الأعلى

تفسير سورة الأعلى

الترجمة الهوساوية

هَوُسَ

الترجمة الهوساوية

ترجمة معاني القرآن الكريم للغة الهوسا ترجمها أبو بكر محمود جومي، نشرها مجمع الملك فهد لطباعة المصحف الشريف بالمدينة المنورة، عام الطبعة 1434. ملاحظة: ترجمات بعض الآيات (مشار إليها) تم تصويبها بمعرفة مركز رواد الترجمة، مع إتاحة الاطلاع على الترجمة الأصلية

﴿بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ سَبِّحِ اسْمَ رَبِّكَ الْأَعْلَى﴾

Ka tsarkake sũnan Ubangijinka Mafi ɗaukaka.

﴿الَّذِي خَلَقَ فَسَوَّىٰ﴾

Wanda Yã yi halitta sa'an nan Ya daidaita abin halittar.

﴿وَالَّذِي قَدَّرَ فَهَدَىٰ﴾

Kuma Wanda Ya ƙaddara (abin da Ya so) sannan Ya shiryar, (da mutum ga hanyar alhẽri da ta sharri).

﴿وَالَّذِي أَخْرَجَ الْمَرْعَىٰ﴾

Kuma Wanda Ya fitar da makiyãyã.

﴿فَجَعَلَهُ غُثَاءً أَحْوَىٰ﴾

Sa'an nan Ya mayar da ita ƙeƙasassa, baƙa.

﴿سَنُقْرِئُكَ فَلَا تَنْسَىٰ﴾

Za mu karantar da kai (Alƙur'ãni) sabõda haka bã zã ka mantã (shi) ba.

﴿إِلَّا مَا شَاءَ اللَّهُ ۚ إِنَّهُ يَعْلَمُ الْجَهْرَ وَمَا يَخْفَىٰ﴾

Fãce abin da Allah Ya so, lalle ne Shi (Allah) Ya san bayyane da abin da yake bõye.

﴿وَنُيَسِّرُكَ لِلْيُسْرَىٰ﴾

Kuma za Mu sauƙaƙe maka (al'amari) zuwa ga (Shari'a) mai sauƙi.

﴿فَذَكِّرْ إِنْ نَفَعَتِ الذِّكْرَىٰ﴾

Sabõda baka, ka tunãtar, idan tunatarwa zã ta yi amfãni.

﴿سَيَذَّكَّرُ مَنْ يَخْشَىٰ﴾

Wanda yake tsõron (Allah) Zai tuna.

﴿وَيَتَجَنَّبُهَا الْأَشْقَى﴾

Kuma shaƙiyyi, zai nisanceta,

﴿الَّذِي يَصْلَى النَّارَ الْكُبْرَىٰ﴾

Wanda zai shiga wutar da tã fi girma.

﴿ثُمَّ لَا يَمُوتُ فِيهَا وَلَا يَحْيَىٰ﴾

Sa'an nan bã zai mutu ba a cikinta, kuma bã zai rãyu ba.

﴿قَدْ أَفْلَحَ مَنْ تَزَكَّىٰ﴾

Lalle ne wanda ya tsarkaka (da ĩmãni) yã sãmu babban rabo.

﴿وَذَكَرَ اسْمَ رَبِّهِ فَصَلَّىٰ﴾

Kuma ya ambaci sũnan* Ubangijinsa, sa'an nan yã yi salla.

﴿بَلْ تُؤْثِرُونَ الْحَيَاةَ الدُّنْيَا﴾

Ba haka ba! Kunã zãɓin rãyuwa ta kusa dũniya.*

﴿وَالْآخِرَةُ خَيْرٌ وَأَبْقَىٰ﴾

Alhãli Lãhira ita ce mafi alheri kuma mafi wanzuwa.

﴿إِنَّ هَٰذَا لَفِي الصُّحُفِ الْأُولَىٰ﴾

Lalle ne, wannan* yanã a cikin littafan farko.

﴿صُحُفِ إِبْرَاهِيمَ وَمُوسَىٰ﴾

Littaffan Ibrãhĩm da Mũsã.

الترجمات والتفاسير لهذه السورة: