaiwa zuwa ga Masifu, ko Cutarwa da zata game baki xayan Kasashe da kuma Mutane da xaixaikuKuma ya gabata a cikin farkon sakin layi da aka faxi Ayoyi da Hadisan da aka haramta Riba ko Zalunci ko Ha'inci ko Varna a bayan Qasa Allah Maxaukaki ya ce:Kuma waɗanda suke cũtar mũminai maza dã muminai mãtã, bã da wani abu da suka aikata ba to, lalle sun ɗauki ƙiren ƙarya da zunubi bayyananne.Al-Ahzab: 58Allah Madaukakin Sarki ya ce:Wanda ya aikata aiki na ƙwarai to sabõda kansa ne, kuma wanda ya mũnanã, to, yanã akansa. Kuma Ubangiwinka, bã Mai zãlunci ga bãyinSa ne ba.Fussilat: 46Kuma ya zo a cikin Sunna: "Cewa Manzon Allah SAW yayi hukunci cewa babu cuta babu cutarwa"Sunan Abi DaudAnnabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:Duk wanda yai Imani da Allah da Ranar lahira to ya fadi Alkairi ko yayi shiru, kuma duk wanda yayi Imani da Allah da Ranar Lahira to ta girmama Makwabcinsa,kuma duk wanda yayi Imani da Allah da Ranar Lahira to ta girmama to ya girmama BakonsaSahih Muslim: 47Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Anyiwa wata Mata Azaba saboda Mage da ta kulle har ta Mutu saboda ita aka saka ta a cikin Wuta ita bata bata Abinci ba ko Ruwa ita kuma bata barta ba ta tafi taci kwarin bayan Qasa"Sahih Al-Bukhari: 3482Wannan fa ga wanda ya xutar da Mage ne to mai kake zaton wanda yake cutar da Mutane, saboda an rawaito daga Xan Umar ya ce: Manzon ALlah SAW ya hau Munbari sai yai kira da murya mai qarfi kuma ya ce:" Ya ku jama'ar da suka Musulunta da harshen su kuma Imani bai shiga Zuciyarsu ba kada ku cutar da Musulmai kuma kada ku aibatasu kuma kada ku bibiyi Al-aurarsu saboda duk wanda yabi Al-aurar wani Xan Uwansa Musulmi to Allah zai bibiyi Al-aurarsa Kuma duk wanda Allah ya bi Al-aurarsa sai ya kunyata, ko da kuma yana cikin Mutanensa ne, ya ce: Kuma Ibn Umar wata Rana ya kalli Xakin Allah ko zuwa Ka'aba sai ya ce: Mai yafiki girma da Alfarma kuma Mumini shi ne mafi girmanki Alfarma a wajen Allah"Tirmizi ne ya rawaito shi (2032) da Ibn Hibban (5763)Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:Duk wanda yai Imani da Allah da Ranar lahira to ya fadi Alkairi ko yayi shiru, kuma duk wanda yayi Imani da Allah da Ranar Lahira to ta girmama Makwabcinsa,kuma duk wanda yayi Imani da Allah da Ranar Lahira to ta girmama to ya girmama BakonsaSahih Al-Bukhari: 6018An karvo daga Abu Huraira daga manzon Allah SAW ya ce: "Shin kunsan wane ne Tozartacce? Suka ce Tozartacce a cikin mu shi ne wanda bashi ko kwabo kuma bashi da kaya, sai ya ce: "Lallai Tozartacce daga cikin Al-umma ta wanda ya zo a Ranar Al-qiyama da azumi da sallah da Zakka kuma yazo ahalin ya zagi wancan yayiwa wancan qazafi kuma yaci kuxin wancan sai a zaunar da shi sai a xauka daga kyawawan Ayyukansa idan suka qare kafin abiya abunda yake kansa sai a xebo zunubansu sai lafta masa sannan a jefa shi cikin Wuta"Muslim ne ya rawaito shi (2581) da kuma Tirmi zi (2418) da Ahmad (8029) kuma lafazin nasa neManzon Allah ya ce:"Ya kasance akan hayar akwai wani reshe da yake cutar da Mutane sai ya kawar da shi sai Allah ya sa shi a Al-janna"Bukahri ne ya rawaito shi (652) da Ma'anarsa da Muslim (1914) kwatankwacinsa, da Ibn Majah (3682) da Ahmad (10432) kuma Lafazin Nasu ne, saboda kawar da cuta akan Hanya yana sa a shiga Al-janna to yaya kuma wanda yake cutar da Mutane kuma yake vata Rayuwarsu?Kuma ya gabata a cikin farkon sakin layi da aka faxi Ayoyi da Hadisan da aka haramta Riba ko Zalunci ko Ha'inci ko Varna a bayan Qasa Allah Maxaukaki ya ce:Kuma waɗanda suke cũtar mũminai maza dã muminai mãtã, bã da wani abu da suka aikata ba to, lalle sun ɗauki ƙiren ƙarya da zunubi bayyananne.Al-Ahzab: 58Allah Madaukakin Sarki ya ce:Wanda ya aikata aiki na ƙwarai to sabõda kansa ne, kuma wanda ya mũnanã, to, yanã akansa. Kuma Ubangiwinka, bã Mai zãlunci ga bãyinSa ne ba.Fussilat: 46Kuma ya zo a cikin Sunna: "Cewa Manzon Allah SAW yayi hukunci cewa babu cuta babu cutarwa"Sunan Abi DaudAnnabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:Duk wanda yai Imani da Allah da Ranar lahira to ya fadi Alkairi ko yayi shiru, kuma duk wanda yayi Imani da Allah da Ranar Lahira to ta girmama Makwabcinsa,kuma duk wanda yayi Imani da Allah da Ranar Lahira to ta girmama to ya girmama BakonsaSahih Muslim: 47Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Anyiwa wata Mata Azaba saboda Mage da ta kulle har ta Mutu saboda ita aka saka ta a cikin Wuta ita bata bata Abinci ba ko Ruwa ita kuma bata barta ba ta tafi taci kwarin bayan Qasa"Sahih Al-Bukhari: 3482Wannan fa ga wanda ya xutar da Mage ne to mai kake zaton wanda yake cutar da Mutane, saboda an rawaito daga Xan Umar ya ce: Manzon ALlah SAW ya hau Munbari sai yai kira da murya mai qarfi kuma ya ce:" Ya ku jama'ar da suka Musulunta da harshen su kuma Imani bai shiga Zuciyarsu ba kada ku cutar da Musulmai kuma kada ku aibatasu kuma kada ku bibiyi Al-aurarsu saboda duk wanda yabi Al-aurar wani Xan Uwansa Musulmi to Allah zai bibiyi Al-aurarsa Kuma duk wanda Allah ya bi Al-aurarsa sai ya kunyata, ko da kuma yana cikin Mutanensa ne, ya ce: Kuma Ibn Umar wata Rana ya kalli Xakin Allah ko zuwa Ka'aba sai ya ce: Mai yafiki girma da Alfarma kuma Mumini shi ne mafi girmanki Alfarma a wajen Allah"Tirmizi ne ya rawaito shi (2032) da Ibn Hibban (5763)Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:Duk wanda yai Imani da Allah da Ranar lahira to ya fadi Alkairi ko yayi shiru, kuma duk wanda yayi Imani da Allah da Ranar Lahira to ta girmama Makwabcinsa,kuma duk wanda yayi Imani da Allah da Ranar Lahira to ta girmama to ya girmama BakonsaSahih Al-Bukhari: 6018An karvo daga Abu Huraira daga manzon Allah SAW ya ce: "Shin kunsan wane ne Tozartacce? Suka ce Tozartacce a cikin mu shi ne wanda bashi ko kwabo kuma bashi da kaya, sai ya ce: "Lallai Tozartacce daga cikin Al-umma ta wanda ya zo a Ranar Al-qiyama da azumi da sallah da Zakka kuma yazo ahalin ya zagi wancan yayiwa wancan qazafi kuma yaci kuxin wancan sai a zaunar da shi sai a xauka daga kyawawan Ayyukansa idan suka qare kafin abiya abunda yake kansa sai a xebo zunubansu sai lafta masa sannan a jefa shi cikin Wuta"Muslim ne ya rawaito shi (2581) da kuma Tirmi zi (2418) da Ahmad (8029) kuma lafazin nasa neManzon Allah ya ce:"Ya kasance akan hayar akwai wani reshe da yake cutar da Mutane sai ya kawar da shi sai Allah ya sa shi a Al-janna"Bukahri ne ya rawaito shi (652) da Ma'anarsa da Muslim (1914) kwatankwacinsa, da Ibn Majah (3682) da Ahmad (10432) kuma Lafazin Nasu ne, saboda kawar da cuta akan Hanya yana sa a shiga Al-janna to yaya kuma wanda yake cutar da Mutane kuma yake vata Rayuwarsu? 37. Musulunci ya zo da kiyaye Hankula da Haramta dukkan abunda zai vata shi kamar Shan Giya, kuma Musulunci ya xaga Darajar Hankali kuma ya sanya shi doron dora nauyi, kuma ya 'Yantashi daga dabaibayin Taysuniyoyo da bautar gumaka kuma a Musulunci babu wasu Voyayyun abubuwa ko hukunce Hukunce da suka kevanci Wasu Mutane koma bayan Wasu, kuma baki xayan hukunce Hukuncen sa da Shari'unsa sunyi daidai da hankula Ingantattu, kuma ita ce daidai da Adalci da HikimaMusulunci ya zo da kiyaye Hankali kuma ya xaga Darajarsa Allah Maxaukaki ya ce:"Lallai ji da Gani da Zuciya dukkan waxancan sun kasance ababan tambaya"Al-Isra'a: 36To ya Wajaba akan Mutum ya kiyaye Hankalinsa saboda haka Musulunci ya haramta giya da ababan Maye, kuma an faxi haramcin giya a sakin layi na (34) da kuma Ayoyin Al-qur'ani Masu yawa wacce ta qare da faxinsa Maxaukaki:"Ko kwayi hankali"Al-baqara: 242Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma rãyuwar dũniya ba ta zama ba, fãce wãsa da shagala, kuma lalle ne, Lãhira ce mafi alhẽri ga waɗanda suka yi taƙawa. Shin, ba za ku yi hankali ba?Al-an'am: 32Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Lalle ne Mũ, Mun saukar da shi, yanã abin karantãwa na Lãrabci; tsammãninkũ, kunã hankalta.Yusuf: 2Kuma Allah Maxaukaki yayi bayanin cewa Shiriya da Hikima ba'a anfanuwa da su sai ga Ma'abota Hankali su ne Ma'abota Hankali Allah Maxaukaki ya ce:Yana bãyar da hikima (ga fahimtar gaskiyar abubuwa) ga wanda Yake so. Kuma wanda aka bai wa hikima to lalle ne an bã shi alhẽri mai yawa. Kuma bãbu mai tunãni fãce ma'abuta hankula.Al-Baqara:269Saboda haka Musulunci ya sanya hankali Ma'aunin xora Doka Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi-ya ce:"An xauke Al-qalami ga Mutum Uku: Mai Bacci har sai ya farka da Yaro har sai ya Balaga, da Kuma Mahaukaci har sai ya Warke"Bukhari ne ya rawaito shi a matsayin Mua'allaqi da Sigar yankrwa kafin Hadisi na (5269) da makamancinsa kuma Abu daud ya futar da shi a mausuli (4402) kuma lafazin nasa ne, da tirmizi (1423) da nasa'i a cikin (Al-sunan Alkubra) (7346) da Ahmad (956) da savani kaxan, da Ibn Majah (2042) a taqaice.Kuma ya 'Yantasu daga sasarin tatsunuyoyi da gumaka Allah Maxaukaki ya ce yana bada labarin halin wasu Al-ummai wajen riqonsu da tastuniyoyi da kuma mayarwarsu da gaskioya wacce ta zo musu daga AllahKuma kamar haka, ba Mu aika wani mai gargaɗi ba a gabãninka, a cikin wata alƙarya, fãce mani'imtanta sun ce, "Lalle mũ, mun sãmi ubanninmu a kan wani addini kuma lalle mũ, mãsu kõyi ne a kan gurãbunsu."Al-zukhruf: 23Kuma Alla Maxaukakin Sarki ya ce game da Annabi Ibrahim -Amincin Allah a gare shi- cewa ya ce da Mutanensa:"Waxan nan waxanne Gumaka ne da kuke sunkuyawa" (52)Suka ce: "Mun sãmi Ubanninmu mãsu lazimta a kansu."(53)Al-anbiya: 52-53Sai Musulunci ya zo kuma ya umarci Mutane da barin bautar Gumaka da barin tatsuniyoyi waxanda suka gada daga Iyayensu da Kakanni da bin Hanyar Manzanni -Amincin Allah a gare su-kuma babu wasu sirruka a Musulunci ko Hukunce Hukunce da suka kevanci wasu mutane banda WasuAn Tamabyi Ali Bn Abi Xalib -Allah ya yarda da shi- kuma shi ne Xab baffan manzon Allah SAW kuma Mijin Xiyarsa: ko Manzon Allah ya kevance ku da wani? sai ya ce: "Manzon Allah SAW bai kevance mu da komai ba da bai game Mutane da shi ba bakio xaya sai abunda yakasance a cikin kuben tabona wannan, ya ce: sai ya futo da wata takarda a ruce a cikinta: Allah ya tsinewa duk wanda yayi yanka ga wanin Allah kuma Allah ya tsinewa Marar Qasa, kuma Allah ya tsinewa wanda ya la'anci Iyayensa, kuma Allah ya tsinewa duk wanda bada nafaka ga Xan Bidi'a"Sahih Muslim: 1978Kuma baki xayan Hukun Hukuncen Musulunci da Shari'unsa sunyi daidai da Lafiyayyun Hankula kuma sun daidai da abunda Adalci ya qunsa da Hikima"Lallai ji da Gani da Zuciya dukkan waxancan sun kasance ababan tambaya"Al-Isra'a: 36To ya Wajaba akan Mutum ya kiyaye Hankalinsa saboda haka Musulunci ya haramta giya da ababan Maye, kuma an faxi haramcin giya a sakin layi na (34) da kuma Ayoyin Al-qur'ani Masu yawa wacce ta qare da faxinsa Maxaukaki:"Ko kwayi hankali"Al-baqara: 242Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma rãyuwar dũniya ba ta zama ba, fãce wãsa da shagala, kuma lalle ne, Lãhira ce mafi alhẽri ga waɗanda suka yi taƙawa. Shin, ba za ku yi hankali ba?Al-an'am: 32Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Lalle ne Mũ, Mun saukar da shi, yanã abin karantãwa na Lãrabci; tsammãninkũ, kunã hankalta.Yusuf: 2Kuma Allah Maxaukaki yayi bayanin cewa Shiriya da Hikima ba'a anfanuwa da su sai ga Ma'abota Hankali su ne Ma'abota Hankali Allah Maxaukaki ya ce:Yana bãyar da hikima (ga fahimtar gaskiyar abubuwa) ga wanda Yake so. Kuma wanda aka bai wa hikima to lalle ne an bã shi alhẽri mai yawa. Kuma bãbu mai tunãni fãce ma'abuta hankula.Al-Baqara:269Saboda haka Musulunci ya sanya hankali Ma'aunin xora Doka Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi-ya ce:"An xauke Al-qalami ga Mutum Uku: Mai Bacci har sai ya farka da Yaro har sai ya Balaga, da Kuma Mahaukaci har sai ya Warke"Bukhari ne ya rawaito shi a matsayin Mua'allaqi da Sigar yankrwa kafin Hadisi na (5269) da makamancinsa kuma Abu daud ya futar da shi a mausuli (4402) kuma lafazin nasa ne, da tirmizi (1423) da nasa'i a cikin (Al-sunan Alkubra) (7346) da Ahmad (956) da savani kaxan, da Ibn Majah (2042) a taqaice.Kuma ya 'Yantasu daga sasarin tatsunuyoyi da gumaka Allah Maxaukaki ya ce yana bada labarin halin wasu Al-ummai wajen riqonsu da tastuniyoyi da kuma mayarwarsu da gaskioya wacce ta zo musu daga AllahKuma kamar haka, ba Mu aika wani mai gargaɗi ba a gabãninka, a cikin wata alƙarya, fãce mani'imtanta sun ce, "Lalle mũ, mun sãmi ubanninmu a kan wani addini kuma lalle mũ, mãsu kõyi ne a kan gurãbunsu."Al-zukhruf: 23Kuma Alla Maxaukakin Sarki ya ce game da Annabi Ibrahim -Amincin Allah a gare shi- cewa ya ce da Mutanensa:"Waxan nan waxanne Gumaka ne da kuke sunkuyawa" (52)Suka ce: "Mun sãmi Ubanninmu mãsu lazimta a kansu."(53)Al-anbiya: 52-53Sai Musulunci ya zo kuma ya umarci Mutane da barin bautar Gumaka da barin tatsuniyoyi waxanda suka gada daga Iyayensu da Kakanni da bin Hanyar Manzanni -Amincin Allah a gare su-kuma babu wasu sirruka a Musulunci ko Hukunce Hukunce da suka kevanci wasu mutane banda WasuAn Tamabyi Ali Bn Abi Xalib -Allah ya yarda da shi- kuma shi ne Xab baffan manzon Allah SAW kuma Mijin Xiyarsa: ko Manzon Allah ya kevance ku da wani? sai ya ce: "Manzon Allah SAW bai kevance mu da komai ba da bai game Mutane da shi ba bakio xaya sai abunda yakasance a cikin kuben tabona wannan, ya ce: sai ya futo da wata takarda a ruce a cikinta: Allah ya tsinewa duk wanda yayi yanka ga wanin Allah kuma Allah ya tsinewa Marar Qasa, kuma Allah ya tsinewa wanda ya la'anci Iyayensa, kuma Allah ya tsinewa duk wanda bada nafaka ga Xan Bidi'a"Sahih Muslim: 1978Kuma baki xayan Hukun Hukuncen Musulunci da Shari'unsa sunyi daidai da Lafiyayyun Hankula kuma sun daidai da abunda Adalci ya qunsa da Hikima 38. kuma Addinann Vata idan Mabiyansu basu gamsu da abunda yake cikinsu ba na kwangaba kwanbaya, da Al-amuran da hankali ba zai xauka ba sai Malaman Mabiya Addinin sai su ruxi Mabiyan da cewa ai Addini sama yake da Hankali. kuma cewa Hankali ai dole sai da shi wajen fahimtar Addini da kuma riqeshi wanda ko Musulunci ya sanya Hankali wani Haske ne da yake Haskawa Hankali Hanya; saboda Ma'abota Addinan Qarya sunason Mutum ne ya bar Hankalinsa ya bi su, kuma Musulunci yana son Mutum ne da ya farkar da hankalinsa, don yasan haqiqanin Al-amura kamar yadda yakekuma Addinann Vata idan Mabiyansu basu gamsu da abunda yake cikinsu ba na kwangaba kwanbaya, da Al-amuran da hankali ba zai xauka ba sai Malaman Mabiya Addinin sai su ruxi Mabiyan da cewa ai Addini sama yake da Hankali. kuma cewa Hankali ai dole sai da shi wajen fahimtar Addini da kuma riqeshi wanda ko Musulunci ya sanya Hankali wani Haske ne da yake Haskawa Hankali Hanya; saboda Ma'abota Addinan Qarya sunason Mutum ne ya bar Hankalinsa ya bi su, kuma Musulunci yana son Mutum ne da ya farkar da hankalinsa, don yasan haqiqanin Al-amura kamar yadda yakeKuma kamar wancan Mun aika wani rũhi (rai mai haɗa jama'a) zuwa gare ka, daga gare Mu. Ba ka kasance kã san abin da yake littãfi ba, kõ abin da Yake ĩmãni, kuma amma Mun sanya shi (rũhin, watau Alƙur'ãni) wani haske ne, Munã shiryar da wanda Muke so daga cikin bãyĩnMu game da shi. Kuma Lalle kai, haƙĩƙa, kanã shiryarwa zuwa ga hanya, madaidaiciya.Al-Shura: 52To Wahayi Allah ya qunshi Hujjoji da Dalilai abunda zai Shiryar da lafiayyayun Hankula zuwa haqiqai Waxan da kake son saninsu da Imani da su Allah Maxaukaki ya ce:Yã kũ mutãne! Haƙĩƙa wani dalĩli daga Ubangijinku yã je muku kuma Mun saukar da wani haske, bayyananne zuwa gare ku.Al-Nisa: 174Allah SWT yana son Mutum ya rayu cikin hasken shiriya da kuma Ilimi da haqiqa, su kuwa shaxanu da Xagutai suna son Mutum ya wanzu cikin duhhan Kafirci da Jahilci da kuma Vata Allah Maxaukaki ya ce:Allah shi ne masoyin wadanda suka yi imani, yana fitar da su daga duffai zuwa ga haske, kuma wadanda suka kafirta, masoyansu Dagutu ne, suna fitar da su daga haske zuwa ga duffai…Baqara: 257Kuma kamar wancan Mun aika wani rũhi (rai mai haɗa jama'a) zuwa gare ka, daga gare Mu. Ba ka kasance kã san abin da yake littãfi ba, kõ abin da Yake ĩmãni, kuma amma Mun sanya shi (rũhin, watau Alƙur'ãni) wani haske ne, Munã shiryar da wanda Muke so daga cikin bãyĩnMu game da shi. Kuma Lalle kai, haƙĩƙa, kanã shiryarwa zuwa ga hanya, madaidaiciya.Al-Shura: 52To Wahayi Allah ya qunshi Hujjoji da Dalilai abunda zai Shiryar da lafiayyayun Hankula zuwa haqiqai Waxan da kake son saninsu da Imani da su Allah Maxaukaki ya ce:Yã kũ mutãne! Haƙĩƙa wani dalĩli daga Ubangijinku yã je muku kuma Mun saukar da wani haske, bayyananne zuwa gare ku.Al-Nisa: 174Allah SWT yana son Mutum ya rayu cikin hasken shiriya da kuma Ilimi da haqiqa, su kuwa shaxanu da Xagutai suna son Mutum ya wanzu cikin duhhan Kafirci da Jahilci da kuma Vata Allah Maxaukaki ya ce:Allah shi ne masoyin wadanda suka yi imani, yana fitar da su daga duffai zuwa ga haske, kuma wadanda suka kafirta, masoyansu Dagutu ne, suna fitar da su daga haske zuwa ga duffai…Baqara: 257 39. Musulunci yana girmama Ingantaccen Ilimi, kuma yana kwaxaitarwa kan binciken Ilimi wanda yake babu son rai a cikinsa, kuma yana kira zuwa Nazari da Tunani cikin Kawunanmu da kuma halittu da suke kewaye da mu, da kuma sakamakon Ilimi ingantacce don Ilimi waxanda basa cin karo da Musulunci.Musulunci yana yana girmama Ingantaccen Ilimi Allah Maxaukaki ya ce:"Allah yana xaga Darajar waxanda sukai Imani daga cikin ku kuma waxanda aka bawa Ilimi suna da Darajjojo, kuma Allah ya na baku labarin abunda kuke aikatawa"(Suratu Almujadalah 11)Kuma ya haxa shaidar Malamai da shaidar sa da kuma shaidar Mala'iku kan Mafi girman abun shaidawa Allah Maxaukaki ya ce:Allah Ya shaida cẽwa: Lalle ne bãbu abin bautãwa fãce Shi kuma malãiku da ma'abũta ilmi sun shaida, yana tsaye da ãdalci, bãbu abin bautãwa face Shi, Mabuwãyi, Mai hikima.Aal Imran: 18Kuma wannan yana nuna Matsayin Ma'abota Ilimi a cikin musulunci da kuma abun da Alah ya umarci annabinsa Muhammad SAW da neman qari daga wani abu na Ilaimi Allah Maxaukaki ya ce:"Kuma ka ce Ya Ubangiji ka xarar da ni Limi"Xaha:114Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Duk wanna ya kama wata turba yana neman Ilimi a cikin ta to Allah zai Sawwake masa da ita Haryar zuwa Al-janna" kuma lallai cewa mala'iku suna shinfixa fukafukansu don tarda da mai neman Ilimi kuma lallai Xalibin Ilimi suna nema masa gafara duk waxanda suke cikin sama da Qasa har kifaye a cikin ruwa, kuma lallai cewa falalar Malami kan Mai Ibada Kamar falalar Wata a kan sauran taurari lallai Malamai cewa su ne Magada Annabwa kuma lallai cewa Annabawa basu gadar da Dinare ba ko dirhami kawai sun gadar da Ilimi ne to duk wanda yai riqo da shi to yayi riqo da rabo mai yawa"Abu daud ne ya futar da shi (3641) da Tirmizi (2682) da Ibn Maja (223) kuma lafazin nasa ne da Ahmad (21715)Kuma Musulunci yana kwaxaitarwa kan Ilimi tsantsa wanda babu son rai a cikinsa kuma yana kira zuwa Nazari da Tunani a cikin kawunanmu da kuma cikin halittun da suke gefenmu Allah Maxaukaki ya ce:Zã Mu nũna musu ãyõyinMu a cikin sãsanni da kuma cikin rãyukansu, har ya bayyana a gare su cẽwã lalle (Alƙur'ãni), shi ne gaskiya. Ashe, kuma Ubangijinka bai isa ba, ga cẽwa lalle Shĩ halartacce ne a kan kowane abu ne?Fussilat: 53Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Shin, ba su yi dũbi ba a cikin mulkin sammai da ƙasa, da kuma abin da Allah Ya halitta daga kõme, kuma akwai tsammãni kasancewar ajalinsu, haƙĩƙa, ya kusanta? To, da wane lãbãri a bãyansa suke yin ĩmãni?Al-a'araf: 185Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Shin, kuma ba su yi tafiya ba, a cikin ƙasã dõmin su gani yadda aƙibar waɗanda ke a gabãninsu ta kasance? Sun kasance mafiya ƙarfi daga gare su kuma suka nõmi ƙasa suka rãya ta fiye da yadda suka raya ta, kuma manzanninsu suka je musu da hujjoji bayyanannu. Sabo da haka Allah ba Ya yiwuwa Ya zãlunce su, amma kansu suka kasance sunã zãlunta.Rum: 9Kuma Sakamakon Ilimi Ingantaccen Ilimi baya cin karo da Musulunci kuma zamu faxi wani Misali qwaya xaya wanda Al-qur'ani ya faxi bayanin cikakke dangane da Sha'aninsa tun kafin sama da Shekara Dubu xaya da Xari kuma Ilimin Zamani a qarshe ya sanar da shi; sakamakon daidaituwar abunda yake cikin Al-qur'ani Mai girma kuma shi ne halittar Tayi a cikin Mahaifiyarsa Allah Maxaukaki ya ce:Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun halitta mutum daga wani tsantsa daga lãka.(12)Sa'an nan kuma Muka sanya shi, ɗigon maniyyi a cikin matabbata natsattsiya.(13)Sa'an nan kuma Muka halitta shi gudan jini, sa'an nan Muka halitta gudan jinin tsõka, sa'an nan Muka halitta tsõkar ta zama ƙasũsuwa, sa'an nan Muka tufãtar da ƙasũsuwan da wani nãma sa'an nan kuma Muka ƙãga shi wata halitta dabam. Sabõda haka albarkun Allah sun bayyana, Shi ne Mafi kyaun mãsu halittawa.Al-Mu'aminun: 12-14"Allah yana xaga Darajar waxanda sukai Imani daga cikin ku kuma waxanda aka bawa Ilimi suna da Darajjojo, kuma Allah ya na baku labarin abunda kuke aikatawa"(Suratu Almujadalah 11)Kuma ya haxa shaidar Malamai da shaidar sa da kuma shaidar Mala'iku kan Mafi girman abun shaidawa Allah Maxaukaki ya ce:Allah Ya shaida cẽwa: Lalle ne bãbu abin bautãwa fãce Shi kuma malãiku da ma'abũta ilmi sun shaida, yana tsaye da ãdalci, bãbu abin bautãwa face Shi, Mabuwãyi, Mai hikima.Aal Imran: 18Kuma wannan yana nuna Matsayin Ma'abota Ilimi a cikin musulunci da kuma abun da Alah ya umarci annabinsa Muhammad SAW da neman qari daga wani abu na Ilaimi Allah Maxaukaki ya ce:"Kuma ka ce Ya Ubangiji ka xarar da ni Limi"Xaha:114Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Duk wanna ya kama wata turba yana neman Ilimi a cikin ta to Allah zai Sawwake masa da ita Haryar zuwa Al-janna" kuma lallai cewa mala'iku suna shinfixa fukafukansu don tarda da mai neman Ilimi kuma lallai Xalibin Ilimi suna nema masa gafara duk waxanda suke cikin sama da Qasa har kifaye a cikin ruwa, kuma lallai cewa falalar Malami kan Mai Ibada Kamar falalar Wata a kan sauran taurari lallai Malamai cewa su ne Magada Annabwa kuma lallai cewa Annabawa basu gadar da Dinare ba ko dirhami kawai sun gadar da Ilimi ne to duk wanda yai riqo da shi to yayi riqo da rabo mai yawa"Abu daud ne ya futar da shi (3641) da Tirmizi (2682) da Ibn Maja (223) kuma lafazin nasa ne da Ahmad (21715)Kuma Musulunci yana kwaxaitarwa kan Ilimi tsantsa wanda babu son rai a cikinsa kuma yana kira zuwa Nazari da Tunani a cikin kawunanmu da kuma cikin halittun da suke gefenmu Allah Maxaukaki ya ce:Zã Mu nũna musu ãyõyinMu a cikin sãsanni da kuma cikin rãyukansu, har ya bayyana a gare su cẽwã lalle (Alƙur'ãni), shi ne gaskiya. Ashe, kuma Ubangijinka bai isa ba, ga cẽwa lalle Shĩ halartacce ne a kan kowane abu ne?Fussilat: 53Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Shin, ba su yi dũbi ba a cikin mulkin sammai da ƙasa, da kuma abin da Allah Ya halitta daga kõme, kuma akwai tsammãni kasancewar ajalinsu, haƙĩƙa, ya kusanta? To, da wane lãbãri a bãyansa suke yin ĩmãni?Al-a'araf: 185Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Shin, kuma ba su yi tafiya ba, a cikin ƙasã dõmin su gani yadda aƙibar waɗanda ke a gabãninsu ta kasance? Sun kasance mafiya ƙarfi daga gare su kuma suka nõmi ƙasa suka rãya ta fiye da yadda suka raya ta, kuma manzanninsu suka je musu da hujjoji bayyanannu. Sabo da haka Allah ba Ya yiwuwa Ya zãlunce su, amma kansu suka kasance sunã zãlunta.Rum: 9Kuma Sakamakon Ilimi Ingantaccen Ilimi baya cin karo da Musulunci kuma zamu faxi wani Misali qwaya xaya wanda Al-qur'ani ya faxi bayanin cikakke dangane da Sha'aninsa tun kafin sama da Shekara Dubu xaya da Xari kuma Ilimin Zamani a qarshe ya sanar da shi; sakamakon daidaituwar abunda yake cikin Al-qur'ani Mai girma kuma shi ne halittar Tayi a cikin Mahaifiyarsa Allah Maxaukaki ya ce:Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun halitta mutum daga wani tsantsa daga lãka.(12)Sa'an nan kuma Muka sanya shi, ɗigon maniyyi a cikin matabbata natsattsiya.(13)Sa'an nan kuma Muka halitta shi gudan jini, sa'an nan Muka halitta gudan jinin tsõka, sa'an nan Muka halitta tsõkar ta zama ƙasũsuwa, sa'an nan Muka tufãtar da ƙasũsuwan da wani nãma sa'an nan kuma Muka ƙãga shi wata halitta dabam. Sabõda haka albarkun Allah sun bayyana, Shi ne Mafi kyaun mãsu halittawa.Al-Mu'aminun: 12-14 40. kuma Allah baya Karvar aiki ko ya bada lada akansa a lahira sai daga waxanda sukai Imani da Allah kuma suka gasgata Manzanninsa -Amincin Allah a gare su- kuma Allah baya karvar ibadu sai da abunda ya Shar'anta, saboda mai zai sa Mutum ya kafircewa Allah kuma ya qaunaci ladansa? kuma Allah baya karvar Imani wani Mutum sai idan yayi Imani da Annabawa -Amincin Allah a gare su baki xaya- Kuma yayi Imani da Saqon Annabi Muhammad SAW.Kuma Allah baya karvar aikin kuma baya bada lada akansa a lahira sai daga wanda yayi Imani da Allah kuma ya bishi kuma ya gasgata Manzonsa -Amincin Allah a gare shi- Allah maxaukaki ya ce:Wanda ya kasance yanã nufin mai gaggãwa, sai Mu gaggauta masa a cikinta, abin da Muke so ga wanda Muke nufi, sa'an nan kuma Mu sanya masa Jahannama, ya ƙõnu da ita, yanã abin zargi kuma abin tunkuɗewa.(18)Kuma wanda ya nufi Lãhira, kuma ya yi aiki sabõda ita irin aikinta alhãli kuwa yanã mũmĩni, to, waɗannan aikinsu ya kasance gõdadde.(19)Al-Israa: 18-19Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Dõmin wanda ya aikata daga ayyukan kwarai alhãli kuwa yanã mai ĩmãni, to, bãbu musu ga aikinsa, kuma Mu Mãsu rubũtãwa gare shi ne.Al-anbiya: 94Kuma Allah baya karvar Ibadu sai waxanda ya Shar'anta Allah Maxaukaki ya ce:Saboda haka wanda ya kasance yana fatan haduwa da Ubangijinsa,to, sai ya yi aiki na kwarai. Kuma kada ya hada kowa ga bauta wa Ubangijinsa.Al-Kahf: 110Saboda haka yayi bayani cewa Aiki baya kasancewa Nagartacce sai in ya kasance yana daga cikin abunda Allah ya Shar'anta kuma mai shi ya kasance ya taskake shi saboda Allah a cikin Aikinsa kuma yana mai Imani da Allah yana mai kuma yana mai gasgatawa da Annabawansa da Manzanninsa -Amincin Allah a gare su- amman wanda ya kasance aikinsa wanina hakan ne to haqiqa Allah Maxaukaki ya ce:Kuma Muka gabãta zuwa ga abin da suka aikata daga aiki, sai Muka sanya shi ƙũra wãtsattsiya.Al-furqan: 23Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Wasu huskõki a rãnar nan ƙasƙantattu ne.(2)Mai aiki tana shan Wuya (3)Zata shiga Wiuta Mai Quna (4)Al-gashiya: 2-4To Waxan nan fuskoki masu shan Wahalar aiki sai dai su sun kasance suna aiki ne ba tare shiriya daga Allah ba, Allah sai ya sanya Makomarta zuwa Wuta; saboda batai aiki da da abunda Allah ya Shar'anta ba a'a tayi aiki ne da Ibadu Vatattu kuma ta bi Shugabannin Vata waxan da suka qirqirar musu Addinan Vata saboda aiki nagari karvavve a wajen Allah shi wanda yayi daidai da abunda Manzon Allah SAW ya zo da shi to t ayaya Mutum zai kafirta da Allah kuma ya ya zo kuma ya saka masa??Kuma Allah baya karvar Imanin Wani daga cikin Mutane sai idan yai Imani da Annabawa -Amincin Allah a gare su- baki xayan su, kuma yayi Imani da Saqon Manzon Allah SAW ya gabata cewa an faxi wasu dalilai akan hakan a saki layi na (20) Allah Maxaukaki ya ce:Manzon Allah yã yi ĩmãni da abin da aka saukar zuwa gare shi daga Ubangijinsa, da mũminai. Kõwanensu yã yi ĩmãni da Allah, da mala'ikunSa, da littattafanSa, da manzanninSa. Bã mu rarrabẽwa a tsakãnin daya daga manzanninSa. Kuma (mũminai) suka ce: "Mun ji kuma mun yi dã'a; (Muna nẽman) gãfararKa, yã Ubangijinmu, kuma zuwa a gare Ka makõma take "Al-Baqara: 285Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku yi ĩmãni da Allah da Manzonsa, da Littãfin da Ya sassaukar ga ManzonSa da Littãfin nan wanda Ya saukar daga gabãni. To, wanda ya kãfirta da Allah da malã'ikunSa, da LittattafanSa, da ManzanninSa, da Rãnar Lãhira, to, lalle ne yã ɓace, ɓata mai nĩsa.Al-nisa'a: 136Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma a lõkacin da Allah Ya riƙi alkawarin Annabãwa: "Lalle ne ban bã ku wani abu ba daga Littãfi da hikima, sa'an nan kuma wani manzo ya je muku, mai gaskatãwa ga abin da yake tãre da ku; lalle ne zã ku gaskata Shi, kuma lalle ne zã ku taimake shi." Ya ce: "Shin, kun tabbatar kuma kun riƙi alkawarĩNa a kan wannan a gare ku?" suka ce: "Mun tabbatar." Ya ce: "To, ku yi shaida, kuma Nĩ a tãre da ku Inã daga mãsu shaida."Aal Imran: 81Wanda ya kasance yanã nufin mai gaggãwa, sai Mu gaggauta masa a cikinta, abin da Muke so ga wanda Muke nufi, sa'an nan kuma Mu sanya masa Jahannama, ya ƙõnu da ita, yanã abin zargi kuma abin tunkuɗewa.(18)Kuma wanda ya nufi Lãhira, kuma ya yi aiki sabõda ita irin aikinta alhãli kuwa yanã mũmĩni, to, waɗannan aikinsu ya kasance gõdadde.(19)Al-Israa: 18-19Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Dõmin wanda ya aikata daga ayyukan kwarai alhãli kuwa yanã mai ĩmãni, to, bãbu musu ga aikinsa, kuma Mu Mãsu rubũtãwa gare shi ne.Al-anbiya: 94Kuma Allah baya karvar Ibadu sai waxanda ya Shar'anta Allah Maxaukaki ya ce:Saboda haka wanda ya kasance yana fatan haduwa da Ubangijinsa,to, sai ya yi aiki na kwarai. Kuma kada ya hada kowa ga bauta wa Ubangijinsa.Al-Kahf: 110Saboda haka yayi bayani cewa Aiki baya kasancewa Nagartacce sai in ya kasance yana daga cikin abunda Allah ya Shar'anta kuma mai shi ya kasance ya taskake shi saboda Allah a cikin Aikinsa kuma yana mai Imani da Allah yana mai kuma yana mai gasgatawa da Annabawansa da Manzanninsa -Amincin Allah a gare su- amman wanda ya kasance aikinsa wanina hakan ne to haqiqa Allah Maxaukaki ya ce:Kuma Muka gabãta zuwa ga abin da suka aikata daga aiki, sai Muka sanya shi ƙũra wãtsattsiya.Al-furqan: 23Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Wasu huskõki a rãnar nan ƙasƙantattu ne.(2)Mai aiki tana shan Wuya (3)Zata shiga Wiuta Mai Quna (4)Al-gashiya: 2-4To Waxan nan fuskoki masu shan Wahalar aiki sai dai su sun kasance suna aiki ne ba tare shiriya daga Allah ba, Allah sai ya sanya Makomarta zuwa Wuta; saboda batai aiki da da abunda Allah ya Shar'anta ba a'a tayi aiki ne da Ibadu Vatattu kuma ta bi Shugabannin Vata waxan da suka qirqirar musu Addinan Vata saboda aiki nagari karvavve a wajen Allah shi wanda yayi daidai da abunda Manzon Allah SAW ya zo da shi to t ayaya Mutum zai kafirta da Allah kuma ya ya zo kuma ya saka masa??Kuma Allah baya karvar Imanin Wani daga cikin Mutane sai idan yai Imani da Annabawa -Amincin Allah a gare su- baki xayan su, kuma yayi Imani da Saqon Manzon Allah SAW ya gabata cewa an faxi wasu dalilai akan hakan a saki layi na (20) Allah Maxaukaki ya ce:Manzon Allah yã yi ĩmãni da abin da aka saukar zuwa gare shi daga Ubangijinsa, da mũminai. Kõwanensu yã yi ĩmãni da Allah, da mala'ikunSa, da littattafanSa, da manzanninSa. Bã mu rarrabẽwa a tsakãnin daya daga manzanninSa. Kuma (mũminai) suka ce: "Mun ji kuma mun yi dã'a; (Muna nẽman) gãfararKa, yã Ubangijinmu, kuma zuwa a gare Ka makõma take "Al-Baqara: 285Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku yi ĩmãni da Allah da Manzonsa, da Littãfin da Ya sassaukar ga ManzonSa da Littãfin nan wanda Ya saukar daga gabãni. To, wanda ya kãfirta da Allah da malã'ikunSa, da LittattafanSa, da ManzanninSa, da Rãnar Lãhira, to, lalle ne yã ɓace, ɓata mai nĩsa.Al-nisa'a: 136Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma a lõkacin da Allah Ya riƙi alkawarin Annabãwa: "Lalle ne ban bã ku wani abu ba daga Littãfi da hikima, sa'an nan kuma wani manzo ya je muku, mai gaskatãwa ga abin da yake tãre da ku; lalle ne zã ku gaskata Shi, kuma lalle ne zã ku taimake shi." Ya ce: "Shin, kun tabbatar kuma kun riƙi alkawarĩNa a kan wannan a gare ku?" suka ce: "Mun tabbatar." Ya ce: "To, ku yi shaida, kuma Nĩ a tãre da ku Inã daga mãsu shaida."Aal Imran: 81 41.Lallai Manufar Sakonnin Allah baki xayansu shi ne: cewa lallai Addinin Gaskiya ya xaukaka Xan Adam, saboda ya kasance tsantsan Bawan Allah Ubangijin Talikai, kuma ya 'Yanta shi daga bautar Mutane ko kuma wani abun Duniya ko kuma Tatsunuyoyi, saboda Musulunci -Kamar yadda kake ganinsa- baya tsarkake Mutane ya xagasu sama da matsayinsu, kuma baya sanya su Alloli ababan bautaLallai Manufar baki xayan Sakonnin Allah shi ne: cewa addinin gaskiya ya zamo ya xaukaka Xan Adam sama da komai sai bawa ya lkasance Bawa mai tsantsanr tsarkake Ibada ga Allah Ubangijin Talikai Kuma Musulunci ya 'Yanta Mutum daga bautar kuxi ko tatsuniyoyi Manzon Allah SAW ya ce""Bawan kwabo da Xari ya wahala da bawan Riga da Sutura idan aka bashi sai ya yarda idan kuma ba'a bashi ba sai yaqi yardaSahih Al-Bukhari: 6435Saboda Mutumin da yake daidai ba zai zamanto ya risina ba sai ga Allah babu wata Dukiya da zata bautar da shi ko wani girma ko matsayi ko Qabila kuma a cikin wannan Qissar akwai abunda zai buxewa mai karatu abunda mutane suke kanasa kafin Zuwan Manzanni kuma yaya suka zama a bayansa"Yayin da Musulman farko suka yi Hijira zuwa Habasha, sai Sarkin Habasha na wannan lokacin -Al-najashi- ya ce da su:"Wane Addini ne wanda ya raba ku da Mutanenku a cikinsa, kuma baku shiga Addini na ba ko Addinin wani daga cikin Waxan nan Al-ummai?Sai ja'afar Bn Abi xalib ya ce:Ya kai Wannan Sarki Kuma a lõkacin da Allah Ya riƙi alkawarin Annabãwa: "Lalle ne ban bã ku wani abu ba daga Littãfi da hikima, sa'an nan kuma wani manzo ya je muku, mai gaskatãwa ga abin da yake tãre da ku; lalle ne zã ku gaskata Shi, kuma lalle ne zã ku taimake shi." Ya ce: "Shin, kun tabbatar kuma kun riƙi alkawarĩNa a kan wannan a gare ku?" suka ce: "Mun tabbatar." Ya ce: "To, ku yi shaida, kuma Nĩ a tãre da ku Inã daga mãsu shaida."Ahmad ne ya rawaito shi (1740) da savani kaxan, da kuma Abu na'im a cikin ((Hilyat Al-auliyaa)) (1/115) a takaice.Saboda Musulunci kamar yadda kake gani baya tsarkake wasu Mutane kuma ya xaga Darajarsu sama da Matsayin su kuma ya sanya su zu zaman to Alloli ko abun bauta.Allah Maxaukakin Sarki ya ceKa ce: "Yã ku Mutãnen Littãfi! Ku tafo zuwa ga kalma mai daidaitãwa a tsakã ninmu da ku; kada mu bauta wa kõwa fã ce Allah. Kuma kada mu haɗa kõme da Shi, kuma kada sãshenmu ya riƙi sãshe Ubangiji, baicin Allah." To, idan sun jũya bã ya sai ku ce: "ku yi shaida cẽwa, lalle ne mu masu sallamã wa ne."Aal Imran: 64Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma ba ya umurnin ku da ku riƙi malã'iku da annabãwa lyãyengiji. Shin, zai umurce ku da kãfirci ne a bãyan kun riga kun zama mãsu sallamãwa (Musulmi)?Aal Imran: 80Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Kada ku wuce gona da iri wajen yabona yadda Nasara suka maida Dan Maryam, ni kawai bawa ne, to kuce Bawan Allah ne kuma Manzonsa"Sahih Al-Bukhari: 3445"Bawan kwabo da Xari ya wahala da bawan Riga da Sutura idan aka bashi sai ya yarda idan kuma ba'a bashi ba sai yaqi yardaSahih Al-Bukhari: 6435Saboda Mutumin da yake daidai ba zai zamanto ya risina ba sai ga Allah babu wata Dukiya da zata bautar da shi ko wani girma ko matsayi ko Qabila kuma a cikin wannan Qissar akwai abunda zai buxewa mai karatu abunda mutane suke kanasa kafin Zuwan Manzanni kuma yaya suka zama a bayansa"Yayin da Musulman farko suka yi Hijira zuwa Habasha, sai Sarkin Habasha na wannan lokacin -Al-najashi- ya ce da su:"Wane Addini ne wanda ya raba ku da Mutanenku a cikinsa, kuma baku shiga Addini na ba ko Addinin wani daga cikin Waxan nan Al-ummai?Sai ja'afar Bn Abi xalib ya ce:Ya kai Wannan Sarki Kuma a lõkacin da Allah Ya riƙi alkawarin Annabãwa: "Lalle ne ban bã ku wani abu ba daga Littãfi da hikima, sa'an nan kuma wani manzo ya je muku, mai gaskatãwa ga abin da yake tãre da ku; lalle ne zã ku gaskata Shi, kuma lalle ne zã ku taimake shi." Ya ce: "Shin, kun tabbatar kuma kun riƙi alkawarĩNa a kan wannan a gare ku?" suka ce: "Mun tabbatar." Ya ce: "To, ku yi shaida, kuma Nĩ a tãre da ku Inã daga mãsu shaida."Ahmad ne ya rawaito shi (1740) da savani kaxan, da kuma Abu na'im a cikin ((Hilyat Al-auliyaa)) (1/115) a takaice.Saboda Musulunci kamar yadda kake gani baya tsarkake wasu Mutane kuma ya xaga Darajarsu sama da Matsayin su kuma ya sanya su zu zaman to Alloli ko abun bauta.Allah Maxaukakin Sarki ya ceKa ce: "Yã ku Mutãnen Littãfi! Ku tafo zuwa ga kalma mai daidaitãwa a tsakã ninmu da ku; kada mu bauta wa kõwa fã ce Allah. Kuma kada mu haɗa kõme da Shi, kuma kada sãshenmu ya riƙi sãshe Ubangiji, baicin Allah." To, idan sun jũya bã ya sai ku ce: "ku yi shaida cẽwa, lalle ne mu masu sallamã wa ne."Aal Imran: 64Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Kuma ba ya umurnin ku da ku riƙi malã'iku da annabãwa lyãyengiji. Shin, zai umurce ku da kãfirci ne a bãyan kun riga kun zama mãsu sallamãwa (Musulmi)?Aal Imran: 80Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Kada ku wuce gona da iri wajen yabona yadda Nasara suka maida Dan Maryam, ni kawai bawa ne, to kuce Bawan Allah ne kuma Manzonsa"Sahih Al-Bukhari: 3445 42.Allah ya Shar'anta tuba a Musulunci wanda shi ne Maida komai da komai xin Xan Adam zuwa ga Ubangijinsa, da barin Zunubai, kuma Musulunci yana rushe abunda yake kafinsa na zunubai, kuma tuba yana wanke abunda ya gabace shi na zunubai, saboda haka babu wata buqata mutum ace sai ya bayyana laifukansa a Mutane.Alllah ya Shar'anta Tuba a cikin Musulunci kuma shi ne Mutum ya Maida komai nasa zuwa ga Ubangijinsa kuma ya bar Zunubai Allah Maxaukaki ya ce:"Kuma ku tuba zuwa ga Allah ya ku Muminai baki xayanku ko kwa rabauta"(Surat Annur 31)Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Shin, ba su sani ba cẽwa lallai Allah, ne Yake karɓar tũbã daga bãyinSa, kuma Yanã karɓar sadakõkinsu, kuma lalle Allah ne Mai karɓar tũba, Mai jin ƙai?Al-Tauba: 104Allah Madaukakin Sarki ya ce:Kuma Shi ne ke karɓar tũba daga bãyinSa, kuma Yanã Yafe ƙananan laifuffuka, alhãli kuwa Yanã sanin abin da kuke aikatãwa.Al-Shura: 25Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Lallai Allah ya fi tsananinin Farin ciki da tuban Bawansa Mumini daga Mutumin da yake cikin wata Qasa ya samu kansa cikin wata qasa sai guguwa ta taso tare da shi abun hawansa akanta Abincinsa da abun shansa sai ya yi bacci sannan ya farka kuma haqiqa ta tafi ya neme ta har sai da qishirwa ta kama shi sannan ya ce: bari in koma wajena wanda nake a cikinsa sai inyi bacci har mutuwa ta same ni sai ya sanya kansa kan dantsensa don ya mutu sai kawai ya farka sai ga Dabbarsa a gabansa kuma akanta guzurinsa da Abincinsa da abun shansa to Allah ya fi shi farin ciki da tuban bawansa Mumini daga mai wannan Dabba da guzirin nasa"Sahih Muslim: 2744Kuma Musulunci yana rushe dukan abunda ya gabace shi na kuma tuba yana wanke abunda ya gabace shi na zunubai Allah Maxaukaki ya ce:Ka ce wa waɗanda suka kãfirta, idan sun hanu, zã a gãfarta musu abin da ya riga ya shige, kuma idan sun kõma, to, hanyar kãfiran farko, haƙĩƙa, ta shũɗe.Al-anfal: 38Kuma Allah ya kirawo Nasara da su tuba sai Allah wanda Sha'aninsa ya xaukaka ya ce:shin fã, bã su tuba zuwa ga Allah, kuma su neme Shi gãfara, alhãli kuwa Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai?Al-Ma'ida: 74Kuma ya kwaxaitar da baki xayan masu savo da masu zunubai da su tuba sai Allah Maxaukaki ya ce:Ka ce: (Allah Ya ce): "Yã bãyĩNa waɗanda suka yi barna a kan rãyukansu! Kada ku yanke ƙauna daga rahamar Allah. Lalle Allah na gãfarta zunubai gabã ɗaya. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai gãfara, Mai jin ƙai."Al-Zumar: 53Kuma yayin da Amr Bn Al-as ya Musulunta sai yaji tsoron ko ba za'a gafarta masa Zunubansa ba waxanda ya aikata kafin Musulunci sai Amr yana mai rawaito wannan lokacin ya ce:"Yayin da Allah ya jefa Musulunci a cikin Zuciyata ya ce nazo wajen Manzon Allah SAW don inyi masa Mubaya'a sai ya shinfixa Hanannayensa gare ni sai na ce: ba zan yi maka Mubaya'a ba ya manzon Allah har sai ka gafarta mun abunda ya gabata daga Zunubai na ya ce: sai Manzon Allah SAW ya ce ya kai Amru baka san cewa Hijira tna shafe abunda ya gabaceta ba na Zunubai ya kai Amru baka sani ba cewa Musulunci ya shafe abunda ya gabace na zunubai"Muslim ne ya rawaito shi (121) mai tasawo kamarsa, da kuma Ahmad (17827) kuma wannan lafazin ma nasa ne."Kuma ku tuba zuwa ga Allah ya ku Muminai baki xayanku ko kwa rabauta"(Surat Annur 31)Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Shin, ba su sani ba cẽwa lallai Allah, ne Yake karɓar tũbã daga bãyinSa, kuma Yanã karɓar sadakõkinsu, kuma lalle Allah ne Mai karɓar tũba, Mai jin ƙai?Al-Tauba: 104Allah Madaukakin Sarki ya ce:Kuma Shi ne ke karɓar tũba daga bãyinSa, kuma Yanã Yafe ƙananan laifuffuka, alhãli kuwa Yanã sanin abin da kuke aikatãwa.Al-Shura: 25Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:"Lallai Allah ya fi tsananinin Farin ciki da tuban Bawansa Mumini daga Mutumin da yake cikin wata Qasa ya samu kansa cikin wata qasa sai guguwa ta taso tare da shi abun hawansa akanta Abincinsa da abun shansa sai ya yi bacci sannan ya farka kuma haqiqa ta tafi ya neme ta har sai da qishirwa ta kama shi sannan ya ce: bari in koma wajena wanda nake a cikinsa sai inyi bacci har mutuwa ta same ni sai ya sanya kansa kan dantsensa don ya mutu sai kawai ya farka sai ga Dabbarsa a gabansa kuma akanta guzurinsa da Abincinsa da abun shansa to Allah ya fi shi farin ciki da tuban bawansa Mumini daga mai wannan Dabba da guzirin nasa"Sahih Muslim: 2744Kuma Musulunci yana rushe dukan abunda ya gabace shi na kuma tuba yana wanke abunda ya gabace shi na zunubai Allah Maxaukaki ya ce:Ka ce wa waɗanda suka kãfirta, idan sun hanu, zã a gãfarta musu abin da ya riga ya shige, kuma idan sun kõma, to, hanyar kãfiran farko, haƙĩƙa, ta shũɗe.Al-anfal: 38Kuma Allah ya kirawo Nasara da su tuba sai Allah wanda Sha'aninsa ya xaukaka ya ce:shin fã, bã su tuba zuwa ga Allah, kuma su neme Shi gãfara, alhãli kuwa Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai?Al-Ma'ida: 74Kuma ya kwaxaitar da baki xayan masu savo da masu zunubai da su tuba sai Allah Maxaukaki ya ce:Ka ce: (Allah Ya ce): "Yã bãyĩNa waɗanda suka yi barna a kan rãyukansu! Kada ku yanke ƙauna daga rahamar Allah. Lalle Allah na gãfarta zunubai gabã ɗaya. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai gãfara, Mai jin ƙai."Al-Zumar: 53Kuma yayin da Amr Bn Al-as ya Musulunta sai yaji tsoron ko ba za'a gafarta masa Zunubansa ba waxanda ya aikata kafin Musulunci sai Amr yana mai rawaito wannan lokacin ya ce:"Yayin da Allah ya jefa Musulunci a cikin Zuciyata ya ce nazo wajen Manzon Allah SAW don inyi masa Mubaya'a sai ya shinfixa Hanannayensa gare ni sai na ce: ba zan yi maka Mubaya'a ba ya manzon Allah har sai ka gafarta mun abunda ya gabata daga Zunubai na ya ce: sai Manzon Allah SAW ya ce ya kai Amru baka san cewa Hijira tna shafe abunda ya gabaceta ba na Zunubai ya kai Amru baka sani ba cewa Musulunci ya shafe abunda ya gabace na zunubai"Muslim ne ya rawaito shi (121) mai tasawo kamarsa, da kuma Ahmad (17827) kuma wannan lafazin ma nasa ne. 43.Saboda a cikin Musulunci dangantaka tsakanin Mutum da Allah kai tsaye ta ke, saboda haka baka buqatar wani Mutum da zai kasance tsani tsakaninka da Allah, saboda Musulunci ya hana Mu sanya Mutane su zamanto Alloli ko kuma suna tarayya da Allah cikin Allantakarsa da BautarsaA cikin Musulunci babu wata Buqatar yin furuci da laifukan Mutum a gaban wani Mutum saboda a cikin Musulunci Alaqa a tsakanin Mutum da Allah kai tsaye saboda ba'a buqatar zuwa wani xaya, saboda ya kasance a tsakaninka da tsakanin Allah kamar yadda ya wuce a sakin layi mai lamba (36) cewa Allah Maxaukaki ya kira baki xayan Mutane zuwa tuba da kuma komawa zuwa gare shi to shi kamar haka ya hana Mutane kan su riqi Annabawa ko Mala'iku tsani tsakaninsa da tsakanin bayinsaKuma ba ya umurnin ku da ku riƙi malã'iku da annabãwa lyãyengiji. Shin, zai umurce ku da kãfirci ne a bãyan kun riga kun zama mãsu sallamãwa (Musulmi)?Aal Imran: 80Saboda Musulunci -kamar yadda kake gani- ya na hana mu sanya Mutum a matsayin Ubangiji ko yai tarayya da Allah a cikin Allantakar ko kuma bauta kuma Allah ya ce game da nasara:Sun riƙi mãlamansu (Yahũdu) da ruhubãnãwansu (Nasãra) Ubannangiji, baicin Allah, kuma sun riƙi Masĩhu ɗan Maryama (haka). Kuma ba a umurce su ba fãce da su bautã wa Ubangiji Guda. Bãbu abin bautãwa fãce Shi. TsarkinSa ya tabbata daga barin abin da suke yin shirki da shi.Al-taubah: 31Kuma Allah ya Musantawa kafiran da suka riqi wasu tsanuka tsakaninsu da shi Allah Maxaukaki ya ce:To, addini tsarkakakke na Allah ne, kuma waɗanda suka riƙi waɗansu majibinta, bã Shi ba, (sunã cẽwa) "Ba mu bauta musu ba fãce dõmin su kusantar da mu zuwa ga Allah, kusantar daraja." Lalle Allah nã yin hukunci a tsakãninsu ga abin da suka zama sunã sãɓãwa a cikinsa. Lalle Allah ba Ya shiryar da wanda yake mai ƙarya, mai kãfirci.Al-Zumar: 3Kuma Allah yayi bayanin cewa Masu bautar Gumaka -Mutanen Jahiliyya- sun kasance suna riqar wasu tsanuka tsakaninsu daAllah cewa su ne masu kusanta su zuwa ga Allah.Kuma idan Allah ya hana Mutane su qiqi Annabawa ko Mal'iku wasu tsani tsakaninsa da Bayainsa; to wasun su sun fi dacewa da a bari kuma ta yaya Annabawa da manzanni -Amincin Allah a gare su- suna gaggawa a cikin kusanci zuwa ga Allah Allah Maxaukaki ya ce yana mai bada labarin halin annabawa da Manzanni -Amincin Allah a gare su-Lalle ne su, sun kasance suna gudun tsere zuwa ga ayyukan alheri. Kuma suna kiranmu a kan kwadayi da fargaba. Kuma sun kasance masu saunar (aikata sabo) gare Mu.Al-anbiya'a: 90Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Waɗancan, waɗanda suke kiran, sunã nẽman tsãni zuwa ga Ubangijinsu. Waɗanne ne suke mafĩfĩta a kusanta? Kuma sunã fãtan sãmun rahamarSa, kuma sunã tsõron azãbarSa. Lalle ne azãbar Ubangijinka ta kasance abar tsõro ce.Al-isra'a: 57Ai lallai cewa waxanda suke bautar wanin Allah -na daga annabawa da salihai= su suna neman kusantar Allah kuma suna neman rahamarsa kuma suna tsoron Azabarsa; to ta yaya yaya za'a roqi wanin Allah?Kuma ba ya umurnin ku da ku riƙi malã'iku da annabãwa lyãyengiji. Shin, zai umurce ku da kãfirci ne a bãyan kun riga kun zama mãsu sallamãwa (Musulmi)?Aal Imran: 80Saboda Musulunci -kamar yadda kake gani- ya na hana mu sanya Mutum a matsayin Ubangiji ko yai tarayya da Allah a cikin Allantakar ko kuma bauta kuma Allah ya ce game da nasara:Sun riƙi mãlamansu (Yahũdu) da ruhubãnãwansu (Nasãra) Ubannangiji, baicin Allah, kuma sun riƙi Masĩhu ɗan Maryama (haka). Kuma ba a umurce su ba fãce da su bautã wa Ubangiji Guda. Bãbu abin bautãwa fãce Shi. TsarkinSa ya tabbata daga barin abin da suke yin shirki da shi.Al-taubah: 31Kuma Allah ya Musantawa kafiran da suka riqi wasu tsanuka tsakaninsu da shi Allah Maxaukaki ya ce:To, addini tsarkakakke na Allah ne, kuma waɗanda suka riƙi waɗansu majibinta, bã Shi ba, (sunã cẽwa) "Ba mu bauta musu ba fãce dõmin su kusantar da mu zuwa ga Allah, kusantar daraja." Lalle Allah nã yin hukunci a tsakãninsu ga abin da suka zama sunã sãɓãwa a cikinsa. Lalle Allah ba Ya shiryar da wanda yake mai ƙarya, mai kãfirci.Al-Zumar: 3Kuma Allah yayi bayanin cewa Masu bautar Gumaka -Mutanen Jahiliyya- sun kasance suna riqar wasu tsanuka tsakaninsu daAllah cewa su ne masu kusanta su zuwa ga Allah.Kuma idan Allah ya hana Mutane su qiqi Annabawa ko Mal'iku wasu tsani tsakaninsa da Bayainsa; to wasun su sun fi dacewa da a bari kuma ta yaya Annabawa da manzanni -Amincin Allah a gare su- suna gaggawa a cikin kusanci zuwa ga Allah Allah Maxaukaki ya ce yana mai bada labarin halin annabawa da Manzanni -Amincin Allah a gare su-Lalle ne su, sun kasance suna gudun tsere zuwa ga ayyukan alheri. Kuma suna kiranmu a kan kwadayi da fargaba. Kuma sun kasance masu saunar (aikata sabo) gare Mu.Al-anbiya'a: 90Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Waɗancan, waɗanda suke kiran, sunã nẽman tsãni zuwa ga Ubangijinsu. Waɗanne ne suke mafĩfĩta a kusanta? Kuma sunã fãtan sãmun rahamarSa, kuma sunã tsõron azãbarSa. Lalle ne azãbar Ubangijinka ta kasance abar tsõro ce.Al-isra'a: 57Ai lallai cewa waxanda suke bautar wanin Allah -na daga annabawa da salihai= su suna neman kusantar Allah kuma suna neman rahamarsa kuma suna tsoron Azabarsa; to ta yaya yaya za'a roqi wanin Allah? 44.a qarshen wannan littafin muna tunsarwa cewa Mutane duk da savanin Zamaninsu da Qabilunsu, da garuruwan su kai baki xayan Duniyar Mutane sun sava a wajen Tunanisu da Manufofin su, sun yi hannun riga wajen garuruwansu da Ayyukan su, saboda haka suna da buqatar wani Mai shiryarwa da zai xorasu kan Turba, da wani tasri da haxe kansu, da wani Jagora da zai kare su, kuma Manzanni -Amincin Allah a gare su- sun jivanci hakan da Wahayi daga Allah Maxaukaki suna shiryar da Mutane zuwa Hanyar Al-kairi da Shiriya, kuma ya haxa su akan Shari'ar Allah kuma suna Hukunci da Gaskiya a tsakaninsu, saboda Al-amuransu su tafi daidai dai dai da yadda waxan nan suka amsawa Manzannin, da kuma kusancinsu da waxan nan lokutan na Saqonnin Allah, kuma Allah ya cika Saqonin Manzancin da Manzo Annabi Muhammad SAW kuma ya Hukunta mata Wanzuwa, kuma ya sanyata Shiriya ga Mutane da kuma Rahama da Haske da Shiriyarwa zuwa Tafarki Mai isarwa zuwa ga Allah SWTA qarshen wannan Littafin muke tunasar da Mutane duk da savanin zamanunsu da Yarukansu, da garuruwansu, kai baki xayan ma Mutanen Duniya sun sava a Tunaninsu da manufofin su a cikin Garuruwansu da Ayyukansu saboda yana bukata zuwa wanda zai shige masa gaba da zai sa shi a Hanya da kuma tsari da zai haxe su da kuma Jagora da zai kare su, kuma Mazanni Masu girma -Amincin Allah a gare su- sun xau wannan nauyin da wahayi daga Allah suna shiryar da Mutane suwa kan tafarkin Al-kairi da kuma shiriya kuma su tara su akan Shari'ar Allah kuma suyi musu Hukunci a tsakaninsu da ita saboda abubuwan su su daidaita, gwargwadon yadda suka amsawa waxan nan Manzanni da kuma kusancin lokacin su da saqonnin Allah kuma yayin da vata ya yawaita, kuma Jahilci ya game ko ina, kuma akai bautar Gunki, saboda haka sai Allah ya aiko Annabi Muhammad SAW da Shiriya da kuma Addini na gaskiya don ya futar da Mutane daga Duhun Kafirci da Jahilci da Bautar Gumaka zuwa Imani da Shiriya. 45.Saboda haka nake roqonka ya kai Xan Adam ka tsaya ga Allah tsayuwa ta gasliya kana mai tsiraita kanka daga Kwaikwayo da Al-ada, kuma kasani cewa kai bayan Mutuwarka zaka koma ne zuwa ga Ubangijinka, kuma ka kalli kanka, da kuma wasu sassa da suke kewaye da kai, ka Musulunta zaka rabauta a Duniyarka da Lahirar ka, idan kuma kana son shiga Musulunci babu abunda zaka yi sai kawai ka shaida cewa Babu abun bauta da gaskiya sai Allah, kuma cewa Annabi Muhammad Manzon Allah ne, kuma kayi watsi da duk abunda ake bautawa koma bayan Allah, kuma kayi Imani cewa Allah zai tashi waxanda suke cikin Qabari kuma cewa Hisabi da sakamako gaskiya ne, to idan ka shaida da Wannan Shaidawar to haqiqa ka zama Musulmi, saboda haka bayan haka zaka bautawa Allah da abunda ya Shar'anta na Sallah da Zakka da Azumi, da kuma Hajjatar Xakin Allah idan ka samu Iko yin hakan,To ina kira gareka ya kai Mutum lallai ka tsaya ga Allah kana mai gaskiya kuma ka rabu duk wani Taqalini da Al-ada kamar yadda Allah Maxaukaki ya faxa:Ka ce: "Ina yi muku wa'azi ne kawai da kalma guda! watau ku tsayu dõmin Allah, bibbiyu da ɗaiɗai, sa'an nan ku yi tunãni, bãbu wata hauka ga ma'abũcinku. Shĩ bai zama ba fãce mai gargaɗi ne a gare ku a gaba ga wata azãba mai tsanani.Saba'i: 46Kuma kana sani cewa kai bayan Mutuwarka zaka koma ga Ubangijinka Allah Maxaukaki ya ce:Kuma mutum bã shi da kõme fãce abin da ya aikata.(39)Kuma llai zaiga Ayyukansa(40)Sannan sai a saka masa da cikakken Sakamako (41)Kuma lallai zuwa ga Ubangijinka Matuqa ta ke (42)Al-Najm: 39-42Kuma lallai cewa ka kalli kanka da kuma sassa da suke kewaye da kai Allah Maxaukaki ya ce:Shin, ba su yi dũbi ba a cikin mulkin sammai da ƙasa, da kuma abin da Allah Ya halitta daga kõme, kuma akwai tsammãni kasancewar ajalinsu, haƙĩƙa, ya kusanta? To, da wane lãbãri a bãyansa suke yin ĩmãni?Al-a'araf: 185to ka Musulunta sai ka rabauta a Duniyarka da Lahirarka kuma idan kana son shiga Musulunci babau wani da zakayi sai ka shaida cewa babu wani Ubangiji da ya cancanci a bauta masa sai Allah kuma lallai cewa Muhammagu Manzon Allah neKuma yayin da Manzo SAW ya tura Mu'az zuwa Yeman ya na mai kira zuwa Musulunci sai ya ce da shi:"Lallai kai zaka je wajen wasu Mutane daga cikin Ahlul kitab ka kirasu zuwa Shaidawa cewa babu wani Ubangiji da ya cancanci a bautawa sai Allah kuma cewa ni manzon Allah ne, to idan suka bi ka akan hakan to ka sanar da su cewa Allah ya farlanta musu salloli biyar a cikin kowace Rana da Daddre, to idan suka bika cikin hakan to ka sanar da su cewa Allah ya farlanta musu Sadaqa da za'a karvo daga Mawadatansu sannan a Mayar ga Talakawansu to idan suka bika akan haka to na haneka da ka kiyayi Mafi Darajar Dukoiyoyinsu"Sahih Muslim: 19Kuma ka rabu da duk wani abu da ake bautawa koma bayan Allah kuma rabuwa da duk abunda ake bautawa koma bayan Allah shi ne Addinin Annabi Ibrahim -Amincin Allah a hare shi- Allah Maxaukaki ya ce:"Haqiqa ya kasance kuma da abun koyi cikin rayuwar Annabi Ibrahim da waxanda suke tare da shi lokacin da suka ce da Mutanen su mu babu mu babu ku da abunda kuke bautawa koma bayan Allah kuma mun kafirce muku kuma gaba ta qullu tsakaninmu da ku da qiyayya har sai kunyi imani da shi kaxai"Al-mumtahana: 4Kuma kayi Imani cewa za'a tashi waxanda suke cikin Qaburbura Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Wancan ne dõmin lalle Allah Shi ne Gaskiya, kuma lalle ne shi Yake rãyar da matattu, kuma lalle Shi Mai ikon yi ne a kan kõme.(6)Kuma lalle ne Sa'ar Tãshin ¡iyãma mai zuwa ce, bãbu shakka a cikinta kuma lalle ne Allah Yanã tãyar da waɗanda suke a cikin ƙaburbura.(7)Alhajji: 6-7Kuma Hisabi da sakamako gaskiya ne Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Alhãli kuwa Allah ne Ya halitta sammai da ƙasã sabõda gaskiya, Kuma dõmin a sãka wa kõwane rai da abin da ya sanã'anta, kuma su, bã zã a zãlunce su ba.Al-jathiya: 22Ka ce: "Ina yi muku wa'azi ne kawai da kalma guda! watau ku tsayu dõmin Allah, bibbiyu da ɗaiɗai, sa'an nan ku yi tunãni, bãbu wata hauka ga ma'abũcinku. Shĩ bai zama ba fãce mai gargaɗi ne a gare ku a gaba ga wata azãba mai tsanani.Saba'i: 46Kuma kana sani cewa kai bayan Mutuwarka zaka koma ga Ubangijinka Allah Maxaukaki ya ce:Kuma mutum bã shi da kõme fãce abin da ya aikata.(39)Kuma llai zaiga Ayyukansa(40)Sannan sai a saka masa da cikakken Sakamako (41)Kuma lallai zuwa ga Ubangijinka Matuqa ta ke (42)Al-Najm: 39-42Kuma lallai cewa ka kalli kanka da kuma sassa da suke kewaye da kai Allah Maxaukaki ya ce:Shin, ba su yi dũbi ba a cikin mulkin sammai da ƙasa, da kuma abin da Allah Ya halitta daga kõme, kuma akwai tsammãni kasancewar ajalinsu, haƙĩƙa, ya kusanta? To, da wane lãbãri a bãyansa suke yin ĩmãni?Al-a'araf: 185to ka Musulunta sai ka rabauta a Duniyarka da Lahirarka kuma idan kana son shiga Musulunci babau wani da zakayi sai ka shaida cewa babu wani Ubangiji da ya cancanci a bauta masa sai Allah kuma lallai cewa Muhammagu Manzon Allah neKuma yayin da Manzo SAW ya tura Mu'az zuwa Yeman ya na mai kira zuwa Musulunci sai ya ce da shi:"Lallai kai zaka je wajen wasu Mutane daga cikin Ahlul kitab ka kirasu zuwa Shaidawa cewa babu wani Ubangiji da ya cancanci a bautawa sai Allah kuma cewa ni manzon Allah ne, to idan suka bi ka akan hakan to ka sanar da su cewa Allah ya farlanta musu salloli biyar a cikin kowace Rana da Daddre, to idan suka bika cikin hakan to ka sanar da su cewa Allah ya farlanta musu Sadaqa da za'a karvo daga Mawadatansu sannan a Mayar ga Talakawansu to idan suka bika akan haka to na haneka da ka kiyayi Mafi Darajar Dukoiyoyinsu"Sahih Muslim: 19Kuma ka rabu da duk wani abu da ake bautawa koma bayan Allah kuma rabuwa da duk abunda ake bautawa koma bayan Allah shi ne Addinin Annabi Ibrahim -Amincin Allah a hare shi- Allah Maxaukaki ya ce:"Haqiqa ya kasance kuma da abun koyi cikin rayuwar Annabi Ibrahim da waxanda suke tare da shi lokacin da suka ce da Mutanen su mu babu mu babu ku da abunda kuke bautawa koma bayan Allah kuma mun kafirce muku kuma gaba ta qullu tsakaninmu da ku da qiyayya har sai kunyi imani da shi kaxai"Al-mumtahana: 4Kuma kayi Imani cewa za'a tashi waxanda suke cikin Qaburbura Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Wancan ne dõmin lalle Allah Shi ne Gaskiya, kuma lalle ne shi Yake rãyar da matattu, kuma lalle Shi Mai ikon yi ne a kan kõme.(6)Kuma lalle ne Sa'ar Tãshin ¡iyãma mai zuwa ce, bãbu shakka a cikinta kuma lalle ne Allah Yanã tãyar da waɗanda suke a cikin ƙaburbura.(7)Alhajji: 6-7Kuma Hisabi da sakamako gaskiya ne Allah Maxaukakin Sarki ya ce:Alhãli kuwa Allah ne Ya halitta sammai da ƙasã sabõda gaskiya, Kuma dõmin a sãka wa kõwane rai da abin da ya sanã'anta, kuma su, bã zã a zãlunce su ba.Al-jathiya: 22Saboda idan ka shaida da wannan Shaidawar to haqiqa ka zama Musulmi to ya wajaba akan ka bayan haka ka bautawa Allah da abunda ya Shar'anta na Sallah da Zakkah da Azumi da Hajji idan ka samu damar dama yi da wanin hakan,Kwafi a ranar 19-11-1441Wanda ya Rubuta shi Shi Farfesa Muhammad Bn Abdullahi Al-SuhaimBabban Malamin koyar da Aqida a Vangaren koyar da Darussan Musulunci (a da can)Tsangayar Koyo da koyarwa, na jami'ar Sarki Su'udRitadh, Kasar Saudi Arabia