النبأ

تفسير سورة النبأ

الترجمة الهوساوية

هَوُسَ

الترجمة الهوساوية

ترجمة معاني القرآن الكريم للغة الهوسا ترجمها أبو بكر محمود جومي، نشرها مجمع الملك فهد لطباعة المصحف الشريف بالمدينة المنورة، عام الطبعة 1434. ملاحظة: ترجمات بعض الآيات (مشار إليها) تم تصويبها بمعرفة مركز رواد الترجمة، مع إتاحة الاطلاع على الترجمة الأصلية

﴿بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ عَمَّ يَتَسَاءَلُونَ﴾

A kan mẽ suke tambayar jũna?

﴿عَنِ النَّبَإِ الْعَظِيمِ﴾

A kan muhimmin lãbãri mai girma (Alƙur'ãni)?

﴿الَّذِي هُمْ فِيهِ مُخْتَلِفُونَ﴾

Wanda suke sãɓa wa jũna a cikinsa?

﴿كَلَّا سَيَعْلَمُونَ﴾

A'aha! Zã su sani.

﴿ثُمَّ كَلَّا سَيَعْلَمُونَ﴾

Kuma, a'aha! Zã su sani.

﴿أَلَمْ نَجْعَلِ الْأَرْضَ مِهَادًا﴾

Ashe, ba Mu sanya ƙasa shimfiɗa ba?

﴿وَالْجِبَالَ أَوْتَادًا﴾

Da duwãtsu turaku (ga riƙe ƙasa)?

﴿وَخَلَقْنَاكُمْ أَزْوَاجًا﴾

Kuma, Mun halitta ku mazã da mãtã?

﴿وَجَعَلْنَا نَوْمَكُمْ سُبَاتًا﴾

Kuma, Muka sanya barcinku hũtãwa?

﴿وَجَعَلْنَا اللَّيْلَ لِبَاسًا﴾

Kuma, Muka sanya dare (ya zama) sutura?

﴿وَجَعَلْنَا النَّهَارَ مَعَاشًا﴾

Kuma, Muka sanya yini (yazama) lõkacin nẽman abinci?

﴿وَبَنَيْنَا فَوْقَكُمْ سَبْعًا شِدَادًا﴾

Kuma, Muka gina, a samanku, sammai bakwai mãsu ƙarfi?

﴿وَجَعَلْنَا سِرَاجًا وَهَّاجًا﴾

Kuma, Muka sanya fitila mai tsanin haske (rãnã)?

﴿وَأَنْزَلْنَا مِنَ الْمُعْصِرَاتِ مَاءً ثَجَّاجًا﴾

Kuma, Muka saukar daga cikakkun girãgizai, ruwa mai yawan zuba?

﴿لِنُخْرِجَ بِهِ حَبًّا وَنَبَاتًا﴾

Dõmin, Mu fitar da ƙwaya da tsiri game da shi?

﴿وَجَنَّاتٍ أَلْفَافًا﴾

Da itãcen lambuna mãsu lillibniya?

﴿إِنَّ يَوْمَ الْفَصْلِ كَانَ مِيقَاتًا﴾

Lalle ne, rãnar rarrabẽwa tã kasance abin ƙayyadẽ wa lõkaci.

﴿يَوْمَ يُنْفَخُ فِي الصُّورِ فَتَأْتُونَ أَفْوَاجًا﴾

Rãnar da zã a yi bũsa a cikin ƙaho, sai ku zo, jama'a jama'a.

﴿وَفُتِحَتِ السَّمَاءُ فَكَانَتْ أَبْوَابًا﴾

Kuma, aka buɗe sama, sai ta kasance ƙõfõfi.

﴿وَسُيِّرَتِ الْجِبَالُ فَكَانَتْ سَرَابًا﴾

Kuma, aka tafiyar da duwãtsu, sai suka kasance ƙũra.

﴿إِنَّ جَهَنَّمَ كَانَتْ مِرْصَادًا﴾

Lalle ne, Jahannama tã kasance madãkata.

﴿لِلطَّاغِينَ مَآبًا﴾

Ga mãsu ƙẽtare iyãkõki, tã zama makõma.

﴿لَابِثِينَ فِيهَا أَحْقَابًا﴾

Sunã, mãsu zama a cikinta, zãmunna.

﴿لَا يَذُوقُونَ فِيهَا بَرْدًا وَلَا شَرَابًا﴾

Bã su ɗanɗanãwar wani sanyi a cikinta, kuma bã su ɗanɗana abin sha.

﴿إِلَّا حَمِيمًا وَغَسَّاقًا﴾

Fãce tafasasshen ruwa da ruɓaɓɓen jini.

﴿جَزَاءً وِفَاقًا﴾

Sakamako mai dãcẽwa.

﴿إِنَّهُمْ كَانُوا لَا يَرْجُونَ حِسَابًا﴾

Lalle ne, sũ, sun kasance bã su fãtar sauƙin wani hisãbi.

﴿وَكَذَّبُوا بِآيَاتِنَا كِذَّابًا﴾

Kuma, suka ƙaryata game da ãyõyinMu, ƙaryatãwa!

﴿وَكُلَّ شَيْءٍ أَحْصَيْنَاهُ كِتَابًا﴾

Alhãli, kõwane abu Mun ƙididdigẽ shi, a rubũce.

﴿فَذُوقُوا فَلَنْ نَزِيدَكُمْ إِلَّا عَذَابًا﴾

Sabõda haka, ku ɗanɗana domin haka, bã zã Mu ƙara muku kõme ba fãce azãba.

﴿إِنَّ لِلْمُتَّقِينَ مَفَازًا﴾

Lalle ne, mãsu taƙawã nã da wani wurin sãmun babban rabo.

﴿حَدَائِقَ وَأَعْنَابًا﴾

Lambuna da inabõbi.

﴿وَكَوَاعِبَ أَتْرَابًا﴾

Da yan Mata tsaraikun Juna

﴿وَكَأْسًا دِهَاقًا﴾

Da hinjãlan giya cikakku.

﴿لَا يَسْمَعُونَ فِيهَا لَغْوًا وَلَا كِذَّابًا﴾

Bã su jin yãsassar magana, a cikinta, kuma bã su jin ƙaryatãwa.

﴿جَزَاءً مِنْ رَبِّكَ عَطَاءً حِسَابًا﴾

Dõmin sakamako daga Ubangijinka, kyautã mai yawa.

﴿رَبِّ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا الرَّحْمَٰنِ ۖ لَا يَمْلِكُونَ مِنْهُ خِطَابًا﴾

Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, Mai rahama, bã su da ikon yin wata magana daga gare Shi.

﴿يَوْمَ يَقُومُ الرُّوحُ وَالْمَلَائِكَةُ صَفًّا ۖ لَا يَتَكَلَّمُونَ إِلَّا مَنْ أَذِنَ لَهُ الرَّحْمَٰنُ وَقَالَ صَوَابًا﴾

Rãnar da Rũhi da malã'iku zã su tsaya a cikin safu, bã su magana, sai wanda Allah Ya yi masa izni, kuma ya faɗi abin da ke daidai.

﴿ذَٰلِكَ الْيَوْمُ الْحَقُّ ۖ فَمَنْ شَاءَ اتَّخَذَ إِلَىٰ رَبِّهِ مَآبًا﴾

Wancan, shi ne yini na gaskiya; to wanda ya so, ya riƙa makõma zuwa ga Ubangijinsa.

﴿إِنَّا أَنْذَرْنَاكُمْ عَذَابًا قَرِيبًا يَوْمَ يَنْظُرُ الْمَرْءُ مَا قَدَّمَتْ يَدَاهُ وَيَقُولُ الْكَافِرُ يَا لَيْتَنِي كُنْتُ تُرَابًا﴾

Lalle ne, Mũ, Mun yi muku gargaɗin azãba makusanciya, rãnar da mutum ke dũbi zuwa ga abin da hannãyensa suka aikata, kuma kafiri ya ce: "Kaitona, dã dai nã zama turɓãya!"

الترجمات والتفاسير لهذه السورة: